< Lioka 5 >
1 Teo te nifanihisihy ama’e ondatio hijanjiñe ty tsaran’ Añahare añ’ olo’ i oñe Genesaretay
Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
2 le nivazoho’e ty lakañe roe añ’ olon-drano ey, ie fa niakatse hanasa harato o tompo’eo.
Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
3 Nijoñe an-daka’ i Simona ao re nihalaly te hisitake amy olotsey. Aa le niambesatse an-dakañe ey re nañoke ondatio.
Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
4 Ie modo i fañoha’ey, le hoe re amy Simona: Mivevea mb’an-daleke mb’eo vaho ajoño ao o harato’ areoo hanarike.
Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
5 Le hoe ty natoi’ i Simona aze: O Rañandria, nifanehak’ avao zahay aniankale le tsy nahazo leo raike; fe amo saontsi’oo, hajoko ao i haratoy.
Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
6 Ie nanoe’ iereo izay, le nivokatse fiañe nifamorohotse nahariatañe i harato’ iareoy.
Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
7 Aa le nitsikaore’e o rañe’ iareo amy lakañe ila’e eiio ty hañolotse iareo; nimb’eo iereo, le nipeae’iereo fiañe i lakañe roe rey, vaho ho nilempotse.
Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
8 Ie nahaoniñe izay t’i Simona Petera, le nihotrak’ am-pandia’ Iesoà eo nihalaly ty hoe: O Rañandria, misitaha amako fa ondaty bey hakeo.
Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
9 Toe niveren-draha t’i Simona naho o rañe’eo ami’ty hamarom-piañe niazo.
Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
10 Nihoe izay ka t’i Jaona naho Iakobe, ana’ i Zebedio mpitrao-pitoloñe amy Simona. Hoe t’Iesoà tamy Simona: Ko mahimahiñe fa ondaty ka ty ho tsepahe’o henane zao.
Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
11 Ie toly an-tamboho ey i lakañe rey, le fonga nafoe’ iereo vaho nañorik’ aze.
Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
12 Ie tan-drova raike t’Iesoà, intoy ty lahilahy atseke ty angamae; ie nahaisake Iesoà, le nihohok’ an-dahara’e nitoreo ama’e ty hoe: O Rañandria naho satri’o, mahalio ahy irehe.
Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
13 Nahiti’ Iesoà ty fità’e, nitsapa aze le nanao ty hoe: Satriko ‘nio, maliova; naho niafak’ amy zao i haangamae’ey
Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
14 vaho hinatahata’e tsy hitalily am’ondaty, am’ty hoe: Akia miboaha amy mpisoroñey, le ibanabanào i linili’ i Mosèy ami’ty fahaliova’o ho fitaliliañe.
Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
15 Fe àntsake te niboele ty enge’e, le niropak’ ama’e i lahialeñey hijanjiñe naho ho jangañeñe amo arete’eo.
Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
16 F’ie nivike mb’ am-babangoañe añe, niloloke.
Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
17 Teo te niambesatse eo ty fariseo naho mpañoke Hake hirik’ an-drova e Galilia naho e Iehodà iaby naho boake Ierosaleme añe, le naò’e, vaho tama’e ty haozara’ i Talè hampijangañe.
Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
18 Ie amy zao, nendese’ ondaty an-tihy ty lahilahy kepeke, nipay ty hanjilihañe aze ao, hampandreañe aze añatrefa’e eo.
A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Aa ie tsy naharendreke ty hampitsifirañe aze amy lahialeñey, le nanganik’ ambone’ i anjombay vaho nazotso’ iareo an-tihy, boak’an-tafo mb’ añatrefa’ Iesoà, añivo eo i mararey.
Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
20 Ie nioni’e ty fatokisa’ iareo, le hoe re ama’e: O koahe, afa-tahin-drehe.
Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
21 Fe nitsakore ty hoe o mpanoki-dilio naho o fariseoo: Ia o miteraterao? Ia ty mahafa-kakeo naho tsy i Andrianañahare avao?
Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
22 Fe nifohi’ Iesoà ty ereñeren-tro’ iareo le tinoi’e ty hoe: Ino o fitsakorean’ arofo’ areoo?
Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
23 Ty aia ty mora, ty manao ty hoe: Afake o hakeo’oo? ke ty hoe: Miongaha, mañaveloa?
Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
24 Aa soa te hampahafohineñe anahareo te aman-dily an-tane atoy i Ana’ ondatiy hañaha hakeo, le hoe re amy nisilofe’ i hakepehañeiy: Inao! Miongaha, tintino o tihi’oo, akia mb’ añ’ akiba’o añe.
Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
25 Aa le nitroatse añatrefa’ iereo amy zao re, nandrambe i nandrea’ey vaho nimpoly, nandrenge an’ Andrianañahare.
Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
26 Nilatsa iaby iereo naho nibango an’ Andrianañahare, vaho nanao ty hoe am-pañeveñañe: Nahaoniñe raha tsitantane tika anindroany.
Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
27 Añe zay, le nienga t’Iesoà naho nahavazoho ty mpamory vili-loha atao Levy, niambesatse am-pandroroñañe ao, le hoe re tama’e: Oriho iraho.
Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
28 Aa le nifarie’e ze he’e naho niongake vaho nañorik’ aze.
Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
29 Nanao sandalam-bey ho aze añ’ anjomba’e ao t’i Levy, le maro ty mpamory vili-loha naho ondaty ila’e nitrao-piambesatse am’iereo.
Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
30 Fe niñeoñeoñe amo mpiama’eo o Fariseoo naho o mpanoki-dili’ iareoo ami’ty hoe: Ino ty itraofa’ areo fikama naho finoñe amo mpamory vili-lohao naho amo bey hakeoo?
Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
31 Tinoi’ Iesoà ty hoe: Tsy o jangañeo ro mipay mpanaha fa o marareo;
Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
32 Tsy avy hikoike o vantañeo iraho fa o mpandilatseo, hisoloho.
Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Le hoe ty asa’iareo tama’e: Akore te mililitse naho miloloke o mpiana’ i Jaonao, manao izay ka o mpiamo Fariseoo, fe mitolo-pihinañe naho minoñ’ avao o Azoo?
Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
34 Hoe ty natoi’ Iesoà: Lefe’ areo hao ty hampililitse ty longo’ i mpañengay ie mbe am’ iereo i mpañengay?
Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
35 Mbe ho avy ty andro hanintahañe i mpañengay; hililitse amy andro zay iereo.
Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
36 Hoe ka ty nirazaña’e: Tsy ia ty manakeke lamba vao ami’ty tsirodea, fa ho riate’ i vaoy, naho tsy mete hivitrañe amy tsirodeay ty tampa’ i vaoy.
Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
37 Tsy eo ka ty hañiliñe divay vao an-jonjon-kolitse hambo’e ao, kera ho tosire’ i divay vaoy i zonjon-kolitse hambo’ey vaho hianto i zonjoñey.
Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
38 Tsy mete tsy ailiñ’ an-jonjoñe vao ao ty divay vao.
Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
39 Tsy eo ty minoñe amy elay ty hipay ty vao aniany; fa hoe re: I elay ro soa.
Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”