< Josoa 9 >

1 Ie añe, naho fa jinanji’ o mpanjaka iaby alafe’ Iardeney, am-bohibohitse naho am-bavatane ey naho añolo’ i Riake Jabajabay pak’ e Lebanone añeo; i nte-Kete naho i nte-Amore, i nte-Kanàne, i nte-Perizý, i nte-Kivý, vaho i nte-Iebosý;
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 le nikabija, nifañosoñe hialy amy Iehosoa naho am’Israele.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 Fe jinanji’ o mpimone’ i Giboneo ty nanoe’ Iehosoa am’ Ieriko naho amy Ay,
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 le nikilily famañahiañe: nimb’eo iereo nisare sorotà; ninday voro-gony am-borìke naho kontran-divay toro naho rota nitakefeñe;
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 naho tsoron-kana sinosok’ am-pan­dia’e naho sikiñe voroboro’e ho saro’ iareo; mbore nimaike vaho ni­voravora ty mofo iaby fivati’ iareo.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 Niheo mb’ amy Iehosoa an-tobe e Gilgale ao iereo, nanao ty hoe ama’e naho amo lahilahi’ Israeleo; Boake tsietoitane añe zahay; aa ehe ifañinào.
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 Le hoe ondaty ana’ Israeleo amo nte-Kiveo: Hera t’ie mpimo­neñe ama’ay atoy; aa le aia ty hifañinà’ay.
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 Le hoe ty asa’ iareo am’ Iehosoa: Mpitoro’ areo zahay. Le hoe ty nanoe’ Iehosoa: Ia v’inahareo naho boak’aia?
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 Le hoe ty asa’ iareo ama’e: Boake tsietoitane añe o mpitoro’oo t’ie nivotrak’ atoy ty tahina’ Iehovà An­drianañahare’ areoy; fa jinanji’ay ty enge’e naho ze hene fitoloña’e e Mitsraime ao,
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 naho ze he’e nanoe’e amy mpanjaka roe nte-Amore alafe’ Iardeney añe rey, toe amy Sihone mpanjaka i Khesbone naho amy Oge mpanjaka’ i Basane e Astarote añe.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 Aa le nisaontsy ama’ay o mpiaolo’aio naho o fonga mpimoneñe an-tane’aio, nanao ty hoe: Mindesa vaty amy liay, le akia mifañaoña am’ iereo vaho ano am’ iereo ty hoe: Mpitoro’ areo zahay; ie amy zao, ehe ifañinao.
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 Intoy ty mofo nendese’ay ho vaty ie mbe nimae boak’ añ’ aki­ba’ay amy andro nion­jona’ay hihitrifa’ay mb’ama’ areo mb’ etoay, hehe t’ie maike vaho demodemoke.
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 Le nivao o kontran-divay retoa t’ie fineno’ay, ingo te mikoneatse; hehe ka o siki’aio naho o hana’aio, ie fa modo iaby ty amy halavi’ i liay.
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 Nangala’ o lahilahio ty vati’ iareo, f’ie tsy nihalaly fanoroañe am-palie’ Iehovà.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 Aa le nifampilongo am’ iereo t’Ie­hosoa vaho nifañina t’ie hengañe ho veloñe le nifanta ama’e ka o roandria’ i valobohòkeio.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 Ie telo andro añe te nifañina le jinanji’ iareo t’ie mpañohoke naho mpimoneñe añivo’ iareo ao avao.
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 Ie nañavelo le nivotrak’ amo rova’ iareoo amy andro faha-teloy o ana’ Israeleo. Ty rova’ iareo: i Gibone, le i Kefirà, i Birote vaho i Kiriate-iearime.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 Tsy pinao’ o ana’ Israeleo iereo, ty amy nifantà’ o roandria’ i valobohòkeio amy Iehovà Andrianañahare’ Israele. Aa le niñeoñeoñe amo roandriañeo i valobohòkey.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 Fe hoe o roandriañeo amy valobohòkey: Fa nifanta’ay amy Iehovà Andrianañahare’ Israele; aa le ko paoheñe.
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 Zao ty hanoan-tika: hadoñe ho veloñe; tsy mone ho aman-tika ty haviñerañe, ty amy fanta nifantà’ay am’ iereoy.
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 Le hoe o roandriañeo ty am’ iereo: Angao ho veloñe; le nanoeñe mpamatsi-katae naho mpitari-drano ho a i valobohòkey, ty amy nitaroña’ o roandriañeo.
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Kinoi’ Iehosoa, vaho nisaon­tsie’e ty hoe: Akore ty namañahia’ areo anay ami’ty hoe: Boa-davitse anahareo zahay, ie mpimo­neñe añivo’ay atoy avao?
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 Aa le fokom-patse nahareo; nainai’e tsy ho modo t’ie ho mpitoroñe, mpamatsike hatae vaho mpitari-drano ho añ’ anjomban’ Añahareko.
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 Nanoiñe Iehosoa ami’ty hoe iereo; Amy te toe natalily amo mpitoro’oo te linili’ Iehovà Andrianañahare’o i mpitoro’e Mosèy te hatolo’e anahareo i tane iabiy le ho mongoreñe aolo’ areo ze fonga mpimone’ i taney, aa le nampirevendreveñe anay o fiai’aio ty ama’ areo; izay ty nanoe’ay o raha zao.
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 Ie henane zao, ingo, am-pità’o zahay: aa le ano ama’ay ze atao’o soa naho to am-pi­vazohoa’ areo.
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 Aa le izay ty nanoe’e am’ iereo, vaho rinomba’e am-pità’ o ana’ Israeleo, fa tsy vinono;
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 ie nanoe’ Iehosoa mpama­tsi-katae naho mpitari-drano amy andro zay ho amy valobohòkey naho ho a i kitreli’ Iehovày ampara henaneo, amy toetse ho joboñe’ey.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< Josoa 9 >