< Salamo 3 >

1 Ry Iehovà, Akore ty fitomboa’ o mpamorefore ahikoo! Maro ty miongake hiatreatre ahy.
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 Lako ty manao ty hoe ty amako: Tsy ama’e ty fandrombahan’ Añahare. Selà
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 Fa Ihe, ry Iehovà, ro kalan-defo mañohoñ’ ahy, ty engeko naho ty Mpampiandra ty lohako.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 Ie koiheko am-peo t’Iehovà, le janjiñe’e amy vohi’e miavakey. Selà
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 Màndre iraho vaho miroro; tsekake amy te mpañimba ahy t’Iehovà.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 Tsy hembañako i lahiale miarikoboñe hiatreatre ahikoy.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 Miongaha, ry Iehovà! Rombaho iraho ry Andrianañahareko, fa fonga tinampifi’o ty valañorà’ o rafelahikoo; vaho pinekapeka’o ty nife’ o lo-tserekeo.
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Am’ Iehovà ty fandrombahañe; naho am’ondati’oo ty fitahia’o. Selà
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)

< Salamo 3 >