< Nomery 28 >

1 Hoe ty nitsara’ Iehovà amy Mosè:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Lilio o Ana’ Israeleo naho ano ty hoe: Ambeno’ areo amy andro famantañañ’ azey ty hañengàñe amako i hanekoy, i soroñañe amako ho hàñin-kanintsiñe amakoy.
“Ka umarci Isra’ilawa cewa, ‘Ku tabbatar kun miƙa mini hadaya ta abinci ta wuta mai daɗin ƙanshi a gare ni, a daidai lokaci.’
3 Le ano ty hoe iereo: Zao ty hisoroñañe am’ Iehovà andro am-pohatse ho lilim-pisoroñañe: vik’ añondrilahy roe tsy aman-kandra.
Ka gaya musu, ‘Ga hadaya ta ƙonawa ta kowace rana, da za ku miƙa wa Ubangiji, raguna biyu, bana ɗaya-ɗaya, marasa lahani.
4 Hengae’o maraindray ty vik’ añondry vaho hengae’o folakandro ty faharoe,
A miƙa rago ɗaya da safe, ɗaya kuma da yamma,
5 reketse mona fahafolo’ ty efà linaro mena-piniritse fahèfa’ ty hine ho enga-mahakama.
tare da hadaya ta lallausan gari kashi ɗaya bisa goma na efan, kwaɓaɓɓe da kwalaba ɗaya na man zaitun mafi kyau.
6 Ie lilim-pisoroñañe norizañe ambohi-Sinay añe ho hàñin-kanintsiñe, fisoroñañe am’ Iehovà.
Wannan ita ce hadaya ta ƙonawa ta kullum wadda aka kafa a Dutsen Sinai, don daɗin ƙanshi, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
7 Le songa añengañe enga-rano fahèfa’ ty hine i añondry roe rey; ailiñe am’ Iehovà amy toe-miavakey i divay soay ho enga-rano.
Hadaya ta sha, za tă zama kwalaba ɗaya na ruwan inabi, da ɗan rago guda. Za a kwarara hadaya ta sha ga Ubangiji a wuri mai tsarki.
8 Engae’o ami’ ty folakandro i vik’ añondry ila’ey rekets’ i enga-maha­kama’ey naho i enga-rano’ey, hambañe amy nañengañe amy maraiñeiy ty hañenga’o aze: soroñe ho hàñin-kanintsiñe am’ Iehovà.
Ɗayan ɗan ragon kuma za a miƙa shi da yamma, tare irin hadaya ta lallausan gari, da hadaya ta sha da ka yi da safe. Wannan hadaya ce ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
9 Ie ami’ty andro Sabotse, le vik’ añondrilahy roe tsy aman-kandra, naho mona fahafolo’ ty efa roe ho enga-mahakama, linaro menake naho i enga-rano’ey:
“‘A ranar Asabbaci, za a miƙa’yan raguna biyu, bana ɗaya-ɗaya marasa lahani, tare da hadaya ta sha, da hadaya ta lallausan gari kashi biyu bisa goma na efa, kwaɓaɓɓe da mai.
10 zay ty hisoroñañe boa-tSabata ambone’ i enga hisoroñañe boak’ àndroy rekets’ i enga-rano’ey.
Wannan ita ce hadaya ta ƙonawa ta kowace Asabbaci, ban da hadaya ta ƙonawa ta kullum, tare da ta hadaya ta sha.
11 Mañengà soroñe am’ Iehovà amo jiri-bola’ areoo: bania roe, añon­drilahy raike, vik’ añondrilahy fito tsy aman-kandra;
“‘A rana ta fari ga kowane wata, za a miƙa wa Ubangiji hadayun’yan bijimai biyu, rago ɗaya, da’yan tumaki bakwai, bana ɗaya-ɗaya, dukansu kuma marasa lahani.
12 naho songa mona fahafolo’ ty efà telo linaro menake ty bania; naho fahafolo’ ty efà roe linaro menake ho enga-mahakama, i añondri­lahiy;
Da kowane bijimi, a kasance da hadaya ta lallausan garin da aka kwaɓa da mai na kashi uku bisa goma na efa; da ɗan rago kuwa, a kasance da hadaya ta lallausan garin da aka kwaɓa da mai na kashi biyu bisa goma na efa;
13 le sindre mona fahafolo’ ty efà linaro menake ho enga-mahakama ty vik’ añondry, enga olorañe, hàñin-kanintsiñe, soroñañe am’ Iehovà.
da kowane tunkiya kuma, a kasance da hadaya ta lallausan garin da aka kwaɓa da mai, na kashi ɗaya bisa goma na efa. Wannan hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
14 songa ho divay vaki’ ty hine ty bania, sindre fahatelo’ ty hine i añondrilahiy vaho fonga fah’efa’ ty hine ty vik’ añondry. Izay ty hisoroñañe an-jiri-bola’ ze hene volañe amo taoñeo.
Da kowane bijimi, za a kasance da hadaya ta sha, na rabin kwalabar ruwan inabi; da rago kuwa, a kasance da kashi ɗaya bisa uku; da kowace tunkiya kuma, a kasance da kashi ɗaya bisa huɗu. Wannan ita ce hadaya ta ƙonawa don tsayawar kowane sabon wata na shekara.
15 Le forototò ho engan-kakeo am’ Iehovà ty oselahy; ho tovo’ i soroñe boak’ andro rekets’ i enga-rano’eiy.
Ban da hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadaya ta sha, za a miƙa bunsuru ɗaya ga Ubangiji, hadaya ce don zunubi.
16 Ami’ty andro faha-folo-efats’ambi’ i volam-baloha’ey ty Pèsa’ Iehovà.
“‘Za a yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a rana ta goma sha huɗu ga wata na fari.
17 Le hanoeñe sabadidake amy andro faha folo-lime-ambi’ i volañeiy; ho kamaeñe fito andro ty mofo po-dalivay.
A rana ta goma sha biyar ga wannan wata, za a yi biki; kwana bakwai za a ci burodi marar yisti.
18 Hanao fañohara-miavake nahareo amy andro valoha’ey; tsy itolonan-draha.
A rana ta farko, za ku yi tsattsarkan taro, ba kuwa za a yi aikin da aka saba yi na kullum ba.
19 Le mibanabanà enga hisoroñañe am’ Iehovà: bania roe, ty añondrilahy, naho ty vik’ añondrilahy fito, asoao te tsy aman-kandra.
Za a miƙa hadaya ta ƙonawa da bijimai biyu, rago ɗaya, da’yan raguna bakwai, bana ɗaya-ɗaya; dukansu kuma marasa lahani ga Ubangiji.
20 Mona linaro menake ty enga-maha­kama’ iareo, songa fahafolo’ ty efà telo ty bania, naho fahafolo’ ty efà roe i añondrilahiy;
Da kowane bijimi, a shirya kashi ɗaya bisa uku na efan lallausan gari, kwaɓaɓɓe da mai; da rago guda kuwa, a shirya kashi biyu bisa goma na efan lallausan gari, kwaɓaɓɓe da mai;
21 le sindre fahafolo’ ty efà ty vik’ añondry, ho a i vi’e fito rey;
da kowane’yan raguna bakwai, kashi ɗaya bisa goma.
22 vaho oselahy ty ho engan-kakeo hijebañañe anahareo.
A haɗa da bunsuru guda, a matsayin hadaya don zunubi, don yin muku kafara.
23 Halankañe’ areo ho tovo’ i enga marain­draiñey, i enga boak’ androy.
Ku shirya wannan tare da hadaya ta ƙonawa ta kowace safiya.
24 Izay ty fañengañe boak’ andro, fito andro, ty mahakama’ i enga fisoroñañey, hàñin-kanintsiñe am’Iehovà, engaeñe ho tovo’ i enga boak’ àndroy naho i enga-rano’ey.
Ta haka za a shirya abinci don hadayar da aka yi da wuta, kowace rana, har kwana bakwai don daɗin ƙanshi ga Ubangiji; a shirya shi haɗe da hadaya ta ƙonawa ta kullum, da kuma hadaya ta sha.
25 le hanao fañohara-miavake nahareo ami’ty andro fahafito. Tsy itoloñan-draha.
A rana ta bakwai, za ku yi tsattsarkan taro, amma ba za a yi aikin da aka saba yi kullum ba.
26 Ie amy andron-dengom-boay, le mibanabanà enga-mahakama vao am’ Iehovà amy sabadida-kereñandro’ areoy, le ano fañohara-miavake vaho ko mitolon-draha.
“‘A ranar nunan fari, sa’ad da za ku miƙa wa Ubangiji hadayar sabon hatsi, a lokacin Bikin Makoni, za a yi tsattsarkan taro, ba kuwa za a yi aikin da aka saba yi ba.
27 Mibanabanà enga hisoroñañe ho hàñin-kanintsiñe am’ Iehovà: bania roe, ty añondri­lahy raike vaho ty vik’añondrilahy fito,
A miƙa hadaya ta ƙonawa da’yan bijimai biyu, rago ɗaya da’yan raguna bakwai, bana ɗaya-ɗaya don daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
28 mitraok’ ami’ty mona linaro menake ho enga-mahakama’e: songa fahafolo’ ty efà telo ty bania, naho fahafolo’ ty efà roe i añondrilahiy
Da kowane bijimi a kasance da hadaya ta lallausan gari kashi uku bisa goma na efa, kwaɓaɓɓe da mai; da rago kuwa, a kasance da hadaya ta lallausan gari kashi biyu bisa goma na efa, kwaɓaɓɓe da mai;
29 sindre fahafolo’ ty efà ty vik’ añondry ho amy vi’e fito rey;
da kowane’yan raguna bakwai, kashi ɗaya bisa goma.
30 vaho ty vik’ oselahy hijebañañe anahareo.
A haɗa da bunsuru guda don yin muku kafara.
31 Hengae’ areo ho tovo’ i soroñañe nainai’ey rezay, naho o enga mahakama’e naho enga-rano’e. Asoao t’ie tsy ho aman-kandra.
A miƙa waɗannan tare da hadayarsu ta sha, haɗe da hadaya ta ƙonawa ta kullum, da kuma hadayarta ta sha. A tabbata dabbobin nan marasa lahani ne.

< Nomery 28 >