< Bhakoloshai 3 >

1 Bhai monaga nnyushiywenje pamo na a Kilishitu, mwiloleyanje indu ya kunani kubhali a Kilishitu, numbe bhashitama kunkono nnilo gwa a Nnungu.
Da yake an tashe ku tare da Kiristi, sai ku sa zukatanku a kan abubuwan da suke sama, inda Kiristi yake zaune a hannun dama na Allah.
2 Mwiganishayanje indu ya kunani, nngabha indu ya pa shilambolyo pano.
Ku sa hankulanku a kan abubuwan sama, ba kan abubuwan duniya ba.
3 Pabha mwawilenje, na gumi gwenunji ushiiywa pamo na a Kilishitu kwa a Nnungu.
Gama kun mutu, ranku yanzu kuwa yana ɓoye tare da Kiristi a cikin Allah.
4 Pushibhabhoneshe a Kilishitu bhali gumi gwetu, penepo shimmonekanje pamo na bhenebho, muukonjelo.
Sa’ad da Kiristi, wanda shi ne ranku, ya bayyana, ku ma za ku bayyana tare da shi cikin ɗaukaka.
5 Bhai, ibhalo yenunji inalame nkulokolila indu ya pashilambolyo, malinga kulabhalabha na indu ya nyata na ilokoli ya nyata na ng'aniyo yangali ya mmbone, pabha kutenda yeneyo ni malinga kutindibhalila yanamu.
Saboda haka, sai ku fid da duk wani abin da yake kawo sha’awa a zukatanku, fasikanci, ƙazanta, sha’awa, muguwar sha’awa, da kuma kwaɗayi wanda shi ma bautar gumaka ne.
6 Kwa ligongo lya genego, nnjimwa ja a Nnungu jinakwiya.
Gama fushin Allah zai sauko a kan masu aikata waɗannan.
7 Nkali mmanganyanji bhukala mwatemingenenje nndamo ja tenda yene induyo.
Dā kun yi waɗannan abubuwa, sa’ad da rayuwar tana cikin duniya mai wannan hali.
8 Ikabheje nnaino mmanganyanji nnapinjikwanga kuileka yoweyo, nnjimwa, na ilokoli, na ilebho na kulosha na matukano, ganakoposhe nkang'wa yenunji.
Amma yanzu dole ku raba kanku da dukan ire-iren abubuwan nan. Ku daina fushi, ku daina ƙiyayya da ƙeta. Ku bar ɓatan suna da kuma ƙazamar magana daga leɓunanku.
9 Nnabhalanjilananje ya unami, pabha nng'ulilenje gundu gwa bhukala na itendi yakwe yowe,
Kada ku yi wa juna ƙarya, da yake kun tuɓe tsohon halinku tare da ayyukansa
10 nng'wetenje gundu gwa ambi. Upunda alaywa ukoto nkwaalanda a Nnungu, nkupinga nkolanje lunda lwa kwaamanya bhayene bhaapanganya.
kun ɗauki sabon halin nan da ake sabuntawa ga sani, bisa ga kamannin Mahaliccinsa.
11 Penepo shakwa sha lugula kabhili kuti abha, Bhayaudi eu Bhagiliki eu ajalwishe na jwangajaluka, nngumba wala jwampenye, ntumwa wala nngwana, ikabhe a Kilishitu ni yowe, na kwa kila shindu.
A wannan sabuwar rayuwa babu bambanci ko kai mutumin Al’ummai ne ko mutumin Yahuda, mai kaciya ne ko marar kaciya, baƙo, baƙauye, bawa ne ko’yantacce, gama Kiristi shi ne kome, kuma yana cikin kome.
12 Bhai pabha nshibhanganga bhandu nng'agwilwenje na a Nnungu, bha ukonjelo nkupingwanga, ntolanje ntima gwa shiya na uguja na kwiitimalika na shinunu na kwiiluma.
Da yake Allah ya mai da ku zaɓaɓɓu, tsarkaka, ƙaunatattu, sai ku dinga jin tausayin juna, kuna yin alheri, kuna nuna tawali’u da sauƙinkai da jimrewa.
13 Nnaukumulane nneshelelananje, mundu akolaga shiumilo sha kunnugula nnjakwe, bhai mbaya anneshelele malinga Bhakulungwa shibhanneshelelenje mmanganyanji.
Ku riƙa yin haƙuri da juna kuna kuma gafarta wa juna duk wani laifin da wani ya yi muku. Ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarce ku.
14 Kupunda gene gowego, ntamangananje nkupingana, pabha kupingana kunalundanya indu yowe nibha shindu shimo sha nng'ilimila.
Fiye da waɗannan duka, ku yi ƙaunar juna, gama ƙauna ce take haɗa kome gaba ɗaya.
15 Na ulele gwa a Kilishitu gunnongoyanje mitima jenunji, pabha genego ni gunshemelwenje kubha shiilu shimo. Na mmanganje bhandunji bhatendanga eja.
Ku bar salamar Kiristi tă yi mulki a zukatanku, da yake a matsayin gaɓoɓin jiki ɗaya an kira ku ga salama. Ku zama masu godiya.
16 Malobhe ga ngani ja a Kilishitu gagumbale mmitima jenunji, akuno nnijiganyananga na leyana kwa lunda lowe, nnikwaajimbilanga a Nnungu nyimbo ya mbeembela na nyimbo ya muntima, akuno nnitendanga eja mmitima jenunji.
Ku bar maganar Kiristi ta zauna a cikinku a yalwace yayinda kuke koya, kuna kuma yi wa juna gargaɗi da dukan hikima, da kuma yayinda kuke waƙoƙin zabura, waƙoƙi da waƙoƙin ruhaniya tare da godiya a zukatanku ga Allah.
17 Shoshowe shinkukamulanga kwa lilobhe eu itendi, yowe ntendanje kwa lina lya Bhakulungwa a Yeshu, na kwaatendela eja Atati a Nnungu kwa lina lya a Yeshu.
Kuma ko mene ne kuke yi, ko cikin magana ko cikin ayyuka, ku yi shi duka a cikin sunan Ubangiji Yesu, kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.
18 Mmandonyanji mwaapilikanilanje ashimbuje bhenunji, nneyo ni shibhapinga Bhakulungwa.
Mata, ku yi biyayya ga mazanku, yadda ya dace cikin Ubangiji.
19 Mmanabhalume nnombilenje, mwaapinganje ashakongo bhenunji, nnakolanje nngomo.
Maza, ku ƙaunaci matanku kada ku nuna musu hali marar tausayi.
20 Bhana, mwaapilikanilanje bhankwetenje kwa kila shindu, pabha genego ni gubhapinga Bhakulungwa.
’Ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku cikin kome, gama wannan yakan gamshi Ubangiji.
21 Na mmanganyanji ashaaina mundu, nnaatandubhanje ashibhana bhenunji, bhanawanganga mitima.
Ubanni, kada ku matsa wa yaranku lamba, don kada su fid da zuciya.
22 Bhatumwa, mwaapilikanilanje bhakulungwa bhenunji bha pa shilambolyo pano, kwa kila shindu na nngabha kwa jimililwape nkupinga muikonjeleyanje pa meyo gabhonji, ikabheje ntendanje nneyo kwa ntima gwa mmbone, akuno nnikwaajogopanga a Nnungu.
Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya cikin kome; kada ku yi aikin ganin ido kamar masu neman yabon mutane, sai dai ku yi aiki tsakaninku da Allah, kamar masu tsoron Ubangiji.
23 Shoshowe shinkukamulanga, ntendanje kwa ntima gowe mbuti nkwaatendelanga Bhakulungwa na wala nngabha mundu.
Kome kuke yi, ku yi shi da dukan zuciyarku, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba ga mutum ba.
24 Mmumanyanje kuti shimposhelanje upo ya ulishi ibhammishilenje Bhakulungwa. Pabha nnakwaatumishilanga Bhakulungwa a Kilishitu.
Kun san cewa zai ba ku gādo a matsayin ladanku. Ubangiji Kiristi ne fa kuke bauta wa.
25 Pabha atenda yangali ya mmbone shalipwe yangali ya mmbone malinga shatendile, pabha kwa a Nnungu kwangali bhonelwa.
Duk wanda ya yi laifi, za a sāka masa don laifinsa, babu sonkai.

< Bhakoloshai 3 >