< Itendi 4 >
1 A Petili na a Yowana bhalinginji nkwaalungushiyanga bhandunji, gubhaikengenenje bhakulungwanji bha bhaabhishila na bhakulungwanji bha ulinda gwa liekalu na ashi Mashadukayo.
Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
2 Ashi Mashadukayo na bha kulungwanji bha ulinda gubhaatumbalilenje kwa kaje a Petili na a Yowana, pabha bhatendanga kwajiganyanga na kwaalungushiyanga bhandunji ga yuka kwa a Yeshu ngani jitaya kuti kupali kuyuka kwa bhawilenje.
Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
3 Bhai, gubhaakamulenje na pabha yaliji tome na pilila, gubhaabhishilenje muulinda mpaka pa malabhi gakwe.
Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
4 Ikabheje bhabhagwinji bhapilikenenje jene nganijo gubhakulupalienje, bhaakulupalila bhanabhalume gubhaishilenje tome na ishila elupu nng'ano.
Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
5 Pa malabhi gakwe, ashikalongolele bha Shiyaudi, na bhanangulungwa na bhaajiganya bha malajilo ga a Musha gubhapegwilwe na a Nnungu, gubhaimenenje ku Yelushalemu.
Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
6 Gubhaimenenje pamo na bhakulungwa bha bhaabhishila a Anashi, na a Kayapa, na a Yowana, na a Alekishanda, na bhananji bhalinginji bha ulongo bha bhakulungwa bha bhaabhishila.
Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
7 Bhakaajimikanjeje bhantenga bhala mmujo jabhonji, gubhaabhushiyenje, “Mmanganya nshitendanga yenei kwa mashili gakeni na antumilenje gani?”
Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
8 Penepo, a Petili bhali bhagumbelwe na Mbumu jwa Ukonjelo, gubhaalugulilenje, “Mmanganya ashikalongolele na bhanangulungwa bha pa Ishilaeli!
Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
9 Ibhaga lelo tubhuywanga ga shitendi sha mmbone shatendelwe mundu aaliji nangwabha jula shashite lamiywa,
In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
10 bhai, mmanganya na bhandu bhowe bha pa Ishilaeli nnapinjikwanga mmumanyanje kuti, aju munduju akunnjimilanga lelo ali alamile kwa mashili ga lina lya a Yeshu Kilishitu Bhanashaleti bhumwaakomelenje munshalabha bhala, ikabheje a Nnungu gubhaayushiye.
to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
11 Bhenebha ni bhatashiywe Mmajandiko ga Ukonjelo kuti. ‘Liganga limwalikanilenje mmanganya mmashenganga, nnaino lishibha liganga likulu lya pandumba.’
Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
12 Ntapulo ukaapatikana kuka mundu juna jojowe, pabha pashilambolyo, twangapegwa lina lika mundu juna lya kututapula.”
Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
13 Bhanangulungwa bha lukumbi bhala, akuno bhali bhamumanyinji kuti a Petili na a Yowana bhandupe bhangashomanga, gubhakanganigwenje ga kwaabhonanga bhalibheleketanga gwangali bhoga. Gubhamumanyinji kuti pubhalinginji pamo na a Yeshu.
Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
14 Ikabheje bhakammonanjeje mundu alamiywe jula ajimi nabhonji, bhangabheleketanga shindu.
Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
15 Kwa nneyo, gubhaamulishenje bhakopokanje nnukumbi mula, gubhalepekenje ashaayenenji bhalikungulukanga.
Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
16 Gubhabhuyenenje, “Twaatendanje nndi bhene bhandunjibha? Pabha kila mundu atama pa Yelushalemu pano amumanyi kuti shishitendeka shilapo na uwe tukakombola kutauka shenesho.
Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
17 Ikabheje nkupinga kuibhila shene shindushi shinapunde kushuma kubhandu, twaaleyanje bhanakungulukanje na mundu jojowe ga lina lya a Yeshu.”
Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
18 Kwa nneyo gubhaashemilenje kabhili nkati, gubhaalimbiyenje bhanakungulukanje pa lugwinjili na wala bhanaajiganyanje bhandu ga mashili ga a Yeshu.
Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
19 Ikabheje a Petili na a Yowana gubhaajangwilenje. “Nng'ukumulanje mwaashayenenji, shammbone shei, kumpilikanishiyanga mmanganya eu kwaapilikanishiya a Nnungu?
Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
20 Pabha uwe tukaleka bheleketa ga ituibhweni na ituipilikene.”
Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
21 Bhai bhanangulungwa bha lukumbi bhala gubhaakalipilenje kwa kaje, kungai gubhaaleshelelenje. Bhangaaukumulanga pabha bhandunji bhowe bhatendaga kwaakuyanga a Nnungu kwa ligongo lya gakoposhele gala.
Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22 Mundu alamiywe jula paaliji jwa yaka ya punda makumi nsheshe.
Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
23 A Petili na a Yowana shangupe bhakaleshelelwanjeje, gubhapitengenenje kwa bhaakulupalila ajabhonji, gubhaatalashiyenje yowe ibhabhalanjilwenje na bhakulungwanji bha bhaabhishila na bhanangulungwa.
Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
24 Bhalabhonji bhakapilikananjeje genego, gubhatemingenenje pamo nikwaajuga a Nnungu bhalinkutinji, “Mmakulungwa, mmwe mpengenye shilambolyo na bhaali na yowe ili nkati jakwe!
Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
25 Mmwe mwaatendile bhatumishi bhenu, ainabhetu a Daudi, bhabhelekete kwa mashili gaka Mbumu jwa Ukonjelo kuti, ‘Kwa nndi bhailambo ina bhashishimwanga? Pakuti bhandunji bhanaatendanga lukumbi?
Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
26 Bhapalume bha shilambolyo bhashikwishimilikanga, na bhatawala bhashiimana pamo nkwaakana Bhakulungwa na a Kilishitu bhabho.’
Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
27 “Pabha, kweli a Elode na a Pontio Pilato na bhandunji bha pa Ishilaeli na bhandunji bha ilambo ina bhaimenenje pannjini pano, nkwaakana a Yeshu Bhatumishi bhenu bha Ukonjelo bhumwaagwile.
Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
28 Elo, bhashinkuimananga nkupinga bhatendanje gene gumwatumbilile na panga bhukalago kwa mashili genu mmayene malinga shimwapinjile.
Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
29 Ikabheje nnaino, Mmakulungwa nnole shibhakuti kutujogoyanga. Ntushimilishe tulunguye lilobhe lyenu gwangali jogopa.
Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
30 Nngoloye nkono gwenu mwaalamyanje bhandu. Ntende ilangulo na ilapo kwa mashili ga lina lya a Yeshu Bhatumishi bhenu bha Ukonjelo.”
Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
31 Bhakamaliyanjeje kujuga Nnungu, pene pubhaimenenje pala pakutenganywaga, na bhowenji gubhagumbelwenje na Mbumu jwa Ukonjelo. Bhowe gubhapundilenje kulunguya lilobhe lya a Nnungu gwangali jogopa.
Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
32 Nkumbi gowe gwa bhaakulupalila pugwaaliji na ntima gumo na ng'aniyo yabhonji imope. Jwakwapi akwetele shindu shakwe, ikabheje bhatendaga gabhana indu yowe ibhakwetenje.
Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
33 Mitume bhatendaga kong'ondelanga kwa mashili kuyuka kwa Bhakulungwa a Yeshu, na a Nnungu gubhaapelenje mboka yaigwinji.
Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
34 Akapagwaga wala mundu jumo atubhilwaga na shindu, pabha bhakwetenje migunda eu nyumba bhatendaga ushanga
Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
35 nikwaakamuyanga mitume ela ila, nigabhanya kwa kila mundu malinga shapingaga.
su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
36 Bhashinkupagwa Bhalawi bhamo, bha ku Kipulo, lina lyabho a Yoshepu, mitume pubhaashemangaga a Bhanabha, malombolelo gakwe “Mundu ataga ntima”.
Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
37 Na bhalabho bhashinkukola nngunda, gubhaushiye, gubhatolile ela ila gubhapite kamuya kwa ashimitume.
ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.