< Filipiana 2 >
1 Aa naho eo ty fañosihañe amy Norizañey, ke eo ty fañohòañe an-koko, ke eo ty fitraofan-kina amy Arofoy, he eo ty halèm-po naho fiferenaiñañe,
In kuna da wata ƙarfafawa daga tarayya da Kiristi, in da wata ta’aziyya daga ƙaunarsa, in da wani zumunci da Ruhu, in da juyayi da tausayi,
2 le henefo’ ty haehako am-piharoan-drehake naho am-pikokoañe raike vaho mifampipiteha arofo naho fivetsevetse.
to, sai ku sa farin cikina yă zama cikakke ta wurin kasance da hali ɗaya, kuna ƙauna ɗaya, kuna zama ɗaya cikin ruhu da kuma manufa.
3 Ko manao inoñe am-patitiañe naho firengeañe kòake, fe mifampiasia an-trentram-po;
Kada ku yi kome da sonkai ko girman kai, sai dai cikin tawali’u, ku ɗauki waɗansu sun fi ku.
4 Ko sindre mañambeñe o azeo avao, fe ampiraoraò ondatio.
Bai kamata kowannenku yă kula da sha’anin kansa kawai ba, sai dai yă kula da sha’anin waɗansu ma.
5 Itsakoreo an-troke ao i tam’ Iesoà Norizañeiy, te
A cikin dangantakarku da juna, ya kamata halayenku su zama kamar na Kiristi Yesu.
6 Ie nihambam-bintañ’ aman’ Añahare, tsy naereñere’e te hitavane ty fihambañañe aman’ Añahare,
Wanda, ko da yake cikin ainihin surar Allah yake, bai mai da daidaitakansa nan da Allah wani abin riƙewa kam-kam ba,
7 fe finao’e ty fañòva’e, le nandrambe ty vinta' ondaty, vaho nampihambañeñe ami'ty mpitoroñe.
amma ya mai da kansa ba kome ba, yana ɗaukan ainihin surar bawa, aka yi shi cikin siffar mutum.
8 Ie tendreke te hambam-bintañe ama’ ondaty, le nirè-batañe, nivohotse an-kavilasy— eka navetrake amy hatae ajaley!
Aka kuma same shi a kamannin mutum, ya ƙasƙantar da kansa ya kuma zama mai biyayya wadda ta kai shi har mutuwa, mutuwar ma ta gicciye!
9 Toly ndra nonjonen’ Añahare, vaho tinolo’e ty tahinañe ambone’ ze kila añarañe,
Saboda haka Allah ya ɗaukaka shi zuwa mafificin wuri ya kuma ba shi sunan da ya fi dukan sunaye,
10 soa te hitongaleke amy Iesoà ze kila ongotse an-dikerañe añe naho an-tane atoy vaho ambane’ tane ao,
don a sunan Yesu kowace gwiwa za tă durƙusa, a sama da a ƙasa da kuma a ƙarƙashin ƙasa,
11 vaho hiantoke te Iesoà Norizañe ro Talè ze hene fameleke handrenge an’Andrianañahare Rae.
kowane harshe kuma yă furta cewa Yesu Kiristi Ubangiji ne, don ɗaukakar Allah Uba.
12 Ie amy zao, ry rañetseo, ie mivohotse nainai’e, tsy ami’ty fiatrefako avao, fa àntsake henane te tsy eo, le mifanehafa ami’ty fandrombahañe anahareo, am-pañeveñañe naho fineveneverañe;
Saboda haka, ya abokaina ƙaunatattu, kamar yadda kullum kuke biyayya ba kawai sa’ad da ina nan ba, amma yanzu da ba na nan tare da ku, ku ci gaba da yin ayyukan cetonku da tsoro da kuma rawan jiki,
13 toe mitoloñe ama’ areo t’i Andrianañahare hilozoha’areo toloñe amy ze satri’e soa.
gama Allah ne yake aiki a cikinku, don ku nufa ku kuma aikata bisa ga nufinsa mai kyau.
14 Hene ano, tsy miñeoñeoñe tsy mandietse,
Ku yi kome ba tare da gunaguni ko gardama ba,
15 soa tsy hanan-kakeo, tsy hanan-tahiñe, fa ho anan’ Añahare tsy aman-kandra añivo’ ty tariratse mengoke naho miola toy, mipelatse hoe failo ami’ty voatse toy,
don ku zama marasa abin zargi, sahihai’ya’yan Allah, waɗanda ba su da laifi, a zamanin mutane karkatattu, kangararru, waɗanda kuke haskakawa a cikinsu kamar fitilu a duniya
16 mivontititse amy tsaran-kaveloñey, hampirebeke ahy an-tsa’ i Norizañey t’ie tsy nilay tsi-vente’e vaho tsy nilesa te nifanehake.
kuna kuwa cin gaba da riƙe maganar rai domin in yi taƙama a ranar Kiristi cewa ban yi gudu ko fama a banza ba.
17 Eka, ndra t’ie ampidoañeñe hoe ènga-rano ami’ty fisoroñañe naho fitoloñañe amo fatokisa’ areoo, le mbe mifale naho mitrao-pirebeke ama’ areo iaby.
Amma ko da ana tsiyaye jinina kamar hadaya ta sha a kan hadaya da kuma hidimar da take fitowa daga bangaskiyarku, ina murna ina kuma farin ciki da ku duka.
18 Aa le mifalea ka vaho miharoa firebeke amako.
Haka ma ya kamata ku yi murna ku kuma yi farin ciki tare da ni.
19 Misalala am’ Iesoà Talè ao iraho, te hampihitrifeñe mb’ama’ areo mb’eo aniany t’i Timoty, hampanitsiñe ahy t’ie mitsanoñe ty ama’areo.
Ina sa rai a cikin Ubangiji Yesu cewa zan aika da Timoti zuwa gare ku ba da daɗewa ba, don ni ma in ji daɗi sa’ad da na ji labarinku.
20 Fa tsy amako ty mañirinkiriñe aze ami’ty fahimbaña’e miatrake anahareo,
Ba ni da wani kamar sa, wanda yake da ainihin sha’awa a zaman lafiyarku.
21 toe mipay ty aze avao i maroy, fa tsy ty a’ Iesoà Norizañey.
Gama kowa yana lura da al’amuran kansa ne kawai, ba na Kiristi Yesu ba.
22 Fohi’ areo ty namentea’e vatañe, ie hoe anake aman-drae’e te nitraoke amako amy fitoroñañe i talili-soaiy.
Amma, ai, kun san darajar Timoti yadda muka yi bautar bishara tare, kamar ɗa da mahaifinsa.
23 Aa le salalaeko ty hañitrike aze aniany naho fa fantako ty amako.
Saboda haka, ina sa rai, in aike shi da zarar na ga yadda abubuwa suke a nan.
24 Le iantofako amy Talè te homb’eo aniany ka iraho.
Ni kuma ina da tabbaci a cikin Ubangiji cewa zan zo ba da daɗewa ba.
25 Toe sinafiriko ty hampihitrike i Epafrodito rahalahiko mb’ama’ areo mb’eo, mpifanehake naho lahindefo mpiamako, ie toe ìra’ areo naho mpiatrak’ ahiko,
Amma ina gani ya dace in aika da Afaforiditus, ɗan’uwana, abokin aikina da kuma abokin famana, wanda kuma yake ɗan saƙonku, wanda kuka aika domin yă biya mini bukatuna.
26 ie nijagobo ty ama’areo, naho nalovilovy te jinanji’ areo ty amy fatindri’ey.
Gama yana marmarin ganinku duka ya kuma damu domin kun ji cewa ya yi rashin lafiya.
27 Toe niheta’e re ho nivetrake, fe niferenaiñan’ Añahare, le tsy ie avao fa izaho, hera ho nanahelo an-kontoke.
Ba shakka ya yi rashin lafiya, har ya kusa mutuwa. Amma Allah ya nuna masa jinƙai, ba shi kaɗai ba amma har da ni ma, don yă rage mini baƙin ciki kan baƙin ciki.
28 Aa le nihavoa iraho te nampolieñe ama’areo, soa t’ie isa’ areo indraike ro handia taroba, vaho hampanintsiñe ahy ka.
Saboda haka na yi niyya ƙwarai in aike shi wurinku, don sa’ad da kuka sāke ganinsa za ku yi murna, ni kuma in rage damuwa.
29 Aa le rambeso amy Talè an-kaehake vaho onjono ondaty hoe zaio;
Ku marabce shi cikin Ubangiji da farin ciki mai yawa, ku kuma girmama mutane irinsa,
30 amy te ho nametrake aze i fitoloña’e amy Norizañeiy, ie namoy-ay hañeneke i tsy nilefe’ areo amy fiatrahañe ahikoy.
domin ya kusa yă mutu saboda aikin Kiristi, ya yi kasai da ransa don yă cikasa taimakon da ba ku iya yi mini ba.