< Jakoba 4 >
1 Hirik’aia o aly naho fifandierañe ama’ areoo? Tsy o hasiji’ areoo hao ty mitrobo añ’ova ao?
Me yake jawo faɗace-faɗace da gardandami a tsakaninku? Ashe, ba sha’awace-sha’awacenku da suke yaƙi a zukatanku ba ne?
2 Mikirañe f’ie tsy manañe, mamono; mihàñe fe tsy mahazo, naho mifandietse vaho mialy, f’ie tsy manañe amy te tsy mihalaly,
Kukan nemi abu ku rasa, sai ku yi kisa da ƙyashi. In kuka rasa abin da kuke nema sai ku shiga yin gardama da faɗa. Kukan rasa ne, domin ba ku roƙi Allah ba.
3 Mihalaly fe kanao tsy tendreke, vàlañe i hatakey, ie ho nirite’areo an-kadrao avao.
Sa’ad da kuka roƙa, ba kwa samu, don kun roƙa da mugun nufi, don ku kashe abin da kuka samu a kan sha’awace-sha’awacenku.
4 Ty karapilo! Tsy apota’ areo hao te falaiñañe an’ Andrianañahare ty firañetañe ami’ty voatse toy? Aa le ze te ho rañe’ ty tane toy manao ty vata’e ho rafelahin’ Añahare.
Ku mazinata, ba ku san cewa abokantaka da duniya gāba ce da Allah ba? Duk wanda ya zaɓa yă zama abokin duniya ya zama abokin gāban Allah ke nan.
5 Hera atao’ areo te tsy aman-tali’e ty itsara’ i sokitse masiñey t’y hoe: Mañiriñe am-pihàñañe ty Arofo mimoneñe aman-tikañe ao.
Ko kuna tsammani a banza ne Nassi ya ce ruhun da ya sa yă zauna a cikinmu yana kishi sosai?
6 Fe itolora’e fañisoham-bey. Izay ty anoe’e ty hoe: Zeharen’ Añahare ty mpiebotsebotse, fe tolora’e arofo ty mpirèke.
Amma yakan ba mu alheri a yalwace. Shi ya sa Nassi ya ce, “Allah yana gāba da masu girman kai amma yakan ba da alheri ga masu tawali’u.”
7 Aa le miambanea aman’ Añahare. Liero i mpañìnjey, le hibioñe.
Saboda haka, ku miƙa kanku ga Allah. Ku yi tsayayya da Iblis, zai kuwa guje ku.
8 Harineo t’i Andrianañahare, le hitotofa’e. Mandiova fitàñe ry mpanan-kakeo vaho mañefera arofo ry mpanao sadrò-lahiagao.
Ku matso kusa da Allah shi kuwa zai matso kusa da ku. Ku wanke hannuwanku, ku masu zunubi, ku kuma tsarkake zukatanku, ku masu zuciya biyu.
9 Mihontoha, mandalà naho mangololoiha; afotero ho firovetañe ty fitohafa’ areo vaho halonjerañe ty haeha’ areo.
Ku yi baƙin ciki, ku yi makoki ku kuma yi kuka. Ku mai da dariyarku ta zama makoki, farin cikinku kuma yă zama ɓacin zuciya.
10 Miambanea aolo’ i Talè le hongahe’e.
Ku ƙasƙantar da kanku a gaban Ubangiji, zai kuwa ɗaukaka ku.
11 O ry longo, ko mifamokafoka. Ty mañìnje Hake naho mizaka Hake ro mañìnje rahalahy Vaho mizaka longo; Aa kanao maniñe Hake irehe, le tsy mpañambeñe Hake, fa mpizaka.
’Yan’uwa, kada ku ɓata wa juna suna. Duk wanda ya zargi ɗan’uwansa ko ya ɗora masa laifi, yana gāba da doka ne yana kuma yin mata shari’a ke nan. In kuwa ka ɗora wa shari’a laifi, kai ba mai binta ba ne, mai ɗora mata laifi ne.
12 Raike t’i Mpanolotse Hake, Ie ty maharombake naho maharotsake. Ia v’iheo te hizaka ondaty?
Akwai Mai ba da doka da kuma Alƙali guda ɗaya tak, shi ne yake da ikon ceto da kuma hallakarwa. Amma kai, wane ne da za ka hukunta maƙwabcinka?
13 Hete! ie manao ty hoe: Ke anito, he hamaray, le hionjoñe mb’an-drova an-koe añe zahay, ho tambatse añe taoñe raike hanao takinake vaho hanontom-bara.
Yanzu fa sai ku saurara, ku da kuke cewa, “Yau ko gobe za mu je wannan ko wancan birni, mu yi shekara a can, mu yi kasuwanci, mu ci riba.”
14 Fe tsy apota’ areo te inoñe ty ho fiai’ areo te hamaray, ie toe zono miboak’ aniany vaho mimiañ’ añe.
Alhali kuwa ba ku ma san abin da zai faru gobe ba. Wane iri ne ranku? Ku kamar hazo ne da yake bayyana na ɗan lokaci sa’an nan yă ɓace.
15 Fe hàmake te hanoe’o ty hoe: Naho satri’ i Talè, te ho velon-jahay le hanao zao naho zao.
A maimakon haka, ya kamata ku ce, “In Ubangiji ya yarda, muna kuma a raye, za mu yi wannan ko wancan.”
16 F’ie miroharoha am-pirengevohañe henaneo, toe raty o fisengeañeo.
Ga shi, kuna fariya da taƙama. Duk irin wannan taƙama mugun abu ne.
17 Le aman-kakeo ze mahafohiñe ty soa hanoe’e fe tsy anoe’e.
Saboda haka, duk wanda ya san abu mai kyan da ya kamata yă yi, bai kuwa yi ba, ya yi zunubi ke nan.