< Luka 8 >

1 Gakapiteje genego a Yeshu bhashinkupita mwilambo na ijiji bhalipita lunguya Ngani ja Mmbone ja Upalume gwa Nnungu. Bhaajiganywa likumi limo na bhabhili bhala gubhalongenenabhonji.
Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
2 Na kabhili bhanabhakongwe bhana bhashoshiywenje maoka na bhalamywenje ilwele na a Yeshu bhatendagalongana nabhonji. Bhene bhanganyabho pubhalinginji, a Malia Magidalena, bhashoshiywe maoka shabha,
mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
3 a Yowana akongobhabho a Kusha bhatumishi bhakulu bha nnyumba ja a Elode na a Shushana na bhananji bhowepe, bhene bhanabhakongwebho bhatendaga kwajangutilanga a Yeshu kwa mali gabhonji ashaayene.
da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
4 Likundi likulungwa lya bhandunji lyashinkwaajiila a Yeshu kukoposhela ilambo na ilambo. Nabhalabho gubhaatanjilenje aluno lutango luno.
Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
5 “Nkupanda ashinkwenda miya mmbeju yakwe. Pamiyaga pala mmbeju ina ikugwilaga mumpanda, bhapita mpanda gwaalibhetenje na ijuni gwiilile.
“Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
6 Ina gwiigwilile nnindandawe, ikameleje gwiiwile pabha pakakweteje mashi.
Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
7 Ina gwiigwilile mmibha. Mibha ila ikakuleje guitenjele.
Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
8 Na ina guigwilile palitaka lya mmbone, guimelile niogoya yaigwinji.” Bhakabheleketeje genego, gubhautiye lilobhe bhalinkuti, “Akwete makutujo apilikane!”
Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
9 Bhaajiganywa bhabho a Yeshu gubhaabhushiyenje malombolelo ga lwene lutangolo.
Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
10 Bhalabho gubhajangwile, “Mmanganya nkwetenje shikono sha kwiimanya indu ya nng'iyo ya mu Upalume gwa a Nnungu, ikabhe nngabha bhananjibho, kwa bhanganyabho pungwaabhalanjilanga kwa ndango. Nkupinga bhalolangaga bhanashibhonanje shindu na bhapilikanangaga bhanamumanyanje.”
ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
11 Bhai gegano malombolelo ga lutangolu. Mmbeju lilobhe lya a Nnungu.
To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
12 Nneyo peyo shikoposhele kwa mmbeju igwilile mumpanda shinalandana na bhandunji bhakulipilikananga lilobhe lila, kungai gwaishe ibhilishi gwalishoshiye mmitima jabhonji, bhanakulupalilanga nitapulwa.
Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
13 Nneyo peyo shikoposhele kwa mmbeju igwilile pa lindandawe, shinalandana na bhandunji, bhakupilikananga lilobhe lila bhanakuliposhelanga nikwiinonyela. Ikabheje, namalinga mmbeju ila, bhene bhandunjibho pabha bhangalinji nnjiga, bhanakulupalilanga kashokope na bhalingwangaga bhakaakabhanga kuwa ntima.
Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
14 Nneyo peyo shikoposhele kwa mmbeju igwilile mmibha shinalandana na bhandunji bhakulipilikananga lilobhe lila, ikabheje bhajabhulanganaga kashokope, bhanaakamulwanga na lipamba, na indu na mboka ya ndamo, bhalabhonji bhakaaogoyanga iepo nikomala.
Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
15 Nneyo peyo shikoposhele kwa mmbeju igwilile pa litaka lya mmbone, shinalandana na bhandunji bhakulipilikananga lilobhe lila kwa ntima gwa mmbone nikunda. Bhanganyabho bhanakwiikakatimilanga mpaka niogoya iepo.
Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
16 Bhandu bhakakoleyanga kandili nikujiunishila eu kujibhika nng'ungu. Ikabheje pabhikwa panani, nkupinga bhandu bhajinjilanga bhashibhonanje shilangaya.
Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
17 “Pabha shoshowe shishiiywe, shipinga undukulwa na yowe ili ya nng'iyo ipinga manyika kulugwinjili.
Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
18 “Kwa nneyo mwiiteiganje na inkupilikanangayo, pabha akwete shindu shajenjesheywe, ikabheje jwangali shindu, nkali shishoko shaaganishiya akwete shila, apinga pokonyolwa.”
Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
19 Penepo anyinabhabho na ashaapwabho a Yeshu gubhaikengenenje kukwaalola, ikabheje bhangakombolanga kwaabhandishila kwa ligongo lya lugwinjili lwa bhandu.
Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
20 A Yeshu gubhabhalanjilwe kuti, anyinabhenu na ashaapwenu pubhalinginji palanga, bhanapinganga kummona.
Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
21 Ikabheje a Yeshu gubhaabhalanjilenje bhandu bhowe, “Bhakulipilikanishiyanga na kulikamulila lilobhe lya a Nnungu bhanganyabho ni a mama na ashapwanga nne.”
Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
22 Lyubha limo a Yeshu na Bhaajiganywa bhabho bhashinkukwelanga mmashua, gubhaabhalanjilenje, “Tujomboshe litanda tuishe kung'ambu.” Bhai, mwanja niguutandwibhe.
Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
23 Bhalinginji mmashua, a Yeshu gubhagonile lugono. Mbungo na mabhimbili gamakulumakulu gugatabhile, mashi nigugatandwibhe kupakushila mmashua, nigubhajogopenje kaje, nibha atali.
Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
24 Bhaajiganywa bhala gubhapite kukwaajumuyanga a Yeshu, bhalinkutinji, “Mmakulungwa, Mmakulungwa, tunawa!” A Yeshu nigubhajumwishe, nigubhajikalipile mbungo na mabhimbili gala, niguitondwebhe, kwa jii.
Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
25 Penepo nigubhaabhushiyenje, “Jili kwei ngulupai jenunji?” Gubhakanganigwenje na jogopa, akuno bhalibhuyananga, “Igala bhenebha bhandu bhashi, nkali mbungo na mabhimbili bhanakwiamulisha nikwaapilikana?”
Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
26 Gubhaikengenenje kushilambo sha Bhagelashi, shilolana na ku Galilaya kung'ambu ja litanda.
Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
27 A Yeshu pubhaulukaga kumbwani, mundu jumo nshilambo jwa shene shilambo shila, akwete maoka, gwabhaishile. Kwa mobha gamagwinji jwene mundujo akawalaga nngubho wala akatamaga nnyumba, ikabhe ndamo jakwe pujaaliji mmashembo ga shishila bhandu.
Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
28 Akaabhoneje a Yeshu, gwajobhele gwaigwishiye pai mmujo jabho akuno alibheleketa kwa utiya, “Mmwe a Yeshu bhanabhabho a Nnungu bhakulu, mmwe nndi na nne? Shonde, ngunajuga nnamboteshe!”
Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
29 Ashinkubheleketa nneyo pabha a Yeshu bhammalanjile lioka jula kuti anshoshe mundu jula. Jwene lioka jwangali jwa mmbone jula akakabhaga kunkamula mundu jula, nkali bhandu bhanng'ugalilanje nnyumba nikuntabha mindondolo ja itale na pingu mmakono na mmakongono, akakabhaga kukutulanya yoweyo, na lioka jula atendaga kumminganjila kuanga.
Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
30 Bhai a Yeshu gubhammushiye, “Lina lyako gani?” Gwajangwile, “Lina lyangu, ‘Manjola’” Pabha gashinkunjinjila maoka gamagwinji.
Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
31 Ashimaoka bhala gubhaashondelesheyenje a Yeshu bhanaabhinganjilanje ku Jeanamu. (Abyssos g12)
Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos g12)
32 Penepo lyashinkupagwa likundi lya ngulubhe lilipitalya nshitumbi. Bhai ashimaoka bhala gubhaashondelesheyenje a Yeshu bhaaleshelelanje bhakaajinjilanje ashingulubhe bhala. Na bhalabho a Yeshu gubhaaleshelelenje.
Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
33 Kwa nneyo ashimaoka bhala bhakunshokanganaga mundu jula, gubhaajinjilenje ashingulubhe, gubhaelelenje nnikote shibhutuka, nititimila nnitanda.
Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
34 Bhalinda bha ngulubhe bhakagabhonanjeje gowe gakoposhele gala, gubhabhutukenje pita shumya nshilambo mula na mmigunda.
Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
35 Bhandunji gubhaikengenenje kulola gakoposhele. Gubhaajendelenje a Yeshu, gubhammweninji mundu ashoshilwe na maoka jula, atemi pa makongono ga a Yeshu, awete nngubho, ali na lunda lwakwe lwa mmbone, gubhajogopenje.
Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Bhandu bhagawenenje pugatendekaga, gubhaatalashiyenje bhananji, shaashite lamywa mundu akwete maoka jula.
Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
37 Bhashilambo bha Kugelashi gwaajogopenje kwa kaje. Kwa nneyo gubhaajujilenje a Yeshu bhashoshe. Bhai a Yeshu gubhakwelile ntumbwi gubhaijabhulile.
Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
38 Mundu ashoshiywe maoka jula, akwaashondelesheyag a Yeshu alonganenabho. Ikabheje a Yeshu gubhannajile bhalinkuti,
Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
39 “Ubhuje kumui ukatalashiye yowe ibhakutendele a Nnungu.” Bhai mundu jula gwajabhwile pita lunguya ibhantendele a Yeshu, mmbali yowe ya shilambo shila.
“Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
40 A Yeshu bhakabhujeje, gubhaposhelwe na likundi likulungwa lya bhandu, pabha bhatendaga kwaalindililanga.
Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
41 Penepo gubhaishe bhandu bhamo bhashemwaga a Yailo bhakulungwa bha shinagogi, gubhaatindibhalile a Yeshu, gubhaajujile bhajende kunngwabho,
Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
42 pabha nabhiti jwabho jwa yaka likumi limo na ibhili, numbe jwa jikape, paliji nnwele tome nawa. A Yeshu bhali nkwenda, bhandunji bhatendaga nokolananga nkwaabhandishila.
saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
43 Bhai nnikundi lya bhandu mula bhashinkupagwa bhakongwe bhamo bhalwalaga nsholosholo yaka likumi limo na ibhili, bhashinkumaliya indu yabho yowe ku bhamitela, ikabheje jwakwapi akombwele kwaalamya.
Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
44 Bhakongwe bhala gubhaakagwile a Yeshu pa nnyuma, gubhaakwashiye libhiniko lya nngubho jabho. Popo pepo gubhalamile shilwele shila.
Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
45 A Yeshu gubhabhushiye, “Gani angwashiye?” Bhowe gwaajangulenje kuti jwakwapi ankwashiye. Na a Petili gubhashite, “Mmaajiganya, lugwinjili lwa bhandu lushikunngumbalila nikuntimbilila ndendende!”
Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
46 Ikabheje a Yeshu gubhashite, “Apali mundu angwashiye, pabha njikwiipilikana mashili galinjoka.”
Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
47 Bhakongwe bhala bhakabhoneje kuti ikakomboleka kwiiya, gubhailangwiye bhalitetemela kwa jogopa, gubhaatindibhalile a Yeshu. Penepo gubhatalashiye pa bhandu bhowe shiumilo sha kwaakwaya a Yeshu na shibhashite lamywa gwanakamope.
Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
48 A Yeshu gubhaabhalanjile. “Mwanangu ngulupai jako jikulamiye. Ujende kwa ulele.”
Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
49 A Yeshu bhakanabhe maliya kubheleketa a Yailo gubhapeleshelwe ntenga kukopoka kungwabho, “Mwali jwenu awile, igala gabhuli kupunda kwaabhuya bhaajiganya?”
Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
50 A Yeshu bhakapilikaneje genego, gubhaabhalanjile a Yailo, “Mmwe nnajogope nkulupalilepe, shalame.”
Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
51 Bhakaisheje kumui bhangapinga kujinjila naka mundu juna ikabhe na a Petili na a Yowana na a Yakobho pamo na bhankwetenje mwana jula.
Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
52 Bhandu bhowe pubhalinginji nkunngutila ililo. A Yeshu gubhaabhalanjilenje, “Mpumulanje kuguta, pabha mwana jwangawa ashigonape!”
Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
53 Bhalabhonji gubhaeshilenje, pabha bhamumanyinji kuti mwana awile.
Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
54 Ikabheje a Yeshu gubhankamwile nkono, nikunshema, “Mwanangu jumuka!”
Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
55 Gumi gwakwe ukummujilaga, shangupe gwajumwishe. A Yeshu gubhaalugulilenje bhampanganje shalya.
Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
56 Bhankwetenje gubhakanganigwenje kwa kaje, ikabheje a Yeshu gubhaamulishenje bhanannugulilanje mundu jojowe gene gatendeshe gala.
Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.

< Luka 8 >