< Joon 18 >

1 Jisu ih rang ah jensoom ano, Kidron joisah saangko heliphante loong damdi daankata. Erah di pa esiit angta, eno Jisu nyia heliphante loong ah erah di nopwang rumta.
Da ya gama addu’a, sai Yesu ya fita tare da almajiransa suka haye Kwarin Kidron. A wancan ƙetaren kuwa akwai lambun zaitun, da shi da almajiransa suka shiga ciki.
2 Jisu jootkotte Judas ih erah pa ah mani angta erah jat eta, tiimnge liidi heliphante loong ah damdi Jisu erah di hepoot hepoot pakchomui roh ka ih rumta.
To, Yahuda, wanda ya bashe shi, ya san wurin, domin Yesu ya sha zuwa wurin da almajiransa.
3 Erah thoidi romwah phokhothoon nyia Pharisi nok hah loong ah ih Judas damdi Room nok hah sipaahi nyia Rangteenook bante loong ah langpi papi ih wangthuk rumta, eno neng loong ah weetook nyia phiitwe ah piirum ano erah pa adi nopwang rumta.
Saboda haka Yahuda ya zo cikin lambun, yana jagoranta ƙungiyar sojoji da waɗansu ma’aikata daga wurin manyan firistoci da Farisiyawa. Suna riƙe da toci, fitilu da kuma makamai.
4 Jisu ih heh teeteewah ah mamah theng ah, erah banjat eta, eno neng taangko ih tiitkhoom kah ano cheng rumta, [O jam han sen ih ah?]
Yesu kuwa, sane da duk abin da zai same shi, ya fito ya tambaye, su ya ce, “Wa kuke nema?”
5 “Najaret dowa Jisu,” neng loong ah ih ngaakbaat rumta. “Erah liihan abah ngah,” Jisu ih baat rumta. Mih khumtante, Judaas, ah erah di roongchap wangta.
Suka amsa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce, “Ni ne shi.” (Yahuda kuwa wanda ya bashe shi yana nan tsaye tare da su.)
6 Jisu ih [Erah liihan abah ngah ngeh ih liikano[ neng liko ih ngaakchap rum ano hah ni loongjup rumta.
Da Yesu ya ce, “Ni ne shi,” sai suka ja da baya suka fāɗi a ƙasa.
7 Jisu ih weengaak cheng rumta, “O jam han sen ih ah?” “Najaret dowa Jisu,” neng loong ah ih liita.
Sai ya sāke tambayar su ya ce, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.”
8 [Ngah ih jen baat ih rum taha erabah ngah ngeh ah.] Jisu ih baat rumta, [Ngah jam hali bah wahoh loong ah ngaakkaat ih thuk an.’’ Jisu ih emah ih li rumta. (
Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku ni ne shi. In kuma ni ne kuke nema, to, sai ku bar waɗannan su tafi.”
9 Heh ih maangdi ban baatta ah amiisak ih angsuh neng loong asuh emah li rumta, Jisu ih Hewah rang ah emah ih soomta: [Ewah! An ih kotahang miloong ah wasiit taan uh ngah ih mat haatmuh.])
Wannan ya faru ne don a cika kalmomin da ya yi cewa, “Ban yar da ko ɗaya daga cikin waɗanda ka ba ni ba.”
10 Simon Pitar ih lang esiit huita, erah dokkhoom ano Romwah phokhothoon dah na ah dakmiiko ah dat dookta. Erah dah men ah langla Malkus ngeh angta.
Sai Siman Bitrus, wanda yake da takobi, ya zāre, ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama (Sunan bawan kuwa Malkus ne.)
11 Jisu ih Pitar suh liita, [An lang ah hetoop adoh sak hui uh! Seng Wah ih kohalang chamnaang lookkep adoh tajokka nih thun hu?]
Sai Yesu ya umarce Bitrus ya ce, “Mai da takobinka kube! Ba zan sha kwaf da Uba ya ba ni ba?”
12 Eno Room nawa sipaahi nyia neng saahaap, erah damdi Jehudi nok hah bante loong ah ih Jisu ah jorum ano kit rumta,
Sai ƙungiyar soja tare da shugaban sojanta da kuma ma’aikatan Yahudawa suka kama Yesu. Suka daure shi
13 jaakhoh thoon ah Kaiphas hopwah Anna reeni siitwan rumta, erah paang adi Kaiphas ah Romwah Phokhothoon angta.
sa’an nan suka kawo shi da farko wurin Annas, wanda yake surukin Kayifas, babban firist a shekaran nan.
14 Jehudi ngoong awang loong asuh loongtang raang ih wasiit tek ah eseethoon ang ah ngeh ih hukbaatte ah Kaiphas angta.
Kayifas ne wanda ya shawarci Yahudawa cewa zai fi kyau mutum ɗaya yă mutu saboda mutane.
15 Pitar nyia heliphante wahoh wasiit Jisu lilih ih phankhoom kanyuuta. Erah heliphante ah Romwah Phokhothoon damdi menjat ang thoidi, Romwah Phokhothoon nok taakkhu ni Jisu damdi waknop wangta,
Siman Bitrus da kuma wani almajiri suna bin Yesu. Domin almajirin nan sananne ne ga babban firist, sai ya shiga tare da Yesu a filin gidan babban firist ɗin,
16 eno Pitar ah paakaawan adi banchapta. Heliphante ah kaalu ko ngaak kah ano jaalasah nusiit chapta asuh baat ano Pitar ah waknopsiit wanta.
Bitrus kuwa ya dakata a waje a bakin ƙofa. Almajirin nan da yake sananne ga babban firist, ya dawo ya yi magana da yarinyar mai aiki a can, ya kuma shigo da Bitrus.
17 Enoothong jaalasah rah ih kaalu adi Pitar suh chengta, [An uh Jisu liphante tanih angkoko?] [Ngah tah angkang, ] Pitar ih ngaakbaatta.
Yarinyar da take bakin ƙofar ta ce wa Bitrus, “Kai ba ɗaya ne daga cikin almajiran mutumin nan ba ne?” Bitrus ya amsa ya ce, “A’a, ba na ciki.”
18 Song ang kano, laksuh nyia bante loong ah we ah takrum ano songlom suh weekaang ni kookchap rumta. Erah di Pitar ah wang ano weekaang ni roong lomchap wangta.
To, ana sanyi, bayi da ma’aikatan suna tsattsaye kewaye da wutar da suka hura don su ji ɗumi. Bitrus ma yana tsaye tare da su, yana jin ɗumi.
19 Romwah Phokhothoon ih Jisu suh heliphante loong tiit nyia heh ih nyootsootta ah chengta.
Ana cikin haka, sai babban firist ya tuhumi Yesu game da almajiransa da kuma koyarwarsa.
20 Jisu ih ngaakbaatta, “Saarookwet ngah nokraat ni mirep suh saasa ih jenglang; Jehudi rangsoomnok ni nyia Rangteenok ni, maradi miloong ah kalomkhoon rum taha di ah. Mabah uh ngah husah ni jengmuh
Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na yi wa duniya magana a fili. Na kuma sha yin koyarwa a majami’u ko kuma a haikali inda Yahudawa duka sukan taru. Ban taɓa faɗin kome a ɓoye ba.
21 An ih emah tiim esuh cheng halang? Nga jeng boichaatte loong asuh cheng uh. Ngah ih tiimjih baat rumtang neng ih chaat eta.]
Don me kake tuhumata? Ka tambayi waɗanda suka ji ni. Ba shakka, sun san abin da na faɗa.”
22 Jisu ih emah li kano, bante dowa wasiit ih hethe ni baangbuh ano liita, [Romwah Phokhothoon suh an ih emah mamah naan liihu!]
Da Yesu ya faɗa haka, sai ɗaya daga cikin ma’aikatan da yake tsaye kusa ya mare shi a fuska ya ce, “Haka za ka amsa wa babban firist?”
23 Jisu ih heh suh ngaak liitta, “Ngah tiim bah uh mokjeng etang bah, mirep suh adoh baat uh. Enoothong ngah tiim jengtang erah punjeng etang baleh tiim esuh buh halang?]
Yesu ya amsa ya ce, “In na faɗi abin da ba daidai ba, ka nuna abin da ba daidai ba. Amma in gaskiya na faɗa, don me ka mare ni?”
24 Annas ih Jisu ah kitchoi Romwah Phokhothoon Kaiphas taang ni wangthukta.
Sai Annas ya aika da shi, a daure, wurin Kayifas babban firist.
25 Erah di Pitar ah weekaang ni chaproh eta. Erah thoidi miloong ah ih cheng rumta, [An uh erah wah liphante taba ang koko?] Pitar ih weeliita, [Ngah ah tah angkang.]
Da Siman Bitrus yana nan tsaye yana jin ɗumin wuta, sai aka tambaye shi, “Kai, kai ma ba ɗaya daga cikin almajiransa ba ne?” Sai ya yi mūsu, yana cewa, “Sam, ba na ciki.”
26 Romwah Phokhothoon dah wasiit, Pitar ih heh na datdook ta phoh awah erah di eje angta. Erah dah rah ih liita, [Jisu damdi pa ni taba tup taha?]
Sai wani daga cikin bayin babban firist dangin wanda Bitrus ya sare wa kunne, ya tambaya shi ya ce, “Kana tsammani ban gan ka tare da shi a gonar zaitun ba?”
27 Eno Pitar we leekta, Tajatkang—erah damdam ih woh ah weeta.
Bitrus ya sāke yin mūsu, nan take kuwa zakara ya yi cara.
28 Rangkhano ih Kaiphas nok nawa Jisu ah Kobono noklong ni siitwan rumta. Neng banlam di Khopi kuwaang miiphaksat suh neng ah esa ang theng, erah thoidi Jehudi ngoong awang loong ah kobono nokmong ni tanop wang rumta.
Sa’an nan Yahudawa suka fitar da Yesu daga wurin Kayifas zuwa fadar gwamnar Roma. A yanzu dai, safiya ta yi, don gudu kada su ƙazantar da kansu Yahudawa ba su shiga cikin fadar ba; sun so su iya ci Bikin Ƙetarewa.
29 Erah thoidi Pilat ah dokkhoom kah ano chengkah rumta, [Arah mih ah tiim thoidi jowan halan?]
Saboda haka Bilatus ya fito wajensu ya ce, “Wace ƙara kuke kawowa game da mutumin nan?”
30 Neng ih ngaakbaatta, [Lamoongre dobah an suh ju tajoot kot wantheng tahe.]
Suka amsa suka ce, “Da a ce shi ba mai laifi ba ne, ai, da ba mu bashe shi gare ka ba.”
31 [Emah ang abah sen hootthe jun ih mat ah taat hoonkaat thaak an.] Pilat ih baat rumta. Jehudi loong ah ih ngaakli rumta, [Seng ih mih tami tek haatke.] (
Bilatus ya ce, “Ku tafi da shi da kanku mana, ku hukunta shi bisa ga dokarku.” Sai Yahudawa suka ƙi suka ce, “Ba mu da ikon yanke wa wani hukuncin kisa.”
32 Erah langla Jisu ih heh mamah ih tektheng ah erah tiit ban baatta ah wuusa nah amiimi dong angsuh jeng rumta.)
Wannan kuwa ya faru ne don a cika kalmomin da Yesu ya yi da suka nuna irin mutuwar da zai yi.
33 Pilat ih Jisu nokmong ni poonwan ano cheng wanta, [An Jehudi Luuwang nih ah?]
Sai Bilatus ya koma cikin fada, ya kira Yesu ya tambaye shi, “Shin, kai ne sarkin Yahudawa?”
34 Jisu ih ngaakbaatta, [Nga tiit ah an thung ih tamcheng halang tam aleh mih ih baat ho ih cheng halang?]
Yesu ya yi tambaya ya ce, “Wannan ra’ayin kanka ne, ko waɗansu ne suka yi maka magana game da ni?”
35 Pilat ih ngaak liita, [Ngah suh Jehudi nok hah nih li halang? An mina loong nyia romwah phokhoh loong ih ba jokoh wanrum halang. An tiimjih ih kotu?]
Bilatus ya amsa ya ce, “Ni mutumin Yahuda ne? Ai, mutanenka ne da kuma manyan firistoci suka bashe ka gare ni. Me ka yi?”
36 Jisu ih ngaakbaatta, [Nga hasong ah arah mongrep hasong tah angka; arah mongrep hasong angta bah nga lih phanjootte loong ah Jehudi ngoong awang suh lajoot thuksuh mui etheng rumta. Nga hasong bah mongrep hasong tah angka.]
Yesu ya ce, “Mulkina ba na duniyan nan ba ne. Da na duniyan nan ne da bayina sun yi yaƙi su hana Yahudawa kama ni. Amma fa mulkina daga wani waje ne.”
37 Eno Pilat ih Jisu suh chengta, [Enoobah, an luuwang tam ah?] Jisu ih ngaakbaatta, [An ih liitu ngah luuwang ngeh ah. Ngabah dongtup hangno arah mongrep adi jisiit raangtaan ih ra tahang, erah langla amiitiit ah baat suh. O mina amiisak mih ang ah erah ih nga jeng ah boichaat hang.
Sai Bilatus ya ce, “To, wato, kai sarki ne!” Yesu ya amsa ya ce, “Haka yake, ni sarki ne yadda ka faɗa. Tabbatacce, saboda wannan dalili ne aka haife ni, kuma don wannan ne na zo duniya, domin in shaidi gaskiya. Duk wanda yake gefen gaskiya yakan saurare ni.”
38 “Enoobah amiitiit ah tiimah?” Pilat ih chengta. Eno Pilat ah weengaak dokkhoom kah ano miloong asuh liikah rumta, [Heh tiim thoilam doh thet haat theng ah ngah ebah tah jatjoh kang.
Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Mece ce gaskiya?” Da ya faɗi haka, sai ya sāke fitowa wurin Yahudawa ya ce, “Ni fa ban sami wani abin zargi game da shi ba.
39 Enoothong sen banlam di, Khopiikuh rookwet sen raangtaan ih phaatak nawa wasiit ah daap haat koroh erum hala. Sen loong raangtaan ih Jehudi luuwang ah daap haat kot ah tamjam han?”
Amma fa kuna da wata al’ada in lokacin Bikin Ƙetarewa ya yi, nakan sakar muku da ɗan kurkuku ɗaya. To, kuna so in sakar muku ‘sarkin Yahudawa’?”
40 Neng loong ah ih riiraak damdi ngaakbaat rumta, “Heh tah angka! Barabbas jamhi! (Barabbas ah miputte angta.)
Sai suka ɗau kururuwa suna cewa, “Kai, ba shi ba! A ba mu Barabbas!” To, Barabbas ɗin nan yana da hannu dumu-dumu a wani tawaye.

< Joon 18 >