< Marka 14 >

1 Ie henane zay, roe andro taolo’ i Fihelañey naho i Sabadidake-Mofo-po-Dalivaiy, le nipay ty hitsepake Iesoà am-pamañahiañe o mpisorom-beio naho o mpanoki-dilio hañoho-doza ama’e.
Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi.
2 Fe hoe iereo: Tsy amy sabadidakey, kera hikoràke i màroy.
Suna cewa amma “Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane”.
3 Ie te Betania añ’anjomba’ i Simona angamae ao, nidegañe am-pandambaña eo, le niheo mb’ama’e mb’eo ty rakemba ninday rame saro-bily am-pitavonañe sinihara; nipoñafe’e i fitavonañey vaho nadoa’e añambone’e eo.
Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa.
4 Fe hoe ty nifamondromondroa’ ty ila’e: Akore ty fiànton-drano-mañitse toy?
wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa
5 Ie mete ho naletake denaria telon-jato vaho natolotse amo rarakeo. Le nendaha’ iareo i ampelay.
“Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?
6 Aa hoe t’Iesoà tama’e: Adono, inoñe ty anirika’ areo aze? Ie nañasoa ahy.
Sai Yesu yace masu “Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata,
7 Fa mitraoke ama’ areo nainai’e o rarakeo vaho mete hasoàñe ndra mbia mbia tea’ areo, fe tsy ho nainai’e ama’ areo iraho.
ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba.
8 Nanoe’e ze taka’e; nihosora’e aolo’ i leveñey ty sandriko.
Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza.
9 Eka! to t’itaroñako te ndra aia aia an-tane atoy ro italili­añe ty talili-soa toy, le ho talilieñe ka i nanoe’ i rakembaiy ho fitiahiañe aze.
hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba.”
10 Niavotse mb’amo mpisorom-beio mb’eo amy zao t’i Jodasy, mpiamy folo ro’amby rey, hamotera’e aze.
Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu,
11 Niehake iereo te nahajanjiñe, naho nampitamae’ iareo drala. Aa le namototse nipay ty hamotera’e aze re.
Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.
12 Ie ami’ty andro valoha’ i Mofo-po-dalivaiy, ie nisoroña’ o mpiama’eo i Fihelañey le hoe ty ontane’ iareo ama’e: Aia ty tea’o handenà’ay hañalankañe ty hikama’o i Fihelañey?
A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa “Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa?
13 Aa le nirahe’e ty roe amo mpiama’eo ami’ty hoe: Miziliha an-drova ao, le hifanampea’ ty lahilahy milolohe sihoan-drano: oriho.
Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa “Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa.
14 Le ndra aia’ aia imoaha’ey, misaontsia amy tompon’ anjombay, ty hoe: Hoe t’i Talè: Aia ty trañon’ ambahiny hitraofako fikama i Fihelañey amo mpiamakoo?
Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace “ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?”'
15 Le hitoroa’e traño bey reke-bara nihajarieñe, le fa veka’e am-batsa ao, halankaño ao ty antika.
Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can.”
16 Aa le niavotse o mpiama’eo, nimb’an-drova mb’eo, le nizoe’ iereo hambañe amy nitalilia’ey, vaho hinajari’ iareo i Fihelañey.
Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.
17 Ie hariva le nizilike ao mindre amy folo ro’amby rey.
Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun.
18 Aa ie nidegañe eo nikama, le hoe t’Iesoà: Eka! to t’itaroñako te hifotetse ahy ty raike ama’ areo, ty mitrao-pikama amako.
Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce “Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni”.
19 Le nangoae iereo nifandimbe nanao ty hoe ama’e: Izaho hao? naho ty raike: Izaho hao?
Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa “Hakika bani bane ko?”
20 Tinoi’e ty hoe: Raike amy folo ro’ ambiy. I miharo mandò am-pingakoy.
Yesu ya amsa masu da cewa “Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar”.
21 Toe hienga amy pinatetse ty ama’ey i Ana’ Ondatiy; fe hankàñe ami’t’indaty mifotetse amy Ana’ Ondatiy! Hàmake te tsy nasamake indatiy!
Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! “zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba”.
22 Naho nikama iereo le nandrambe mofo re naho nitatae’e, naho nifolahe’e vaho nazotso’e ami’ty hoe: Intoy, sandriko toy.
Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa “Wannan jikinana ne”.
23 Ie nandrambe i fitoviy le nañandriañe naho nazotso’e vaho songa nikama ama’e,
Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon.
24 vaho nanoa’e ty hoe: Intoy ty lioko amy fañinay, ze adobañe ho ami’ty maro.
Ya ce “Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane”.
25 Eka! to t’itaroñako te, tsy hinoñe ty voka’ o vaheo ka iraho ampara’ ty andro hinomako aze vao am-Pifehean’ Añahare ao.
Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah.”
26 Ie nitakasy sabo raike le niavotse mb’am-bohits’ Oliva mb’eo.
Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun.
27 Hoe t’Iesoà tam’iereo: Hene hi­tsi­kapy nahareo te hariva; hoe ty pinatetse: Ho zevoñeko ty mpiarake, le hivarakaike o añondrio.
Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa “Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;
28 Izaho fa nivañon-ko veloñe, le hiaoloako nahareo mb’e Galilia añe.
Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili.
29 Hoe t’i Petera tama’e: Ndra te fonga hitsikapy, tsy izaho!
Bitrus ya ce masa “ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni”.
30 Le hoe t’Iesoà tama’e: Eka! to t’itaroñako, t’ie anito haleñe, aolo’ i kekeon’ akoholahy faha-roey, ro hitety ahy in-telo.
Yesu yace masa “Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku”.
31 Fe nindrai’e ty hoe: Ndra te itraofako havilasy tsy hitety Azo. Le fonga nanao i hoe zay.
Amma Bitrus ya sake cewa “Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba”. Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.
32 Nandoake an-toetse atao Getsemone ao iereo, le hoe re amo mpiama’eo: Miambesara etoañe, fa hihalaly iraho.
Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa “Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a”.
33 Le nampindreze’e ama’e t’i Petera naho Iakobe naho i Jaona, naho niorotse nangovin-dre vaho nalovilovy;
Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai.
34 le hoe re tam’ iereo: Loho ore ty fiaiko, hoe te hikenkañe; eo hey, mijilova.
Sai ya ce masu “Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake”.
35 Nivike re naho nitoke an-tane eo, le nihalaly te, naho nimete ho narirañe ama’e i oray.
Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne “A dauke masa wannan sa'a daga gare shi.
36 Hoe re: O Aba Rae, kila mete ama’o; ehe ahankaño amako ty fitovy toy; fe tsy ty satriko, fa o satri’oo.
Ya ce “Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka”.
37 Nimb’eo re, le zoe’e nirotse iereo, vaho hoe re amy Petera: O Simona, miroro v’iheo? Tsy naha­tan-droro ora raike hao?
Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba?
38 Mijilova naho mihalalia, tsy mone hijoñe am-panjiziañe ao. Toe veka’e ty arofo, fe maifoifo ty nofotse.
Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne.
39 Nisitake indraike re, nihalaly, naho nahere’e i tsaray.
Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.
40 Ie nibalike nizoe’e nidefoke eo iereo (amy te nigibeñe o fihaino’eo), le tsy nahatoiñe aze.
Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome.
41 Nimb’eo fañintelo’e re, le nanoa’e ty hoe: Miròta hey, mitofà; soa izay, fa tendreke i oray; ingo fa nifotereñe am-pità’ o mpanan-kakeoo i Ana’ Ondatiy.
Ya sake komowa karo na uku yace masu “har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi”.
42 Miongaha, antao; hehe fa eo ty mifotetse ahy.
Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato.”
43 Ie mbe nisaontsy, pok’eo t’i Jodasy, mpiamy folo ro’amby rey, nindre ami’ty firimboñañe boak’amo mpisorom-beio naho o mpanoki-dilio vaho o roandriañeo ninday fibara naho kobaiñe.
Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su.
44 Ie amy zao, fa tinolo’ i mifotetse azey am’iareo ty famantarañe, ty hoe: Ty ondrofako, ro ie, Tsepaho, le tantalio mb’eo am-pañambeñe.
Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa “Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare.
45 Aa ie pok’eo, ro nimb’ama’e mb’eo, nanao ty hoe: O Raby, Talè! le norofa’e.
Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce “Ya malam!”. Sai ya sumbace shi.
46 Nipao-pitàñe ama’e iereo, le namahots’ aze.
Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.
47 Napontsoa’ ty raike amo nijohanjohañeo ty fibara’e le binira’e ty mpitoro’ i talèm-pisoroñey, nañitsike i ravembia’ey.
Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne.
48 Le hoe t’Iesoà tam’ iereo: Niakatse mb’etoa hoe mañoridañe mpikizo hao nahareo minday fibara naho kobaiñe hi­tsepake ahy?
Sai Yesu ya ce “kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni?
49 Boak’ andro iraho ro tama’ areo añ’ Anjomban’ Añahare ao nañoke, fa tsy nitsepahe’ areo; fe tsy mahay tsy ho heneke o Sokitse Masiñeo.
Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada.”
50 Nienga aze iereo, vaho nibioñe.
Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.
51 Mpanonjohy aze ty ajalahy nisikin-damba-leny nanaroñe i haboridaña’ey, fe tsinepa’ o ajalahio,
Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka.
52 f’ie nipolititse amy siki’ey, nirimatse añe am-pihaloa’e.
Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.
53 Kinororo’ iereo mb’amy talèm-pisoroñey mb’eo t’Iesoà; le hene nifanontoñe ao o mpisorom-beio naho o roandriañeo vaho o mpanoki-dilio.
Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa.
54 Norihe’ i Petera ey re mb’ an-kiririsam-pisorom-bey ao, le nitrao-piambesatse amo mpitoroñe namindro añ’afoo.
Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.
55 Nimanea’ o mpisorom-beio naho o mpivory iabio pay ty mpitaroñe hahaseseke Iesoà, hañohofan-doza ama’e—fe tsy nahaisake.
Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba.
56 Maro ty nanao kitomboke aze f’ie tsy niharo-sisý.
Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.
57 Le teo ty niongake nanao kipetake aze ami’ty hoe:
Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce.
58 Tsinano’ay ty asa’e ty hoe: Ho rotsaheko ty kivoho rinafi-pitàñe toy, le harafiko añate’ ty telo andro ty tsy nanoem-pitàñe.
“Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba”.
59 Ie amy zay, tsy niharo saontsy avao iereo.
Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.
60 Aa le niongake añivo eo i talèm-pisoroñey nañontane Iesoà ty hoe: Akore te Ihe tsy manoiñe o anisìa’ iretoañeo?
Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace “Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka?
61 Nianjin-dre, tsy nanoiñe. Nañontanea’ i talèm-pisoroñey indraike ami’ty hoe: Ihe hao i Norizañey, ty Ana’ i Rengèñey?
Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa “To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki?
62 Hoe t’Iesoà: Ie iraho, le ho isa’ areo miambesatse am-pitàn-kavanan-kaozarañe ey i Ana’ Ondatiy, mito­tsake amo rahon-dikerañeo.
Yesu ya ce “Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare”.
63 Rinia’ i talèm-pisoroñey o saro’eo le nanao ty hoe: Inoñe ty mbe ipaian-tika valolombeloñe?
Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace “Wacce shaida kuma zamu nema?
64 Fa jinanji’ areo i teratera’ey; akore arè? Le songa namira-vava t’ie mañeva ho vonoeñe,
Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa.
65 vaho nandrora’ ty ila’e, le nitakonañe ty lahara’e naho nikomondroeñe, naho nanoeñe ty hoe: Mitokia! le rinambe’ o mpigaritseo vaho rinarateha’iareo.
Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa “Yi annabci” Dogaran kuma suka yi ta marinsa.
66 Ie tan-kiririsa ambane ey t’i Petera, le nimb’eo ty raike amo ampela mpitoro’ i talèm-pisoroñeio,
Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.
67 le nahatrea i Petera namindro; hinente’e vaho nanoe’e ty hoe: Toe nimpiamy Iesoà nte Nazareta ka irehe.
Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce “Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu”.
68 Fe hoe ty lie’e: Alike amako izay, tsy apotako o enta’o zao, le niakatse mb’an-davaranga mb’eo vaho inay ty kekeon-akoholahiy.
Amma ya musa ya ce “Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta”. Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.
69 Ie niisa’ i mpitoroñ’ ampelay, le hoe re am’ondaty nijohanjohañeo: Toe mpiama’ iareo itìañe.
Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma daya daga cikinsu ne”.
70 Fe nandiera’e. Tsi-paepae’ izay, nanao ty hoe amy Petera o nizorazorao: Mpiam’ iareo vata’e n’iheo fa nte-Galilia.
Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus “Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai”.
71 Fe ndra nifàtse naho nifànta t’i Petera ami’ty hoe: Amoeako ze ondaty saontsie’ areo zao.
Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa “Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba”.
72 Inay ty kekeo faharoe; le nitiahi’ i Petera i nisaontsia’ Iesoà ty hoe: Aolo’ te mikekeo fañindroe’e i akoholahiy, le hitety ahy in-telo irehe; nitsakorea’e vaho nangoihoy ty rovetse.
Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku”. Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.

< Marka 14 >