< Nomery 13 >

1 Hoe ty nitsara’ Iehovà amy Mosè,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Añiraho ondaty hitingañe an-tane Kanàne añe, ie hatoloko amo ana’ Israeleo, songa amantoho ondaty raike o fifoko­an-droae’eo, fonga mpamelek’ am’ iereo.
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 Aa le nampionjone’ i Mosè boak’ am-patrambei’ i Parane ao iereo ami’ ty nandilia’ Iehovà, songa mpiaolo’ o ana’ Israeleo indaty rey.
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 Aa le zao o tahina’ iareoo: tam-pifokoa’ i Reòbene, t’i Samoà ana’ i Zakore;
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 tam-pifokoa’ i Simone t’i Safate ana’ i Horý;
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 tam-pifokoa’ Iehodà t’i Kalebe ana’ Iefonè;
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 tam-pifokoa’ Isakhare t’Igale ana’ Iosefe;
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 tam-pifokoa’i Efraime t’i Hoseà ana’ i None;
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 tam-pifokoa’ i Beniamène t’i Paltý ana’i Rafò;
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 tam-pifokoa’ i Zebolone t’i Gadiele ana’i Sodý;
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 tam-pifokoa’ Iosefe, tam-pifokoa’ i Menasè: t’i Gadý ana’ i Sosý;
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 tam-pifokoa’ i Dane, t’i Amiele ana’ i Gemalý;
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 tam-pifokoa’ i Asere t’i Setore ana’ i Mikhaele;
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 tam-pifokoa’ i Naftalý t’i Nakhbý ana’ i Vofsý;
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 tam-pifokoa’i Gade, t’i Geoele ana’ i Makhý;
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 Ie ro tahina’ ondaty nafanto’ i Mosè hitingañe i taneio, le novae’ i Mosè ty tahina’ i Hoseà ho Iehosòa.
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 Aa le nirahe’ i Mosè iereo hitin­gañe an-tane Kanàne añe naho nafanto’e ty hoe: Mionjona mb’ amo Negeveo mb’eo vaho mañambonea mb’ am-bohibohitse añe,
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 le isaho te inoñe i taney naho ondaty mimo­neñe aoo ke maozatse ke maifoifo, he tsy ampeampe he maro;
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 le i tane imoneña’ iareoy, ke soa he raty; naho o rova itoboha’ iareoo ke t’ie tobe he arikoboñen-kijoly;
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 le i taney ke kobokara he tsy mamokatse; ke mitiry hatae he tsie. Aa le mahasibeha vaho añandeso ty voka’ i taney. Toe san-doha-voam-balòboke henane zay.
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 Aa le nienga iereo nijoko boak’ am-patrambei’ i Tsine mb’e Rekhobe am-pimoaha’ i Hamate mb’eo.
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 Le nion­joñe mañatimo naho nigodam-b’e Kebrone naho Akimane naho e Sesaý vaho e Talmaý, mb’amo ana’ i Anàkeo mb’eo. (Naoreñe fito taoñe taolo’ i Tsoane e Mitsraime añe ty Kebrone.)
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 Le nivotrak’ am-bavatane’ Eskole eo iereo vaho nibira tsampam-baloboke rekets’ angaroza’e raike nampitarazoeñe ondaty roe am-baoñe, naho nangalak’ ampongabeindañitse vaho aviavy.
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 Natao Vavatane’ i Eskole i taney amy angaroza nihitsife’ o ana’ Israeleoy.
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 Ie efa-polo andro añe le nimpoly i nitampoñe i taney rey,
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 le niheo mb’amy Mosè naho i Aharone vaho i valobohò’ Israeley am-patram-bei’ i Parane e Kadese mb’eo ninday saontsy ama’e naho amy valobohò’ Israele iabiy, vaho naboa’ iereo ty voka’ i taney.
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 Le hoe ty natalili’ iareo ama’e, Nigodañe’ay i tane’ nañiraha’o anaiy. Toe iorikorihan-dronono naho tantele, hehe ty voka’e.
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 Fe misañatse ondaty mimo­neñe amo taneo; le fahe­ran-kijoly fatratse o rova’eo vaho jaba­jaba; mbore nioni’ay ao o ana’ i Anàkeo.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 Mimo­neñe an-tane atimo ao o nte-Amalekeo; le mimoneñe am-bohibohitse ao o nte-Kheteo naho o nte-Ie­bosèo vaho o nte-Amareo; le mimo­neñe añ’ olo’ i riakey naho añ’ olo’ i saka Iardeney o nte-Kanàneo.
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 Nampianjiñe’ i Kalebe añatrefa’ i Mosè ondatio, nanao ty hoe: Antao hionjoñe mb’eo amy zao hitavañe i taney, tsy kalafo te mahagiok’ aze tika.
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 Fe nanao ty hoe ondaty niharo-lia ama’eo: Tsy lefen-tika ty hionjoñe haname ondatio amy t’ie maozatse te aman-tika.
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 Le naboele’ iereo ty talily nahatsonevotse o ana’ Israeleo amy tane nitingane’ iereoy, ami’ty hoe: I tane niranga’ay mpitingañey, le tane mampibotseke o mpimone’eo, vaho mijoalajoala ze hene ondaty niisa’ay ama’e.
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 Nioni’ay ondaty joakeo (toe tarira’ ondaty joake o nte-Anàkeo); le nihoe valala am-pañentea’ay zahay vaho zahay am-pahaisaha’ iareo.
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

< Nomery 13 >