< Mathiu 26 >
1 Jisu ih erah loong ah jen thoon nyootsoot rum ano, heliphante loong asuh baatta,
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin dukan waɗannan abubuwa, sai ya ce wa almajiransa,
2 “Sen ih jat ehan, sa nyi mongdoh, Khopi Kuwaang angte, eno Mina Sah ah bangphak nah rapbot suh mih suh jokoh rum ah.”
“Kamar yadda kuka sani, Bikin Ƙetarewa sauran kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum don a gicciye shi.”
3 Eno romwah phokhoh nyia hadaang phokhoh loong ah Romwah Phokhothoon Kaiaphas noklong ni lomtong rumta,
Sai manyan firistoci da dattawan mutane, suka taru a fadan babban firist, mai suna Kayifas,
4 eno Jisu ah jokhak ano tek haat suh ngoongthum huthum rumta.
suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci, su kuma kashe shi.
5 Neng ih liita, “Seng ih erah kuwaang tokdoh lajaajaat reejih, adoleh miloong ah phophaang daanmui rum ah.”
Suka ce, “Amma ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su tā da rikici.”
6 Bithaani ni Jisu ah engam wah Simoon nok ni angta.
Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,
7 Jisu phaksat phaksah tokdi, minuh nusiit ih kom thuung adi phontum ah pi ano wang taha eno Jisu lah adi lokta.
wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
8 Heliphante loong ah ih erah sok rum ano ekhat ih rumta. “Arah loong ah tumet suh thaaja wan halu? Neng ih cheng rumta.
Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
9 “Arah phontum ah ngun hantek doh sang ano changthih loong suh kotjih boh angta!”
Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
10 Neng ih tumjih li rumta erah Jisu ih ejat etta, eno baat rumta, “Arah nuh ah sen ih tumet suh paklak han? Nga raangtaan ih heh jaase jih nyia epunjih boh reela.
Sane da wannan, Yesu ya ce musu, “Me ya sa kuke damun macen nan? Ta yi mini abu mai kyau ne.
11 Changthih loong abah saarookwih sen damdam eje ang ha, enoothong ngah ah sen damdoh saarookwih lajeete.
Matalauta za su kasance tare da ku kullum, amma ni ba zan kasance tare da ku kullum ba.
12 Arah nuh reela ah langla, nga sak nah phontum ah lok ano nga mangbeng thengnah thiinkaat suh ban khookhamha.
Sa’ad da ta zuba turaren nan a jikina, ta shirya ni ne don jana’izata.
13 Amadi, ngah ih amiimi tiit baat rumhala arah mongrep adoh ruurang ese marah nah thok ah, erah doh arah minuh reela ah labeehaat thang ih samthun jih ang ah.”
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bisharan nan a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
14 Eno heliphante loongdung dowa wasiit—hemen ah Judas Eskeriot—romwah phokhothoon nok ni kah ano
Sai ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, wanda ake kira Yahuda Iskariyot, ya je wurin manyan firistoci
15 chengta, “Jisu ah jokoh ha bah an ih ngah suh tumjih kohang?” Neng ih ngunkholok lo rookjom ah rookweh rum ano Judas suh korumta.
ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi gare ku?” Sai suka ƙirga masa kuɗi azurfa talatin.
16 Erah sa dowa ih Judas ih Jisu ah neng suh jootkot suh rangwuung ban sok ruh eta.
Daga wannan lokaci, Yahuda ya yi ta neman zarafin da zai miƙa shi.
17 Toomuh Baanlo Kuwaang saakhoh thoon adi heliphante loong ah Jisu jiinni thokrum ano cheng rumta, “Khopi Romhoon phaksat ah an raangtaan ih maradoh khookham thuk he?”
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, sai almajiran suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
18 Heh ih baat rumta, “Samnuthung ni mih esiit je ah erah jiinnah kah an, eno heh suh baat an: ‘Nyootte ih liita, nga saapoot ah thok ehala; nga liphante nyia ngah ih Khopi Romhoon phaksat ah an nok nah phaksah ih eah.’”
Ya amsa ya ce, “Ku shiga gari wurin wāne, ku ce masa, ‘Malam ya ce, lokacina ya yi kusa. Zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina a gidanka.’”
19 Heliphante loong ah ih heh ih mamet baatta erah jun ih kuwaang phaksat ah khookham rumta.
Saboda haka almajiran suka yi yadda Yesu ya umarce su, suka kuwa shirya Bikin Ƙetarewa.
20 Rangjaako di, Jisu nyia heliphante asih wanyi loong ah phaksat suh tong rumta.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zauna don cin abinci tare da Sha Biyun.
21 Phaksat tokdi Jisu ih liita, “Ngah ih baat rumhala, sengdung dowa wasiit ih ngah ah mih suh khumtante ang hali.”
Yayinda suke cin abinci, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 Heliphante loong ah rapne ih thungthih rum ano wasiit wasiit ih cheng rumta, Teesu, Amiisak ih ngah suh maamok li jang oh?”
Suka yi baƙin ciki ƙwarai, suka fara ce masa da ɗaya-ɗaya, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
23 Jisu ih ngaakbaat rumta, “Nga damdoh khuungsiit ni roong phaksatte ih khuumtante ang halang.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya sa hannunsa a kwano tare da ni ne, zai bashe ni.
24 Mina Sah abah etek ete Rangteele ni raangha jun ih ah, enoothong tumthan echoojih ang ah Mina Sah khuumtante wah raang ih ah! Erah mih ah lalaan dong tup taha bah ese ang thengta!”
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda aka rubuta game da shi. Amma kaiton mutumin da zai bashe Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da ya fi masa.”
25 Judas, Jisu mokwaante wah, ah toonjengta. “Nyootte, an ih amiimi ngah suh maamok li jang oh?” Judas ih chengta. Jisu ih ngaakbaatta, “An ih liihu ah ju angte.”
Sa’an nan Yahuda, wanda zai bashe shi ya ce, “Tabbatacce ba ni ba ne, ko, Rabbi?” Yesu ya amsa ya ce, “I, kai ma ka fada.”
26 Neng phaksat phaksah rum adi, Jisu ih baanlo ah toonpi ano, Rangte suh lakookmi rangsoom ah soom ano, chepphiitta, eno heliphante loong asuh korum ano, “Phak an; ih baat rumta, “Arah ah nga sak.”
Yayinda suke cikin cin abinci, Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya ya kuma kakkarya, ya ba wa almajiransa yana cewa, “Ku karɓa ku ci; wannan jikina ne.”
27 Erah lilih heh ih lokkep ah toon ano, Rangte suh lakookmi liita, eno heliphante loong asuh korumta. “Jok an,” heh ih baatta;
Sa’an nan ya ɗauki kwaf, ya yi godiya, ya kuma ba su, yana cewa, “Ku shassha daga cikinsa, dukanku.
28 “Arah ah nga sih, Rangte nyia mina chamchi ni nuumiijeng tangmiin ha, nga sih ah miloong rangdah biin anaan suh jan ah.
Wannan jinina ne na sabon alkawari, wanda aka zubar saboda mutane da yawa, don gafarar zunubai.
29 Ngah ih baat rumhala, ngah ih arah kham ah babah uh takah jokkang seng Wah hasong nah sen damdoh kham na ah maang jokjok ah.”
Ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabin nan ba har sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a mulkin Ubana.”
30 Eno neng rangsoom boong ah boong rum ano Olip kong ni dokkhoom wang rumta.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
31 Eno Jisu ih neng suh baatta, “Niikja sen ih ngah ah thiinhaat heeno moongsoon ete, tumeah Rangteele ni liiha, ‘Rangte ih saapriimte ah tek haat et ah, eno saapsah loong phaangjaang eah.’
Sai Yesu ya ce musu, “A wannan dare, dukanku za ku ja da baya saboda ni, gama a rubuce yake cewa, “‘Zan bugi makiyayin, tumakin garken kuwa za su fasu.’
32 Enoothong ngah ewe ngaakthing eh ang doh, Ngah sen jaakhoh nah Galili hadaang adoh kah ang.”
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
33 Pitar ah toonjengta eno Jisu suh baatta, “Wahoh loong ih thiinhaat ho bah uh ngah ih bah tahiin haat ra!”
Bitrus ya amsa ya ce, “Ko da duka sun ja da baya saboda kai, ba zan taɓa ja da baya ba.”
34 Jisu ih Pitar suh baatta, “Ngah ih baat hala niikja woh we ngah ngah an ih ngah suh tajatkang ih lekjom liihang.”
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya maka, a daren nan, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 Pitar ih ngaakbaatta, “An damdoh roongtek jih ang adoh botseh emah ngah tajeng kang!” Eno heliphante wahoh loong eh uh emamah ih baat rumta.
Bitrus ya furta, “Ko da ma zan mutu ne tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Dukan sauran almajiran ma suka faɗa haka.
36 Eno Jisu ah heliphante damdi Getsemani et liiha hah adi kata, eno heh ih baat rumta, “Adoh ban tong an ngah therah doh rangsoom wang ang.”
Sa’an nan Yesu ya tafi da almajiransa zuwa wani wurin da ake kira Getsemane, ya ce musu, “Ku zauna nan, in je can in yi addu’a.”
37 Heh ih heh damdi Pitar nyia Jebidi sah wanyi ah siitwanta. Heh thungthet nyia heh mongsaam ah dong eta,
Ya ɗauki Bitrus da’ya’ya biyun nan na Zebedi tare da shi, sai ya fara baƙin ciki, ya kuma damu.
38 eno heh ih neng suh baatta, “Nga ten ah rapne ih satla etek thanthan ah. Adoh tong anno ngah bansok he.”
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har kamar zan mutu. Ku dakata a nan, ku kuma yi tsaro tare da ni.”
39 Heh amasah haloot ni heng khoomta, eno hah ni kotbon ano rangsoomta, “Ewah ejen lang eabah, arah ngah chamnaang lookkep ah toon et weeuh! Enoothong nga thung jun doh lah angthang ih, an thung jundoh ju toom ang ah.”
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in mai yiwuwa ne, a ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba nufina ba, sai naka.”
40 Eno heliphante wajom jiinni ngaak kah adi, neng ah emokjup ih rum arah kaptupta; eno heh ih Pitar suh baatta, “Senjom ih saapootsiit taan uh mamah lajen bansok et hali?
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya tarar suna barci. Ya tambayi Bitrus ya ce, “Ashe, ba za ku iya yin tsaro tare da ni ko na sa’a guda ba?
41 Rangsoom nah banban ih tong an sen phate joonnaam nah naktoom dat an. Chiiala abah enook taat ela, enoothong hansi ah ba naangla.”
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
42 Jisu leksiit rangsoom we wangta, “Ewah nga maang chamkang jaakhoh nah, chamchoh lookkep ah lajen toonhaat jih ang abah, an thung jun doh toom ang raaha.”
Ya sāke tafiya sau na biyu, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in ba zai yiwu a ɗauke wannan kwaf ba sai na sha shi, to, bari a aikata nufinka.”
43 Heh we ngaak kah adi heliphante loong ah mokjup ruh eh arah we japtup kata; neng mik uh tajen daapsok rumta.
Da ya dawo, har yanzu ya tarar suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi da barci.
44 Eno Jisu ah lekjom we wang ano, erarah ah we soomwangta.
Saboda haka ya sāke barinsu, ya yi addu’a sau na uku, yana maimaita iri abu guda.
45 Eno we ngaak ra haano heliphante loong asuh liita, “Amadi uh sen thok naangjup ruh nih elan? Sok an! Mina Sah ah rangdah miloong lak nah kot suh saapoot echang ela.
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya ce musu, “Har yanzu kuna barci kuna hutawa ba? Ga shi, sa’a ta yi kusa, an kuma bashe Ɗan Mutum a hannuwan masu zunubi.
46 Saat an, kah ih. Sok an, arah nga khuumtante mina rah ah!”
Ku tashi, mu tafi! Ga mai bashe ni nan yana zuwa!”
47 Jisu ih erah baat tokdi heliphante dung dowa Judas, dong khoom taha. Heh damdi mih loong hantek lang apah pan romwah phokhoh nyia hadaang phokhoh ih daapjah rum taha.
Yayinda yana cikin magana, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya iso. Tare da shi kuwa ga taro mai yawa riƙe da takuba da sanduna, manyan firistoci da dattawan mutane ne suka turo su.
48 Judas ih miloong asuh jatthukta: “Marah mih chupphak ang erah mih ah sen ih jam han rah ang ah. Eno erah ah khak an!”
To, mai bashe shi ɗin, ya riga ya shirya alama da su, “Wanda na yi masa sumba, shi ne mutumin; ku kama shi.”
49 Judas Jisu reeni phangla ih wang ano liita, “Semroongroong toomtong uh, Nyootte,” eno chupphakta.
Da zuwansa, sai ya miƙe zuwa wurin Yesu ya ce, “Gaisuwa, Rabbi!” Sa’an nan ya yi masa sumba.
50 Jisu ih ngaakbaatta, “Nga joonwah, tumjih raang ih wang halu, echaan eh uh!” Eno mih loong ah wang rum ano, Jisu ah jokhak rumta.
Yesu ya amsa ya ce, “Aboki, yi abin da ya kawo ka.” Sa’an nan mutanen suka matso, suka kama Yesu suka riƙe shi.
51 Jisu dam dowa mih wasiit ih heh lang ah heehoom ano Romwah Phokhoh dah, na ah chepdookta.
Ganin haka, sai ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu, ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne.
52 Jisu ih baatta, “An lang ah hetoop nah we ngaaksak uh, “O mina ih lang toon ah erah mina ah lang doh ti ah.
Sai Yesu ya ce, masa, “Mai da takobinka kube, gama duk masu zare takobi, a takobi za su mutu.
53 Sen ih tanih jatkan nga pangsuh seng Wah ah ejen poon et thengtang, eno lakdam damdoh rangsah sipaahi loong ah asih wanyi nang ih ehan et daapkaat theng taha?
Kuna tsammani ba zan iya kira Ubana, nan take kuwa yă aiko mini fiye da rundunar mala’iku goma sha biyu ba?
54 Enoothong, emah mok ang abah Rangteele ni elang jaatjaat etheng ih liiha ah amiisak doh mamah ma jen ang ah?
Amma ta yaya za a cika Nassin da ya ce dole haka yă faru?”
55 Eno Jisu ih miloong asuh liita, “Sen loong ah nga joot suh lang apah pan nih ra halan, ehuh elek jootjoot ah? Ngah ih Rangteenok ni tong ano saarookwih kah nyootsoot tang rah ah, erah di mamah lah joh ih tahe?
A wannan lokaci sai Yesu ya ce wa taron, “Ina jagoran wani tawaye ne, da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni? Kowace rana ina zama a filin haikali ina koyarwa, ba ku kuwa kama ni ba.
56 Enoothong arah loong ah khowah loong ih Rangteele ni raangthiin rumta ra amiisak toom ih pun raaha ih angla.” Eno heliphante loong ah heh ah thiinhaat rum ano thoontang moongsoon rumta.
Amma wannan duka ya faru ne don a cika rubuce-rubucen annabawa.” Sa’an nan dukan almajiran suka yashe shi suka gudu.
57 Jisu khakte loong ah ih Romwah Phokhothoon Kaiphas nok adi siitwan rumta, erah di Hootthe nyootte nyia hadaang phokhothoon loong lomtong rumta
Waɗanda suka kama Yesu kuwa suka kai shi wurin Kayifas, babban firist, inda malaman dokoki da dattawa suka taru.
58 Pitar ah haloot nawa neng lilih ih wang ano Romwah Phokhothoon nok adi thok phanjoh wanta. Pitar ah nokmong ni nopkhoom wang ano, sipaahi loong damdi roongtong wang ano mamah angthaak ah ih ban sokta.
Amma Bitrus ya bi daga nesa, har zuwa cikin filin gidan babban firist. Ya shiga, ya zauna tare da masu gadi, don yă ga ƙarshen abin.
59 Romwah Phokhoh loong nyia ah Ngoong awang loong ah ih lalangka di Jisu jen tek haat theng mat ih joot suh taat chung rumta;
Sai manyan firistoci da’yan majalisa duka suka yi ta neman shaidar ƙarya a kan Yesu, don su sami dama su kashe shi.
60 enoothong warep ih Jisu tiit hahuung baat suh taat wang rumha bah uh, hahuung tiit baat suh lampo tajeeta. Hethoondi wanyi toonchap ano
Amma ba su sami ko ɗaya ba, ko da yake masu shaidar ƙarya da yawa sun firfito. A ƙarshe, biyu suka zo gaba,
61 baat nyuuta, “Arah mih rah ih liita, ‘Ngah ih Rangteenok ah thaak haat ang no, sa jom doh we jen hoon ang eah.’”
suka furta cewa, “Wannan mutum ya ce, ‘Ina iya rushe haikalin Allah, in sāke gina shi cikin kwana uku.’”
62 Romwah Phokhothoon ah toonchap ano Jisu suh liita, “An tiit erah thetbaat halu adi ngaak jengjih tatam jeeka?”
Sa’an nan babban firist ya miƙe tsaye, ya ce wa Yesu, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”
63 Enoothong Jisu ah su su ih tongta. Eno Romwah Phokhothoon ah ih we chengta, “Ething Rangte mendi ngah ih an suh thoomhoon thuk hala: baat thaak uh, Rangte Sah Kristo ang uh bah ah.”
Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na haɗa ka da Allah mai rai. Faɗa mana in kai ne Kiristi, Ɗan Allah.”
64 Jisu ih ngaakbaatta, “An ih liihu ah ju ang ah. Enoothong ngah ih sen loong suh baat rumhala: aadowa ih Mina Sah ah sen ih Elong Rangte damdoh jaawako nah tong arah nyia rangmong hasong nawa jiingmuung damdoh raaha rah tup an!”
Sai Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake yadda ka faɗa. Sai dai ina gaya muku duka, nan gaba, za ku ga Ɗan Mutum zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a kan gizagizan sama.”
65 Erah dowa ih Romwah Phokhothoon rah ih heh nyuh ah ranhoom ano liita, Rangte kaanju hu! Erah tokkhodoh wahoh haaki takah jamke! Sen ih Rangte kaanju tiit belam jengta rah echaat ettan.
Sa’an nan babban firist ya yage tufafinsa ya ce, “Ya yi saɓo! Don me muke bukatar ƙarin shaidu? Ga shi, yanzu kun dai ji saɓon.
66 Sen ih mamet thunhan?” Miloong ah li rumta, “Heh emoong ela eno tek haat jaatjaat etjih.”
Me kuka gani?” Suka amsa, suka ce, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Eno heh the adi took rum ano buh rumta; erah dam ih heh botte rah ih
Sai suka tottofa masa miyau a fuskarsa, suka kuma bubbuge shi da hannuwansu. Waɗansu kuma suka mammare shi
68 liita, “Seng tiit ah taat ban jat thaak uh Kristo ang uh bah ah! Jatthaak uh o eh buh taho!”
suka ce, “Yi mana annabci, Kiristi. Wa ya buge ka?”
69 Pitar ah nok taakkhuung ni tong adi Romwah Phokhothoon laksuh minuh ah kah ano liita, “An nep Galili nawa Jisu damdi angtu.”
To, Bitrus yana nan zaune a filin, sai wata yarinya baiwa, ta zo wurinsa. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu mutumin Galili.”
70 Eno heh ih loongtang dung ni daanta. “An ih tumjih tiit baat hu erah ngah ih tajatkang,” Pitar ih ngaakbaat ano,
Amma ya yi mūsu a gabansu duka. Ya ce, “Ban san abin da kike magana ba.”
71 erah dowa kaawan ko ih dokkhoom kata. Romwah Phokhoh laksuh nuhoh ih we tup ano erah dowa miloong asuh baat rumta, “Najaret dowa Jisu damdi heh angta.”
Sa’an nan ya fito zuwa hanyar shiga, inda wata yarinya kuma ta gan shi, ta ce wa mutanen da suke can, “Wannan mutum ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 Eno Pitar ih daan ano we ngaak liita, “Ngah ethoom nep jen eang ngah ih erah mih ah tajatkang!”
Ya sāke mūsu har da rantsuwa, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba!”
73 Amasah ritdi erah di chap rumta miloong ah Pitar reeni kata. “Amiimi anbah neng dam dowa ju angkoko,” Miloong ah ih liita. “Sen Galili nok hah loong ah sen jeng nawa ih jatjoh hi!”
Bayan ɗan lokaci, sai na tsattsaye a wurin, suka hauro wurin Bitrus, suka ce, “Tabbatacce, kai ɗayansu ne, don harshen maganarka, ya tone ka.”
74 Eno Pitar ih liita, “Ngah ih thoomhoon damdi ami tiit baat rumhala! Rangte ih toomjat kohang, ngah ih tajatkang liitang ah hahuung tiit baatkang bah ah! Ngah ih erah mih ah tajatkang!” Erah damdam woh ah weeta,
Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantsuwa yana ce musu, “Ban ma san mutumin nan ba!” Nan da take, sai zakara ya yi cara.
75 eno Pitar ih Jisu jengta ah samthunta: “Woh maang weeka doh an ih tajatkang ih lekjom jeng uh.” Heh dokkhoom kah ano rapne ih huung kata.
Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi cewa, “Kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sani na sau uku.” Sai ya fita waje, ya yi ta kuka.