< Luk 3 >

1 Luungwanglong Teberius ih asih paang banga phansiit adi; Pontius Pilat ah Judia ni Kobono angta, Hirod ah Galili phansiitte angta, heh no Philip ah langla Ituria nyia Trakonite phansiitte angta; Lisania ah Abilini hadaang phansiitte angta,
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
2 eno Annas nyia Kaiphas ah romwah phokhothoon ang nyuuta. Erah tokdi phisaang hah ni Jekaria sah Joon suh Rangte ih jengkhaap baatta.
A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
3 Eno Joon ih Jordaan Juungko ni Rangte tiit ah tumbaat kaatta, “Sen rangdah nawa ngaak hanno juungtem an, eno ba Rangte ih sen rangdah ah biin anaan han.”
Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
4 Erah ah khowah Isaia leedap ni raangthiin cho angta: “Mih phisaang hah ni riingla; ‘Teesu raang ih lam ban hoon thiin an; Heh khoomtheng lamjun ih tan an!
Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
5 Hoongbeng haleng loong ah ebook et ah, kong akaan loong ah hoongthung hane ih hoon ah. lam koongkot loong ah lamjun ih hoon ah, lamthih loong ah lamse ih hoon ah.
Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
6 Rangte jiin nawa khopiiroidong ah warep ih tup ah!”
Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
7 Miloong hantek Joon ih juungtem toom tem he ih ra rum taha. Joon ih liirumta, “Pu sen loong ah!” “O ih baat tahan Rangte ih echamnaang theng daapkaat ha dowa sen epui etheng eah?
Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Rangdah nawa elek elang ih sen reeraang pakna nawa ih noisok anbah. Sen chamchi nah seng Abraham sutoom ih laklak nakwaan an. Abraham sutoom bah Rangte ih jong ah toon ano botseh jen hoon et ah!
Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
9 Bang hehing nah joot haat suh chaang ah ban thiin et ha; hetiikmuh bang loong ah joot haat ano we nah haattak ah.”
An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
10 Miloong ih heh suh cheng rumta, “Erah ang abah, seng ih tumjih et theng ah?”
Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
11 Heh ih ngaakbaat rumta, “O di samsong enyi jeela esiit ah samsong mute suh kotjih, erah damdi o di phaksat jeela rah ih pheekot et theng.”
Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
12 Mararah sokse seete nep juungtem ra taha, eno cheng rumta, “Nyootte, seng ih tumjih reejih ah?”
Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
13 Eno Joon ih baat rumta, “Sokse mathan seejih ah erah ba se an erah tokkhodoh ehan nak mook se an.”
Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
14 Mararah sipaahi ih nep heh suh cheng rumta, seng ih aleh? Tumjih etjih ah? Heh ih baat rumta, “Mih dowa ngun chaan ih nakmok suh an adoleh mih lathika doh ethih etu ih nak nan an. Sen ngun la di mathan cholan erah suh roon an.”
Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
15 Mina loong ah ih choocho ih dong laalom rumta, eno neng ih Joon asuh Kristo tam angla ih thun rumta.
Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
16 Eno Joon ih loongtang suh baat rumta, “Ngah ih juung nawa ih juungtem rumhala, enoothong nga lini mih wasiit nga nang ih elong raaha. Ngah bah heh lakhoop pak taajoh tha uh taliikang. Heh ih bah Esa Chiiala nyia we nawa ih juungtem han.
Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
17 Heh jiinni nunrek je ah, erah ih raan ah dannun ano pung nah toonthiin ah, eno hephaang loong ah we nah babah uh lamettheng adoh tak ah.”
Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
18 Joon ih hejaat hejaat lam nawa ih miloong asuh Ruurang Ese ah nyootsoot leh neng roidong ah elek raangtaan ih baat rumta.
Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
19 Enoothong Joon ih Kobono Hirod asuh liita, tumeah heh ih Hirodias heh no minuh ah, kapta, erah damdi uh ethih loong ephoop reeta.
Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
20 Hirod ih Joon ah phaatak ni sakta rah boot thetreeta.
Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
21 Miloong juungtem lini, Jisu ih nep heh juungtem ah we temta. Heh ih rangsoom adi, rang kaasak ah daap eta,
Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
22 eno Esa Chiiala ah hansi ni wotuupi likhiik heh khothung ni datpura taha. Eno rang ni root esiit dongjengta, “An ah nga mongnook sah. Ngah an suh eroon elang.”
Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
23 Jisu heh mootkaat phangmota tokdi, Heh ah paang rookjom taan angta. Heh ah miwasah, erah raang ih miloong ih, Josep sah ih thunta, Josep ah Heli sah angta,
To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
24 Heli ah Mathat sah, Mathat ah Leewi sah, Leewi ah Melki sah, Melki ah Jannai sah, Jannai ah Josep sah,
ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
25 Josep ah Mattathias sah, Mattathias ah Amos sah, Amos ah Nahum sah, Nahum ah Esli sah, Esli ah Naggai sah,
ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
26 Naggai ah Maath sah, Maath ah Mattatthias sah, Mattatthias ah Semin sah, Semin ah Joseek sah, Joseek ah Joda sah,
ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
27 Joda ah Joonan sah, Joonan ah Resa sah, Resa ah Jerubabel sah, Jerubabel ah Siltiel sah, Siltiel ah Neri sah,
ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
28 Neri ah Melki sah, Melki ah Addi sah, Adidi ah Kosam sah, Kosam ah Elmadiam sah, Elmadiam ah Er sah,
ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
29 Er ah Josua sah, Joshua ah Eliijer sah, Eliijer ah Jorim sah, Jorim ah Matthat sah, Matthat ah Leewi sah,
ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
30 Leewi ah Simoon sah, Simoon ah Judah sah, Juda ah Josep sah, Josep ah Joonam sah, Joonam ah Elaikim sah
ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
31 Elaikim ah Melea sah, Melea ah Menna sah, Menna ah Mattatha sah, Mattatha ah Nathan sah, Nathan ah Dewid sah,
ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
32 Dewid ah Jiisi sah, Jiisi ah Obed sah, Obed ah Booj sah, Booj ah Salmon sah, Salmon ah Nason sah,
ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
33 Nason ah Aminadab sah, Aminadab ah Admin sah, Admin ah Arni sah, Arni ah Hejron sah, Hejron ah Perej sah, Perej ah Judah sah
ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
34 Juda ah Jaakob sah, Jakob ah Isak sah, Esak ah Abraham sah, Abraham ah Terah sah, Terah ah Nahor sah,
ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
35 Nahor ah Serug sah, Serug ah Reu sah, Reu ah Peleg sah, Peleg ah Eber sah, Eber ah Sela sah,
ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
36 Sela ah Kiinan sah, Kiinan ah Arphaksad sah, Arphaksad ah Sem sah, Sem ah Nuah sah, Nuah rah Lameek sah,
ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
37 Lameek ah Methuselah sah, Mathuselah ah Enook sah, Enook ah Jared sah, Jared ah Mahalalil sah, Mahalalil ah Kenan sah,
ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
38 Kenan ah Enosh sah, Enosh ah Seth sah, Seth ah Adam sah, Adam ah Rangte sah.
ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.

< Luk 3 >