< Isaia 38 >
1 Ie amy andro rezay, natindry fa heta’e t’Iekizkia; le nimb’ama’e mb’eo t’Iesaià ana’ i Amotse, nanao ty hoe: Hoe t’Iehovà: Hajario ty anjomba’o fa toe hivetrake, tsy ho veloñe.
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
2 Nampitolihe’ Iekizkia mb’ an-drindriñe ty lahara’e vaho nihalaly am’ Iehovà,
Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
3 ty hoe: Mihalaly ama’o, ry Iehovà, tiahio henaneo ty fandenàko añatrefa’o an-kavantañañe naho an-kaliforan-troke, vaho nanao ze mahity am-pahaoniña’o; aa ie nangololoike ty rovetse,
“Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 nivotrak’ am’ Iesaià ty tsara’ Iehovà nanao ty hoe:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
5 Akia saontsio am’ Iekizkia ty hoe: Hoe t’Iehovà, Andrianañaharen-drae’o Davide. Fa jinanjiko i halali’oy, nitreako o ranom-pihaino’oo; ingo ho tovoñako taoñe folo lim’ amby o andro’oo.
“Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
6 Ho hahako am-pitàm-panjaka’ i Asore irehe naho ty rova toy vaho harovako ty rova toy;
Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
7 le zao ty ho viloñe ama’o boak’am’ Iehovà, te ho henefa’ Iehovà i raha tsinara’ey:
“‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
8 Heheke te hampibaliheko soritse folo amo soritse fa nilia’eo ty talinjom-panondro-andro’ i Akhaze. Aa le nibalik’ amy soritse folo fa nomba’ey i àndroy.
Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
9 Inao ty sinoki’ Iekizkia mpanjaka’ Iehodà, t’ie natindry an-tihy vaho nijangañe amy arete’ey.
Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
10 Hoe iraho: Ami’ty tsipinde-mena’ o androkoo ty ijoñako an-dalambein-tsikeokeoke eo; kinalañ’ amako o andro tsy nirikoo. (Sheol )
Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
11 Hoe iraho: tsy ho treako t’Ià, Eka, Ià an-tane’ o veloñeo; tsy ho isako ka t’indaty mindre amo mpimone’ ty tane toio.
Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
12 Nombotañe vaho nasitake amako hoe kibohom-piarak’ añondry ty kijàko; nahoronkoroñe hoe te asam-panenoñe ty fiaiko: tinampa’e amy tenoñey iraho, handro an-kaleñe ty hamongora’o ty fiaiko.
Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
13 Nifeahako pak’ami’ty maraiñe, manahake ty liona, fe mbe nipozapozake iaby o taolakoo, añivo ty handro naho ty haleñe ty nampigadoña’o ahy.
Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
14 Mikora hoe tivoke naho aliotse iraho; mikò hoe deho; nimokore’ ty fiandrandràko o masokoo. O ry Iehovà, voatindry iraho, Ihe abey ro tsoako.
Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
15 Ino ty ho volañeko? Nametse amako re mbore nanoe’e; hiezañe amo hene androkoo iraho, ami’ty hafairam-piaiko.
Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
16 O Talè, irezay o mahajangañe ondatio, mampanintsiñe ty troko irehe; vaho mameloñ’ ahy.
Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
17 Tsy nanjo fañanintsin-draho te mone haaferon’ aiko; fe o fikokoa’o ahikoo ro nañaha’o ahy amy kobon-kamodoañey; vaho fonga nahifi’o amboho’o ao o hakeokoo.
Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
18 Tsy mahafandrenge Azo ty tsikeokeoke, tsy hañonjoñe azo ty havilasy; tsy mahafitamà ty figahiña’o ty migodañe mb’an-koak’ ao. (Sheol )
Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
19 O veloñeo, o veloñeo, ie ro mandrenge Azoo, manahake ty anoeko henaneo; ampandrendrehen-drae amo keleia’eo ty figahiña’o.
Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
20 Handrombak’ ahy t’Iehovà; le hititiha’ay ami’ty marovany añ’anjomba’ Iehovà ao o sabokoo, amo hene andro hiveloma’aio.
Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
21 Fa hoe ty natao’ Iesaià: Ampangalao garaton-tsakoa hapakotse amy honay himeara’e.
Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
22 Nanao ty hoe ka t’Iekizkia: Ino ty viloñe hampionjoñ’ ahy mb’ añ’ anjomba’ Iehovà mb’eo?
Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”