< Acts 2 >

1 Jitia Pentecost din ahise, biswasi khan sob ek jagah te joma hoise.
Da ranar Fentekos ta yi, dukansu suna tare wuri ɗaya.
2 Aru achanak ta te awaj ekta sorgo pora ahise, aru taikhan bohi thaka pura ghor to bhorta hoi jaise.
Ba zato ba tsammani sai aka ji motsi kamar ta babbar iska tana hurowa daga sama ta kuma cika dukan gidan da suke zaune.
3 Titia taikhan age te juli thaka jui nisena ulaise, aru ekjon-ekjon uporte bohi jaise.
Suka ga wani abin da ya yi kama da harsunan wuta, suka rarrabu suna kuma sassauka a kan kowannensu.
4 Aru taikhan sob Pobitro Atma pora bhorta hoise aru alag kotha pora kobole shuru hoise, Atma pora taikhan ke dusra bhasa pora kobole sikhai dise.
Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka kuma fara magana da waɗansu harsuna yadda Ruhu ya sa suka iya.
5 Aru Jerusalem te Isor jana Yehudi manu khan thakise, aru akas nichete thaka sob desh pora ahikena ta te thakise.
To, a Urushalima akwai Yahudawa masu tsoron Allah, daga kowace ƙasa a duniya.
6 Aru jitia etu awaj ulaise, ta te manu khan sob ahi kene asurit lagise kelemane taikhan nijor laga kotha pora koi thaka hunise.
Da suka ji wannan motsi, taro ya haɗu wuri ɗaya a ruɗe, domin kowannensu ya ji suna magana da yarensa.
7 Titia taikhan sob asurit hoi jaise; aru taikhan koise, “Sabi, etu kotha koi thaka khan Galilee manu khan nohoi naki?
Cike da mamaki, suka yi tambaya suna cewa, “Ashe, duk waɗannan mutane masu magana ba Galiliyawa ba ne?
8 Tenehoile kineka taikhan laga mukh pora amikhan ki kotha koi kene jonom korise etu kotha koi ase?
To, yaya kowannenmu yana ji suna yarensa?
9 Parthia laga aru Mede aru Elam laga, aru kun Mesopotamia te thake, Judea aru Cappadocia, Pontus aru Asia te,
Fartiyawa, Medes da Elamawa; mazaunan Mesofotamiya, Yahudiya da Kaffadokiya, Fontus da Asiya,
10 Phrygia aru Pamphylia, Egypt aru Cyrene usorte Libya, aru Rome phale jai thaka manu khan,
Firjiya da Famfiliya, Masar da sassa Libiya kusa da Sairin; baƙi daga Roma
11 aru Yehudi aru proselyte khan, Crete manu khan aru Arab manu khan, taikhan Isor laga dangor aru asurit kaam kora to amikhan laga bhasa pora koi thaka to hunise.”
(Yahudawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci); Kiretawa da Larabawa, mun ji su suna shelar abubuwan banmamaki na Allah da yarenmu!”
12 Taikhan sob asurit pora bhabona kori kene, aru ekjon-ekjon ke koise, “Etu laga ki motlob ase?”
A ruɗe kuma cike da mamaki, suka tambayi junansu cewa, “Mene ne wannan yake nufi?”
13 Kintu dusra biswasi khan pora sorom khilai kene koise, “Taikhan nisa pani kori kene ase.”
Duk da haka waɗansu suka yi musu ba’a suka ce, “Sun yi tatil da ruwan inabi ne.”
14 Kintu Peter egaroh jon logote khara hoi kene jor pora taikhan ke koise, “Judea laga manu khan aru Jerusalem te thaka khan, apnikhan etu jani lobi, aru moi ki koi ase etu bhal kori kene huni lobi.
Sai Bitrus ya miƙe tsaye tare da Sha Ɗayan nan, ya ɗaga muryarsa ya yi wa taron jawabi ya ce, “’Yan’uwana Yahudawa da dukanku da kuke zama cikin Urushalima, bari in bayyana muku wannan, ku saurara da kyau ga abin da zan faɗa.
15 Kintu etu manu khan to apuni khan pora bhabona kora nisena nisa pani khai kene thaka nohoi, kelemane etiya phojur nou-baji he ase.
Waɗannan mutane ba su bugu ba, kamar yadda kuka ɗauka. Yanzu ƙarfe tara na safe ne kawai!
16 Kintu etu kotha bhabobadi Joel pora koise:
A’a, ai, abin da aka yi magana ta bakin annabi Yowel ke nan cewa,
17 ‘Eneka hekh dinte hobo, Isor pora koise, Moi laga Atma sob manu uporte di dibo Tumikhan laga chokra chukri khan pora bhabobani koribo, Aru jawan manu khan darshan pabo, Aru bura manu khan sapna dikhibo.
“Allah ya ce, ‘A kwanakin ƙarshe, zan zubo Ruhuna bisa dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, samarinku za su ga wahayoyi, dattawanku kuma za su yi mafarkai.
18 Aru Moi laga noukar aru mahila noukar khan uporte Moi laga Atma di dibo, aru taikhan bhabobani kobo.
Kai, har ma a kan bayina, maza da mata, zan zubo Ruhuna a waɗancan kwanaki, za su kuwa yi annabci.
19 Moi akas Aru prithibi te asurit kaam dikhai dibo, Khun aru jui aru dhuwa laga bhap.
Zan nuna abubuwan banmamaki a sararin sama da alamu a nan ƙasa, jini da wuta da kuma hauhawan hayaƙi.
20 Titia suryo to andhera hoi jabo Aru chand to khun nisena dikhibo, Probhu laga dangor mohima din naha age te eitu khan sob hobo.
Za a mai da rana duhu, wata kuma ya zama jini, kafin zuwa rana mai girma da kuma ta ɗaukaka ta Ubangiji.
21 Aru jun manu hekh homoi tak Probhu laga naam loi kene thake tai bachi jabo.’
Kuma duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.’
22 Israel laga manu khan, etu kotha huni bhi, Nazareth Jisu eneka manu thakise junke Isor pora tumikhan nimite pathai dise dangor aru asurit kaam kori bole nimite, aru etu sob Isor pora Probhu Jisu ke loi kene korise, aru etu sob tumikhan pora dikhise.
“Mutanen Isra’ila, ku saurari wannan. Yesu Banazare shi ne mutumin da Allah ya tabbatar muku ta wurin mu’ujizai, ayyukan banmamaki, da kuma alamu, waɗanda Allah ya yi a cikinku ta wurinsa, kamar yadda ku kanku kuka sani.
23 Tai Jisu to, Isor pora kineka age pora bhabona korise aru tai laga gyaan pora, Jisu ke biya manu hathte di dise, aru tumikhan Taike gojal mari kene ekta Cross te morai dise.
An ba da wannan mutum gare ku bisa ga nufin Allah da kuma rigyasaninsa, ku kuma tare da taimakon mugayen mutane, kuka kashe shi ta wurin kafa shi a kan gicciye.
24 Tai ekjon ase junke Isor mora pora jinda kori dise, mora pora taike chari dise, kelemane Taike mora pora aru bandhi rakhibole para nai.
Amma Allah ya tashe shi daga matattu, ya’yantar da shi daga azabar mutuwa, don ba ya yiwuwa mutuwa ta riƙe shi.
25 Kelemane David Tai nimite koise, ‘Moi Probhu ke hodai moi laga chehera usorte dikhe, Tai moi laga dyna hathte thake, moi biya rasta te najabo nimite.
Dawuda ya yi faɗi game da shi cewa, “‘Kullum ina ganin Ubangiji a gabana. Gama yana a hannuna na dama, ba zan jijjigu ba.
26 Etu karone, moi laga mon khushi ase aru moi laga jiba pora dhanyavad kore. Aru, moi laga gaw bhi biswas te jinda thakibo.
Saboda haka, zuciyata na farin ciki, harshena kuma na murna, jikina kuma zai kasance da bege,
27 Kelemane Apuni moi laga jibon Hades te chari nadibo, Aru Apuni laga Pobitro Jonke puchibo nadibo. (Hadēs g86)
gama ba za ka bar ni cikin kabari ba, ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Hadēs g86)
28 Apuni moike jibon laga rasta dikhai dise; Aru apuni laga usorte moike khushi pora bhorta kori dibo.’
Ka sanar da ni hanyoyin rai, za ka cika ni da farin ciki a gabanka.’
29 Bhai khan, moi apuni khan ke etu kobole pari ase ki amikhan laga purush-Baba David pora ki kaam korise, aru tai morise aru taike kobor dise, aru tai laga kobor aji tak amikhan logote ase.
“’Yan’uwa, zan iya tabbatar muku gabagadi cewa kakanmu Dawuda ya mutu aka kuma binne shi, kabarinsa kuwa yana a nan har yă zuwa yau.
30 Etu karone, tai ekjon bhabobadi thakise aru jani thakise Isor tai logote kosom khaise, tai laga khandan pora ekjon ulabo aru uthaikene Tai laga singhason te bohai dibo.
Amma shi annabi ne ya kuma san abin da Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa zai ɗora ɗaya daga cikin zuriyarsa a kan gadon sarautarsa.
31 Aru aha dinte ki hobole ase etu sob to dikhi kene, tai Khrista mora pora jinda huwa laga kotha koise, ‘Taike Hades te bhi chari diya nai, aru Tai laga gaw bhi puchi janai.’ (Hadēs g86)
Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. (Hadēs g86)
32 Jisu ke Isor he jinda kori dise, aru amikhan sob Jisu jee-utha laga gawahi ase.
Allah ya tashe wannan Yesu zuwa rai, mu kuwa duk shaidu ne ga wannan.
33 Etu nimite Taike Isor laga dyna hathte bohai kene uthai dise aru Baba Isor pora Tai laga Pobitro Atma amikhan uporte di dise, juntu apnikhan dikhi ase aru huni bole pari ase.
An ɗaukaka shi zuwa ga hannun dama na Allah, ya karɓi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga Uba, ya kuma zubo abin da yanzu kuke gani kuke kuma ji.
34 Kelemane David to sorgote uthai loi juwa nai, kintu tai nije koise, ‘Probhu he moi laga Probhu ke koise, “Ami laga dyna hathte bohibi,
Gama Dawuda bai hau zuwa sama ba, duk da haka ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
35 Jitia tak tumi laga dushman khan ke tumi laga theng rakha jaga bonai nadiye.’”
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
36 Etu karone, Israel te jiman ghor ase etu jani lobi, Isor pora Taike Probhu aru Khrista bonai dise, etu Jisu, junke tumikhan Cross te morai dise.”
“Saboda haka bari dukan Isra’ila su tabbatar da wannan. Allah ya mai da wannan Yesu, da kuka gicciye, Ubangiji da kuma Kiristi.”
37 Jitia etu kotha hunise, taikhan monte jokhom paise, aru Peter aru ta te thaka apostle khan ke koise, “Bhai khan, amikhan ki koribo?”
Sa’ad da mutane suka ji wannan, sai suka soku a zuci sai suka ce wa Bitrus da sauran manzanni, “’Yan’uwa, me za mu yi?”
38 Titia Peter taikhan ke jowab dise, “Mon ghura bhi, moi koi ase, aru baptizma koribi, sob manu, Jisu Khrista naam pora, nijor laga paap nimite, titia tumikhan Pobitro Atma laga inam pabo.
Bitrus ya amsa, “Ku tuba a kuma yi muku baftisma, kowannenku a cikin sunan Yesu Kiristi domin gafarar zunubanku. Za ku kuwa karɓi kyautar Ruhu Mai Tsarki.
39 Kelemane etu Isor laga kosom apuni aru apuni khan laga bacha khan nimite ase, aru Probhu Isor pora junke matibo, taikhan nimite bhi ase.”
Alkawarin dominku ne da’ya’yanku da kuma dukan waɗanda suke da nesa, domin dukan waɗanda Ubangiji Allahnmu zai kira.”
40 Tai aru bisi kotha pora gawahi dikena taikhan ke samjai se, aru koise, “Nijorke biya manu khan pora bachai rakhibi.”
Da waɗansu kalmomi masu yawa ya gargaɗe su; ya kuma roƙe su cewa, “Ku ceci kanku daga wannan lalataccen zamani.”
41 Titia taikhan sob huni kene baptizma loise, aru tin hajar jon thaka biswasi khan logote aru bhi ginti kori loise.
Waɗanda suka yarda da saƙonsa kuwa aka yi musu baftisma, a ranar kuwa yawansu ya ƙaru da mutum kusan dubu uku.
42 Aru taikhan apostle khan pora ki sikhai dise etu kotha khan koi jai thakise aru ekjon-ekjon logote girja kori thakise, aru roti bhangai kene prathana te thakise.
Suka ba da kansu ga koyarwar manzanni da kuma ga zumunci, ga gutsuttsura burodin da kuma ga addu’a.
43 Aru sob logote bhoi ahi jaise, aru apostle khan dwara asurit kaam korise.
Kowa ya cika da tsoro, manzannin kuwa suka aikata abubuwan banmamaki da alamu masu yawa.
44 Aru biswasi khan logote mili kene thakise, aru sob kaam mili kene kori thakise.
Dukan masu bi suna tare, suna kuma mallakar kome tare.
45 Aru taikhan nijor dhun-sampoti aru saman sob bikiri kori kene kunke lage taikhan ke bhag kori dise.
Suka dinga sayar da ƙaddarorinsu da kayayyakinsu, suka ba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
46 Aru hodai din ekta bhabona loi kene mondoli te kaam kore, aru ekjon-ekjon logote khushi aru mon sapha pora ghor te roti bhangai kene,
Kowace rana suka ci gaba da taruwa a filin haikali. Suka gutsuttsura burodi a gidajensu suna cin abinci tare da farin ciki da zuciya ɗaya,
47 aru hodai Isor ke dhanyavad kori kene, aru sob logot pora morom paikene thakise. Aru hodai jiman Probhu logot biswas kori loi, taikhan majote ginti hoi thakise.
suna yabon Allah suna kuma samun tagomashin dukan mutane. Ubangiji kuwa ya ƙara yawansu kowace rana na waɗanda suke samun ceto.

< Acts 2 >