< Romana 3 >
1 Inoñe arè ty tombo’ ty maha Jiosy; he ino ty mahasoa o savatseo?
To, mece ce ribar zama mutumin Yahuda, ko kuwa mene ne amfanin kaciya?
2 Toe jabajaba tok’aia’aia! Valoha’e, toe nafantoke am’iereo o fepèn’ Añahareo.
Akwai riba ƙwarai ta kowace hanya! Da farko dai, su ne aka danƙa wa kalmomin nan na Allah.
3 Hera tsy nahafiato ty ila’e? Hahamodo ty figahiñan’ Añahare hao ty tsy fatokisa’e?
Amma a ce waɗansu ba su da bangaskiya fa? Rashin bangaskiyarsu nan zai shafe amincin Allah?
4 Sondo’e! Ee abey te ho tendreke to t’i Andrianañahare ndra te kila mpandañitse ondatio, amy pinatetse ty hoe: Soa t’ie ho zoen-to amo tsara’oo vaho handreketse te mizaka.
Ko kaɗan! Bari Allah yă zama mai gaskiya, kowane mutum kuma yă zama maƙaryaci. Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Gama a tabbatar kana da gaskiya, sa’ad da ka yi magana, ka kuma yi nasara sa’ad da ka yi shari’a.”
5 Aa naho onjone’ ty hatsivokaran-tika ty hatòn’ Añahare, le akore ty hatao-tikañe? te tsy to hao t’i Andrianañahare t’ie mandafa? (manao reha’ ondaty rahoo).
Amma in rashin adalcinmu ya bayyana adalcin Allah a fili, me za mu ce ke nan? Za mu ce Allah ya yi rashin adalci ke nan da ya saukar da fushinsa a kanmu? (Ina magana kamar yadda mutum zai yi ne.)
6 Sondo’e ka! Naho nitò, akore ty hizakàn’ Añahare ty voatse toy?
Sam, ko kusa! Da a ce haka ne, ta yaya Allah zai shari’anta duniya?
7 Aa naho ty vandeko ro mampionjoñe ty hatòn’ Añahare ho ami’ty enge’e, le inoñe ty amàrañe ahy ho mpanan-kakeo?
Wani zai iya ce, “In a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka ƙara ɗaukaka shi, to, ta yaya zan zama mai zunubi, in ƙaryata tana kawo ɗaukaka ga Allah?”
8 Aa vaho akore t’ie tsy manao ty hoe: (Amy fanambaitambaiñañe anaiy, ie atao’ ty ila’e te enta’ay), Antao hanao raty hitotsaha’ ty soa? To ty famàrañe iareo.
In haka ne, “Ba sai mu yi ta yin mugunta don yă zama hanyar samun nagarta ba”? Kamar yadda masu baƙar magana game da mu suna cewa wai haka muke faɗa. Tabbatacce za a hukunta irin waɗannan da hukuncin da ya dace da su.
9 Akore arè? Itika hao ro soa? Aiy! fa niventean-tika aniany te songa fehèn-kakeo ke te Jiosy he te Grika.
To, me za mu ce ke nan? Mun fi su ke nan? Ina, ko kaɗan! Mun riga mun zartar cewa da Yahudawa da Al’ummai duk suna a ƙarƙarshin zunubi.
10 Fa pinatetse ty hoe: Tsy eo ty vañoñe, leo raike;
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Babu wani mai adalci, babu ko ɗaya;
11 tsy eo ty mahilala, tsy eo ty mipay an’ Andrianañahare.
babu wani mai fahimta, babu wani mai neman Allah.
12 Fonga nandifike, songa tsy manjofake; tsy ia ty manao soa, leo raike.
Duk sun kauce gaba ɗaya, sun zama marasa amfani; babu wani mai aikata nagarta, babu ko ɗaya.”
13 Kibory misokake ty tretra’ iareo; mitolom-pamañahy ty famele’ iareo; Ambane soñi’ iareo ao ty vore’ o mereñeo.
“Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗun kaburbura ne, harsunansu suna yin ƙarya.” “Dafin mugun maciji yana a leɓunansu.”
14 Lifotse fatse naho afero o falie’ iareoo.
“Bakunansu sun cike da la’ana da ɗacin rai.”
15 Malisa te hampiori-dio ty fandia’ iareo;
“Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;
16 fianto naho hasotriañe ro amo lala’ iareoo;
hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,
17 vaho alik’am’ iereo ty lalam-panintsiñañe.
ba su kuma san hanyar salama ba.”
18 Tsy aolom-pihaino’ iareo ty fañeveñañe aman’ Añahare.
“Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19 Fohintika te ze tsarae’ i Hake ro tsarae’e amy ze ambane’ Hake, hampihomboñe ze kila falie, vaho fonga hampivolilieñe aman’ Añahare ty voatse toy;
Yanzu mun san cewa dukan abin da doka ta ce, tana magana ne ga waɗanda suke ƙarƙarshin doka, saboda a rufe kowane baki; dukan duniya kuma ta ba da lissafin kanta a gaban Allah.
20 fa tsy ama’ nofotse veloñe ty hahazo to ampivazohoa’e ami’ty fimanemanea’e Hake; amy te fampandrendrehan-kakeo ty Hake.
Saboda haka babu wanda Allah zai ce da shi mai adalci ta wurin kiyaye doka kawai; a maimako, ta wurin doka ne muke sane da zunubi.
21 Ie henaneo, fa nadodea alafe’ i Hake ty havantañan’ Añahare, ie taroñe’ ty Hake naho o Mpitokio
Amma yanzu an bayyana wani adalci daga Allah, wannan adalcin bai danganta ga doka ba, Doka da Annabawa suna ba da shaida game da wannan adalci.
22 naho boak’ aman’ Añahare añamy figahiña’ Iesoà Norizañey ty havantañañe, ho amo hene mitam-patokisañeo, le tsy iambakambàhañe;
Wannan adalcin Allah yana zuwa ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi ga dukan waɗanda suka ba da gaskiya ne. Ba bambanci,
23 toe fonga nanao hakeo naho milesa ami’ty engen’ Añahare,
gama duka sun yi zunubi suka kuma kāsa ga ɗaukakar Allah,
24 f’ie nampivantañeñe tsi-ambili’e amy fatariha’e añamy fijebañañe amy Iesoà Norizañeiy,
an kuma kuɓutar da su kyauta ta wurin alherinsa bisa ga aikin fansar da ya zo ta wurin Yesu Kiristi.
25 i sinafirin’ Añahare ho takom-boiñe añamy fiatoañe an-dio’ey, hampiboake ty havantaña’e, fa am-pahaliñisa’e ty nirirañen’ Añahare o hakeo taoloo,
Allah ya miƙa Yesu Kiristi a matsayin hadayar kafara, ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya yi haka domin yă nuna adalcinsa, domin a cikin haƙurinsa bai hukunta zunuban da aka aikata a dā ba
26 hampidodeà’e amo sa zao ty havantaña’e, t’ie i Vantañey naho ty figahiña’ Iesoà ro fañavantañañe ondaty.
ya yi haka domin yă nuna adalcinsa a wannan lokaci, saboda yă zama mai adalci da mai kuɓutar da waɗanda suke ba da gaskiya a cikin Yesu.
27 Aia arè ty firengeañe? Napoke añe. Ami’ty Hake manao akore? He am-pimanemaneañe? Aiy avao, fa amy Hake miato-patokisañey.
To, me za mu yi taƙama a kai? Babu wani abin da zamu yi taƙama a kai. A kan wace ƙa’ida ce za mu yi taƙama? Ta hanyar bin doka ne? A’a, sai dai ta wurin bangaskiya.
28 Aa le agadon-tika te vantañe’ i fatokisa’ey t’indaty fa tsy am-pimanemanea’e Hake.
Gama mun tsaya a kan cewa ta wurin bangaskiya ne ake kuɓutar da mutum, ba ta wurin kiyaye doka ba.
29 Aa vaho Andrianañahare’ o Jiosio avao hao re? Tsy a’ o fokontokoñeo ka hao? Eka, toe a o fokontokoñeo ka.
Allah ɗin, Allahn Yahudawa ne kaɗai? Shi ba Allahn Al’ummai ba ne? I, shi Allahn Al’ummai ne ma,
30 Inao, Raike t’i Andrianañahare, le fatokisañe ty añavantaña’e o sinavatseo naho fatokisañe ka o tsy sinavatseo.
da yake Allah ɗaya ne kaɗai, shi kuma zai kuɓutar da masu kaciya bisa ga bangaskiya da kuma marasa kaciya ta wurin wannan bangaskiya ɗin.
31 Hera faohen-tika am-patokisañe t’i Hake. Aiy, sondo’e! te mone ajadon-tikañe t’i Hake.
To, za mu soke dokar saboda wannan bangaskiyar ne? Ko kaɗan! A maimako, sai ma tabbatar da ita muke yi.