< Lioka 7 >
1 Ie nifonitse i nilañone’e añatrefa’ i màroy le niheo mbe Kapernaomy mb’eo,
Bayan Yesu ya gama gaya wa mutanen dukan waɗannan abubuwa, sai ya shiga Kafarnahum.
2 le teo ty mpitorom-pifehen-dahin-defon-jato nisoheñe, narare, toe heta’e.
A can, akwai wani bawan wani jarumin yana ciwo, yana kuma a bakin mutuwa. Maigidansa kuwa yana sonsa sosai.
3 Ie nijanjiñe’e Iesoà, le nirahe’e homb’ ama’e ty androanavi’ o Jiosio hihalaly ama’e ty homb’eo hampijangañe i mpitoro’ey.
Jarumin sojan ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu dattawan Yahudawa wajensa, yana roƙonsa yă zo yă warkar da bawansa.
4 Aa ie nifanampe amy Iesoà, le nimanea’ iareo toreo ami’ty hoe: Evae’e te hanoe’o,
Da suka isa wurin Yesu, sai suka roƙe shi sosai, suka ce, “Wannan mutum, ai, ya dace a yi masa haka,
5 amy t’ie mpitea ty tanen-tika naho namboatse anjombam-pitontoñañe.
gama yana ƙaunar al’ummarmu ta Yahudawa, har ya gina majami’armu.”
6 Aa le niongake vaho nindre lia am’iereo t’Iesoà. Ie narine i anjombay, le nampanalakà’ i mpifelekey aze o rañe’eo hinday o entañe zao: O Rañandria, ko mañolañ’ ay fa tsy sazò ahy te ihe hiheo ambane’ ty tafo-trañoko.
Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya yi kusa da gidan, sai jarumin nan, ya aiki abokai su ce masa, “Ubangiji, kada ka dami kanka, gama ban isa ka shiga gidana ba.
7 Mbore ataoko tsy mañeva azo te izaho ro homb’ ama’o, fe mitsarà le ho jangañe i mpitorokoy.
Shi ya sa ban ma ga na isa in zo wurinka ba. Amma ka yi magana kawai, bawana zai warke.
8 Izaho ka fehèn-dily vaho mamehe lahindefoñe. Ie ataoko Akia ty raike le mandeha, naho ami’ty raike: Mb’etoa, le avy, vaho amy mpitorokoy: Anò zao, le anoe’e.
Gama ni kaina, mutum ne a ƙarƙashin iko, akwai kuma sojoji a ƙarƙashin ikona. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi, ga wani kuma in ce, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan kuma ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai yă yi.”
9 Ie jinanji’ Iesoà, le nilatsa, naho nitolike, nanao ty hoe am’ ondaty nañorik’ azeo: Itaroñako te mbe lia tsy nahatrea fatokisam-bey hoe izay ndra e Israele atoy!
Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki sosai. Ya juya ya wa taron da yake bin sa, “Ina faɗa muku, ban taɓa samun irin bangaskiya mai girma haka ko cikin Isra’ila ba.”
10 Ie pok’ añ’ anjomba ao o nafanto’eo, le nizoe’ iereo jangañe i mpitoroñe natindriy.
Sai mutanen da aka aika, suka koma gida, suka tarar bawan ya warke.
11 Ie amy loak’androy, nigodañe mb’ an-drova atao Naina mb’eo t’Iesoà; le nañorik’ aze ty maro amo mpiama’eo naho i lahialeñey.
Ba a daɗe ba, sai Yesu ya tafi wani garin da ake kira Nayin. Almajiransa da taro mai yawa suka tafi tare da shi.
12 Ie nitotoke i lalambein-drovay, intoy ty takon-dolo boak’ao, ty ana-dahy bako tokan-drene’e, vantotse; le nañorik’ aze ty valobohòke boak’ an-drova ao.
Da ya yi kusa da ƙofar garin, sai ga wata gawa ana fitowa da ita. Shi ne ɗa kaɗai ga mahaifiyarsa, ita kuma gwauruwa ce. Taro mai yawa daga garin yana tare da ita.
13 Ie nivazoho’ i Talè i rakembay le niferenaiña’e naho nanoe’e ty hoe: Ko mirovetse!
Da Ubangiji ya gan ta, sai ya ji tausayinta ya ce, “Kada ki yi kuka.”
14 Nimb’eo re nitsapa i horantsañey vaho nitsangañe o mpitakoñeo le hoe re: O kirahe, hoe iraho ama’o: Mivañòna!
Yesu ya je ya taɓa akwatin gawar, sai masu ɗaukarsa suka tsaya cik. Sai ya ce, “Saurayi, na ce maka, tashi!”
15 Nitroatse amy zao i nivetrakey naho nisaontsy vaho natolo’e aman-drene’e.
Sai mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuma ya ba da shi ga mahaifiyarsa.
16 Hene niazo’ ty anifañe ondatio le nañomey engeñe an’ Andrianañahare ami’ty hoe: Mpitoky ra’elahy ty nitroatse amantika; vaho ty hoe: Nitilike ondati’eo t’i Andrianañahare.
Sai tsoro ya kama su duka, suka yabi Allah, suna cewa, “Babban annabi ya bayyana a cikinmu. Allah ya zo domin yă taimaki mutanensa.”
17 Nanitsike Iehodà naho o rova mañohok’ aze iabio ty fiboelea’ i talily ty ama’ey.
Wannan labarin game da Yesu, ya bazu ko’ina a Yahudiya da kewayenta.
18 Natalili’ o mpiana’ i Jaonao ama’e i hene rezay.
Almajiran Yohanna suka gaya masa dukan waɗannan abubuwa. Sai ya kira biyu daga cikinsu,
19 Aa le kinanji’ i Jaona ty mpiana’e roe le nampihitrife’e mb’amy Talè mb’eo hañontane aze ty hoe: Ihe hao i ho aviy, ke hafa ty ho tamàe’ay?
ya aike su wurin Ubangiji, su tambaya su ce, “Kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?”
20 Ie nivotraha’ indaty rey le hoe ty asa’ iareo: Nirahe’ i Jaona Mpandipotse mb’ama’o mb’etoan-jahay hañontàne ty hoe: Ihe hao i Ho aviy, kera mbe añe i tamaen-tikañey?
Da mutanen suka iso wurin Yesu, sai suka ce, “Yohanna Mai Baftisma ne ya aike mu wurinka, mu yi tambaya, ‘Ko kai ne wanda zai zo, ko kuma mu saurari wani dabam?’”
21 Amy oray avao ty nañafaha’e ondaty maro amo areteñeo naho amo hasilofañeo naho amo anga-dratio vaho nampañisake ty goa maro.
A daidai lokacin nan, Yesu ya warkar da mutane da yawa masu ciwo, masu cututtuka, da kuma masu mugayen ruhohi. Ya kuma ba makafi da yawa ganin gari.
22 Le hoe ty natoi’ Iesoà: Akia, atalilio amy Jaona o raha niisa’areo naho nijanjiñeñeo; te mahaoniñe o feio, minokitse o komboo, malio o angamaeo, mijanjiñe o giñeo, miheren-ko veloñe o vilasio vaho taroñeñe amo rarakeo i Talili-soay.
Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
23 Haha ze tsy mitorifike amako.
Mai albarka ne mutumin da bai yi shakkar bangaskiyar da yake da ita a kaina ba.”
24 Ie niavotse i mpiana’ i Jaona rey, le nitalily i Jaona amy lahialeñey t’Iesoà, ami’ty hoe: Hisamba inoñe ty lia’areo mb’am-babangoañe añe? Ty Bararata atroetroen-tioke hao?
Bayan almajiran Yohanna suka tafi, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna ya ce, “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
25 ke ino ty niakara’ areo ho isaheñe? Ondaty misikin-tsoa hao? Toe añ’ anjombam-pifehe ao o mpisaroñe lamba marerarerao naho o miaiñ’ añolèñañeo;
In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da tufafi masu kyau ne? A’a, masu sa kayan tsada da suke cikin annashuwa, ai, a fada suke.
26 he ino ty niavota’ areo ho sambaeñe? Mpitoky hao? Eka! hoe iraho ama’areo: lombolombom-pitoky re.
Amma me kuka je kallo? Annabi? I, ina kuma faɗa muku, ya ma fi annabi.
27 Ie nipatereñe ty hoe: Ingo, iraheko aolon-dahara’o eo ty hañajary ty lala’o aolo’o.
Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiko da ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanya, a gabanka.’
28 Aa hoe ty entako ama’areo: Amy ze sinaman-droakemba tsy teo ty mpitoky bey te amy Jaona Mpandipotse; fe jabajaba te ama’e ze minjilìte’e amy Fifehean’Añaharey.
Ina faɗa muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yohanna girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”
29 Songa nañomey to an’ Andrianañahare ondaty nahajanjiñeo naho o mpamory vili-lohao, amy t’ie niliporeñe ami’ty filipora’ i Jaona,
(Dukan mutane, har da masu karɓar haraji, da suka ji kalmomin Yesu, sai suka yarda cewa hanyar Allah gaskiya ce, domin Yohanna ne ya yi musu baftisma.
30 fe nifarie’o Fariseoo naho o mpanoki-dilio ty nisafirien’ Añahare ho a iareo amy t’ie tsy nimete nilipotse ama’e.
Amma Farisiyawa da masanan dokoki, suka ƙi nufin Allah game da su, domin Yohanna bai yi musu baftisma ba.)
31 Inoñe arè ty handrazañako ondati’ ty tariratse toio, isareañe ami’ty ino?
Yesu ya ci gaba da cewa, “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Kamar me suke?
32 Ie hambañe ami’ty ajaja mitobok’ an-tsena ao mifampikoike ty hoe: fa nitiofa’ay soly fe tsy nitsinjaha’areo; nibekoa’ay fandalañe, fe tsy niroveta’areo.
Suna kama da yaran da suke zama a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, “‘Mun busa muku sarewa, amma ba ku yi rawa ba, Mun kuma yi muku waƙar makoki, ba ku kuma yi kuka ba.’
33 Aa ie niloneake t’i Jaona Mpandipotse, tsy nikama mofo, tsy ninon-divay le hoe ty asa’ areo: Aman-kokolampa re.
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo, ba ya cin burodi, ba ya shan ruwan inabi, sai kuka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
34 Ie nivotrake eo ka i Ana’ ondatiy mihinañe naho minoñe, le hoe ka nahareo: Hehe! milonja naho migenoke divay ty rañem-pamory vili-loha naho bey hakeo tia.
Ɗan Mutum ya zo yana ci, yana sha, sai kuka ce, ‘Ga mai yawan ci, mashayi, da kuma abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’
35 Fe mahazo to amo ana’eo ty hihitse.
Amma akan tabbatar da hikima ta gaskiya bisa ga dukan’ya’yanta.”
36 Ie amy zay, nañambara Iesoà ty Fariseo hitrao-pikama. Aa le niheo mb’añ’anjomba’e ao re, niambesatse.
To, ana nan, sai ɗaya daga cikin Farisiyawa ya gayyaci Yesu cin abincin yamma a gidansa, ya kuwa tafi gidan Bafarisiyen, ya zauna a tebur.
37 Le teo ty ampela beihakeo an-drova ao, ie naharendreke t’ie nandrenàndre nikama añ’anjomba’ i Fariseoy, le nandesa’e solike mañitse ami’ty anan-tsinihara.
Da wata mace wadda ta yi rayuwar zunubi a wannan gari ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, sai ta kawo ɗan tulun turaren alabasta,
38 Nijohañe amboho’e eo re nirovetse am-pandia’e, nandè o fandia’eo an-dranomaso’e naho nifòra’e amo volo’eo; le nitolom-pañoroke o fandia’eo vaho nihosora’e solike mañitse.
ta kuma tsaya daga bayansa, wajen ƙafafunsa tana kuka, sai hawayenta sun fara zuba a ƙafafunsa. Sai ta goge su da gashin kanta, ta sumbace su, sa’an nan ta shafa musu turare.
39 Ie nioni’ i fariseo nañambara aze le hoe ty tsakore’e: Naho toe nimpitoky ondatio, le ho nifohi’e te ia izay naho ty sata’ o ampela mitsapatsapa azeo; t’ie bei-hakeo.
Da Bafarisiyen da ya gayyace shi, ya ga wannan, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce take taɓansa, da kuma irin macen da take, cewa mai zunubi ce.”
40 Aa le natoi’ Iesoà ty hoe: O Simona, Inao ty ivolañako. Le hoe re: Isaontsio, Talè.
Sai Yesu ya ce masa, “Siman, ina da abin da zan faɗa maka.” Shi kuwa ya ce, “Malam sai ka faɗa.”
41 Teo ty mpampisongo amam-pisongo roe. Ty raike nitsepake bogady liman-jato, ty raike limam-polo.
Yesu ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu da suke riƙe bashin mai ba da rance. Ana bin guda dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin.
42 Aa kanao tsy eo ty hahavaha’ iareo, sindre nihevea’e. Toiño iraho, ia am’ iereo ty ho lako fitea aze?
Dukan biyun suka gagara biyansa, sai ya yafe musu. To, a ganinka, wa zai fi ƙaunar mutumin nan?”
43 Hoe ty natoi’ i Simona: Va’e i nihevea’e beiy. Hoe t’Iesoà tama’e: To i saontsi’oy.
Siman ya amsa ya ce, “A ganina, wanda aka yafe wa mai yawa ne.” Sai Yesu ya ce, “Ka faɗa daidai.”
44 Nitolik’ amy ampelay re le nisaontsy amy Simona ty hoe: Hehek’ o rakembao? Nizilik’ añ’ anjomba’o atoan-draho le tsy nanjotsoa’o rano hanasàko tomboke, fe o rano-pihaino’eo ro nanasa o tombokoo vaho namaoke aze o maroi’eo.
Sai ya juya wajen macen, ya ce wa Siman, “Ka ga macen nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwa don ƙafafuna ba, amma ta wanke ƙafafuna da hawayenta, ta kuma goge su da gashin kanta.
45 Tsy nondrohe’o; fe boak’ ami’ty nimoahako atoañe le lia’e tsy napo’e ty oroke o tombokoo.
Ba ka yi mini sumba ba, amma tun shigowata a nan, macen nan ba tă daina sumbar ƙafafuna ba.
46 Tsy nañiliña’o menake ty lohako, fe hinoso’ ty rakemba tia solike mañitse o tombokoo.
Ba ka shafa mai a kaina ba, amma ta zubo turare a ƙafafuna.
47 Aa hoe ty taroko ama’o, O tahi’e nimaroo, fonga nimeatse, amy t’ie bey fikokoañe. Aa ze niheveañe kede, kede ka ty fitea’e.
“Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawa, an gafarta mata, gama ƙaunarta mai yawa ce. Amma wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, yakan nuna ƙauna kaɗan.”
48 Le hoe re tamy rakembay: Hene nilioveñe o hakeo’oo.
Sai Yesu ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.”
49 Aa hoe ty fiñeoñeo’ o nitrao-pikama ama’eo: Ia ka ty mbore mañaha hakeo tia?
Sauran baƙin suka fara ce wa juna, “Wane ne wannan, wanda har yake gafarta zunubai?”
50 Hoe t’Iesoà tamy ampelay: Nandrombak’ azo ty fatokisa’o; akia an-kanintsiñe.
Yesu ya ce wa macen, “Bangaskiyarki ta cece ki, ki sauka lafiya.”