< Josoa 8 >

1 Le hoe t’Iehovà am’Iehosoa: Ko hemban-drehe, ko manahelo; miavota naho endeso mindre ama’o mb’e Ày mb’eo ze hene lahin-defoñe, Inao fa natoloko am-pità’o ty mpanjaka’ i Ày naho on­dati’eo naho i rova’ey vaho i tane’ey.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
2 Hanoe’o amy Ày naho amy mpan­jaka’ey hambañe amy nanoa’o am’ Ieriko naho i mpan­jaka’eiy; fe ho tana’ areo ho tsindro’ areo o vara’eo, naho o añom­be’eo, Vandroño boak’ am-boho’e ao i rovay.
Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
3 Aa le niongake t’Iehosoa rekets’ o hene’ lahin-defoñeo, hionjoñe mb’e Ày mb’eo; jinobo’ Iehosoa ty lahilahy telo-ale, fanalolahy mahavany, vaho nirahe’e mb’eo haleñe.
Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
4 Na­fanto’e ami’ty hoe: Inao! hiampitse amboho’ i rovay nahareo hamandroñe i rovay, ko halavira’ areo i rovay, vaho fonga mihentseña.
ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
5 Izaho reketse ze hene’ ondaty amako ro higodañe mb’ amy rovay mb’eo; ie amy zao, naho miakatse hañoridañe anay iereo manahake i teoy, le handripak’ an-day añatrefa’ iareo zahay.
Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
6 Ie miakatse hañoridañe anay, naho fa tinari’ay hisitak’ amy rovay le hanao ty hoe: Hehe t’ie milay an-tikañe manahake tam-pifotora’ey. Izay ty hilaisa’ay aolo’ iareo mb’eo.
Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
7 Hiongak’ am-piampirañe amy zao nahareo hitavañe i rovay; fa hatolo’ Iehovà Andrianañahare’ areo am-pità’ areo.
sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
8 Ie nivotrake amy rovay, le ampiforeheto añ’ afo i rovay; i tsinara’ Iehovày ty hanoa’ areo aze; inay, fa liniliko.
Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
9 Aa le nampionjone’ Iehosa; le nimb’eo iereo niampitse, naho nitobe añivo’ i Betele naho i Ày ahandrefa’ i Ày ao; nialeñe am’ on­datio avao t’Iehosoa.
Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
10 Nañampitso amy loak’ àndroy t’Iehosoa, le nitehafe’e ondatio vaho nionjoñe mb’eo, ie naho o mpiaolo’ Israeleo ty niaolo ondatio mb’e Ày añe.
Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
11 Aa le nionjom’ beo iaby ondaty nindre ama’eo, o lahindefoñeo, naho nañarine mb’eo, le nijohañe tandrife i rovay, vaho nitobe avara’ i Ày ey; toe añivo’e naho i Ày eo ty vavatane.
Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
12 Nandrambe lahilahy va’e lime-arivo re vaho nampiampire’e añivo’ i Betele naho i Ày ahandrefa’ i rovay.
Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
13 Aa le nisalahàñe i maroiy: i lahialeñe avara’ i rovaiy naho o nivolio am-piampirañe ahandrefa’ i rovay ao; le nimb’ añ’ ivo’ i vavataney hialeñe t’Iehosoa.
Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
14 Ie amy zao, naho nahaoniñe izay ty mpanjaka’ i Ay le nalisa niongake maraindray o lahilahi’ i rovaio vaho niakatse hiambotrak’ am’ Israele an-kotakotake, ie naho ondati’e iabio, mb’ amy namotoañañey, aolo’ i Arabày; fe tsy napota’e te amboho’ i rovay ty nivoñoñe aze.
Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
15 Nanao sare gioke aolo’ iareo t’Iehosoa naho Israele iaby, le nan­dripàke mb’ an-dala’ i fatrambeiy mb’eo.
Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
16 Aa le kinoike iaby ondati’ i Aio hifanontoñe, hañoridàñe; le nihoridà’ iareo t’Iehosoa, nisitake amy rovay.
Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
17 Tsy nengaeñe ondaty ty e Ay ndra e Betele ao ze tsy niakatse hañotroke Israele; napo’ iareo nisokake i rovay le nañoridañe Israele.
Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
18 Aa le hoe t’Iehovà am’ Iehosoa: Atora-kitsio mb’amy Ay i lefoñe am-pità’oy; fa hatoloko am-pità’o. Aa le nahiti’ Iehosoa mb’ amy rovay i lefoñe am-pità’ey.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
19 Nivora­tsake boak’ an-toe’e ao amy zao o niam­pitseo; namorehetse ty lay mb’eo ty amy nañitia’e i fità’eiy naho nimoak’ amy rovay ao, nitavañe aze, vaho namiañe afo amy rovay.
Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
20 Aa ie nitolike naho niisake mañamboho o lahilahi’ i Aio, ingo nañatoeñe mb’ an-dikeramb’eo i rovay, le tsy nioniñe ty hipota­tsaha’ iareo ke mb’ atia he mb’ etia amy te nibalike mb’ amo nañoridañe iareoo mb’eo o nilay mb’ ampatrambeio.
Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
21 Naho nioni’ Iehosoa naho Israele iaby te tinava’ o nanàmpokeo i rovay naho te nionjoñe mañambone ty hatoe’ i rovay, le nibalike, vaho zinama’ iareo o lahilahi’ i Aio.
Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
22 Niakatse i rovay ka o ila’eo hifañatrek’ am’ iareo; aa le niarikoboña’ Israele, etia ty ila’e, atia ty ila’e, vaho binaibai’e iereo ampara’ t’ie po-sehanga’e leo raike tsy nahapoliotse.
Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
23 Nenga’ iereo veloñe ty mpanjaka’ i Ay vaho nasese mb’ am’ Ieho­soa mb’eo.
Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
24 Ie nihenefe’ Israele zamañe o mpimone’ i Ay an-kivoke eio naho i ampatrañe ey nañoridañe iareo rezay, toe nampitsingori­triem-pibara ampara’ t’ie nimongotse, le hene nitolike mb’e Ay mb’eo t’Israele, nanjevoñ’ aze an-dela-pibara.
Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
25 Ty hamaro nikorovok’ amy andro zay amo lahilahy naho rakembao, le rai-ale-tsi-ro’arivo—ze hene’ondati’ i Ay.
A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
26 Tsy nafore’ Iehosoa ty fità’e nañity i lefoñey ampara’ te nimongore’e ze fonga mpimone’ i Ay.
Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
27 O añombeo naho i vara-fikopa’ i rovay avao ty tinava’ Israele ho fitsindro’e ty amy tsara linili’ Iehovà am’Iehosoay.
Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
28 Aa le finorototo’ Iehosoa ty Ay naho nanoe’e tamboho tsy modo, toe hoake ampara’ henane.
Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
29 Naradorado’e an-katae ty mpanjaka’ i Ay ampara’ te hariva; ie tsofots’ andro le nandily t’Iehosoa naho nazotso’ iareo amy hataey i lolo’ey, naho navokovoko an-dalam-bei’ i rovay vaho naonjoñe ama’e ty votrim-bato jabajaba mbe eo henanekeo.
Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
30 Le namboara’ Iehosoa kitrely t’Iehovà, Andrianañahare’ Israele, am-bohi’ Ebale eo
Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
31 ty amy nandilia’ i Mosè mpitoro’ Iehovà o ana’ Israeleoy, manahake i sinokitse amy boke Hà’ i Mosèiy, kitrely vato tsy pinèke, tsy nañonjonañe viñe; naho nibanabanae’ iareo soroñe am’ Iehovà, vaho nandenta engan-kanintsiñe.
kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
32 Sinoki’e amo vatoo ty hambañe amy Tsara’ i Mosèy, nisokire’e añatrefa’ o ana’ Israeleo.
A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
33 Hene nijohañe añ’ila’ i vatam-pañinay etoy naho añ’ ila’e eroy añatrefa’ o mpisoroñe nte-Levy nitarazo i vatam-pañina’ Iehovàio t’Israele naho o mpiaolo’eo naho o mpifehe’eo vaho o mpizaka’eo sindre tao ty renetane naho t’indaty; ty ila’e aolo’ i vohi-Gerizimey naho ty ila’e aolo’ i vohi-Ebaley; ty amy nandilia’ i Mosè mpitoro’ Iehovà am-baloha’ey, hitatàñe o ana’ Israeleo.
Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
34 Modo izay le vinaki’e o enta’ i Hake iabio, o tatao naho o fatseo, ze hene sinokitse amy boke’ i Hake ao.
Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
35 Ndra raik’ amo tsara linili’ i Mosèo tsy nado’ Iehosoa fa hene nivakie añatrefam-pivori-bei’ Israele, naho amo rakembao, naho amo keleiañeo vaho amo renetane niharo am’ iereoo.
Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.

< Josoa 8 >