< Isaia 36 >
1 Aa ie amy taom-paha folo-efats-ambi’ Iekizkia mpanjakay le naname ze hene rova’ Iehodà nihafatrareñe t’i Senakeribe mpanjaka’ i Asore vaho tinava’e.
A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin Sarki Hezekiya, Sennakerib sarkin Assuriya ya kai wa dukan birane masu kagaran Yahuda yaƙi ya kuma kame su.
2 Nirahe’ i mpanjaka’ i Asorey boake Lakise mb’am’ Iekizkia e Ierosalaime ao t’i Rabsakè reketse lian-dahin-defo ra’elahy, le nijohañe an-talaha-drano miboak’ amy antara amboney, amy lalan-tetem-panasa-lambay ey.
Sai sarkin Assuriya ya aiki sarkin yaƙinsa tare da mayaƙa masu yawa daga Lakish zuwa wurin Sarki Hezekiya a Urushalima. Sa’ad da sarkin yaƙi ya tsaya a wuriyar Tafkin Tudu, a hanya zuwa Filin Mai Wanki,
3 Niavotse mb’ama’e mb’eo t’i Eliakime, ana’ i Hilkià, mpifelek’ i anjombay naho i Sebna mpanokitse vaho Ioake ana’ i Asafe, mpamolily.
Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka fita zuwa wurinsa.
4 Hoe t’i Rabsakè tam’ iereo, Volaño henaneo am’ Iekizkia: Hoe ty saontsi’ i mpanjaka ra’elahiy, i mpanjaka’ i Asorey. Ajado’ areo ami’ty inom-bao ze o fatokisa’ areo zao?
Sai sarkin yaƙin ya ce musu, “Ku faɗa wa Hezekiya. “‘Ga abin da babban sarki, sarkin Assuriya, ya faɗa. A kan me kake dangana wannan ƙarfin halinka?
5 Hoe iraho: fivolan-kòake hao ty atao safiry naho ozatse hahafialy? Aa le ia ty iatoa’ areo, kanao miola amako?
Ka ce kana da dabara da kuma ƙarfin mayaƙa, amma kana magana banza ce kawai. Ga wa ka dogara, da kake tayar mini?
6 Hehe te iatoa’ areo i fitoñom-bararata vinonotrobokey, i Mitsraime; ie itoñona’ ondaty am-pitàñe le trofake: izay t’i Parò mpanjaka’ i Mitsraime amy ze hene miato ama’e.
Yanzu duba, kana dogara ga Masar, wannan ɗan tsinken kyauron dogarawa, wanda zai soki hannun mutum yă kuma ji masa rauni in ya dangana a kansa! Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga duk wanda ya dogara da shi.
7 Aa naho manao ty hoe amako nahareo: Iehovà iatoa’ay t’i Andrianañahare’ay. Aa tsy ie hao ty nañafaha’ Iekizkia o toe’e ankaboañeo naho o kitreli’eo vaho nanao ty hoe am’ Iehodà naho Ierosalaime te amy ze o kitrely zao ty italahoa’ areo?
Kuma in ka ce mini, “Mun dogara ga Ubangiji Allahnmu ne” ba shi ba ne Hezekiya ya rurrushe masujadan kan tudunsa da bagadansa, yana ce wa Yahuda da Urushalima, “Dole ku yi sujada wa gaban wannan bagade”?
8 Aa ehe manoa kizè amy taleko mpanjaka’ i Asorey, le hatoloko azo ty soavala ro’arivo, naho mete’o ty hampijoñe mpiningitse ama’e.
“‘Yanzu fa, bari in yi ciniki da maigidana, sarki Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sa mahaya a kansu!
9 Akore arè ty hampiambohoa’o ty mpifehe, faragidro’ o mpitoron-talèkoo? te hapite’o amy Mitsraime ty fiatoa’o hahazoa’o sarete naho mpiningitse!
Yaya za ka ƙi hafsan mafi ƙanƙanci na hafsoshin maigidana, ko da yake kana dogara ga Masar don kekunan yaƙi da mahayan dawakai?
10 Aa vaho nionjoñe mb’an-tane atoy hao iraho handrotsak’ aze tsy ama’ Iehovà? Toe nanao ty hoe amako t’Iehovà: Mionjona haname o tane zao le rotsaho.
Ban da haka kuma, na zo ne in faɗa in kuma hallaka wannan ƙasa ba tare da Ubangiji ba? Ubangiji kansa ya faɗa mini in tasar wa wannan ƙasa in kuma hallaka ta.’”
11 Aa le hoe t’i Eliakime, i Sebnà, naho Ioàke amy Rabsakè, Ehe, misaontsia amo mpitoro’oo an-tsaontsi’ i Arame, fa hai’ay; le ko misaontsy ama’ay an-tsaontsi’ Iehodà, am-pijanjiña’ ondaty ambone’ o kijolioo.
Sai Eliyakim, Shebna da Yowa suka ce wa sarkin yaƙin, “Ka yi haƙuri ka yi wa bayinka magana da Arameyanci, da yake muna jinsa. Kada ka yi mana magana da Yahudanci a kunnen mutanen da suke kan katanga.”
12 Fa hoe t’i Rabsakè: Aa vaho nirahe’ i talèkoy iraho hivolañe amy tale’ areoy naho ama’ areo avao o entako zao, le tsy am’ ondaty mitoboke ambone’ o kijolioo, o nozoñeñe hitraoke ama’ o hikama ty fiamonto’e naho hinoñe ty rano faria’eo?
Amma sarkin yaƙin ya amsa ya ce, “Kuna tsammani ga maigidanku da ku ne kawai maigidana ya aiko ni in yi waɗannan maganganu, ba ga mutanen da suke zama a kan katanga ba, waɗanda kamar ku, za su ci kashinsu su kuma sha fitsarinsu?”
13 Aa le niongake t’i Rabsakè vaho pinaza’e ty koike, ami’ty saontsi’ Iehodà ty hoe: Janjiño ty saontsi’ i mpanjaka ra’ elahiy, ty mpanjaka’ i Asore!
Sa’an nan sarkin yaƙin ya tsaya ya kuma yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji kalmomin babban sarki, sarkin Assuriya!
14 Hoe i mpanjakay, Ko apo’ areo ho fañahie’ Iekizkia, fa tsy ho lefe’e rombaheñe.
Ga abin da sarki ya ce kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku. Ba zai cece ku ba!
15 Ko ado’ areo hampiatoa’ Iekizkia am’ Iehovà ami’ty hoe: Toe hamotsotse an-tika t’Iehovà, le tsy hatolotse am-pità’ i mpanjaka’ i Asorey ty rova toy.
Kada ku bar Hezekiya ya rarashe ku ku dogara ga Ubangiji sa’ad da ya ce, ‘Tabbatacce Ubangiji zai cece mu; ba za a ba da wannan birni a hannun sarkin Assuriya ba.’
16 Ko haoñe’ areo t’Iekizkia; fa hoe ty mpanjaka’ i Asore, mifampilongoa amako le miavota mb’etoy; fa songa hikama ami’ty vahe’e t’indaty, naho sindre ami’ty sakoa’e t’indaty vaho hene hinon-drano boak’ an-tsajoa’e t’indaty,
“Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya faɗa. Ku nemi salama da ni ku kuma fito zuwa wurina. Ta haka kowa zai ci daga kuringarsa da kuma itacen ɓaurensa ya kuma sha ruwa daga tankinsa,
17 ampara’ te homb’eo iraho hanese anahareo mb’an-tane manahake ty tane’ areo, tanen-ampemba naho divay, tane ama mahakama naho tanem-bahe.
sai na zo na kuma kwashe ku zuwa ƙasa kamar taku, ƙasar hatsi da kuma sabon ruwan inabi, ƙasar abinci da gonakin inabi.
18 Ko apo’ areo hampivihe’ Iekizkia ami’ ty hoe: Handrombake antika t’Iehovà. Fa ia amo ‘ndrahare’ o kilakila’ ndatio ty nandrombake ty tane’e am-pità’ i mpanjaka’ i Asorey?
“Kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’ Allahn wata al’umma ya taɓa ceci ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
19 Aia o ndrahare’ i Kamate naho i Arpadeo? Aia o ndrahare’ i Sefarvaimeo? Fa navotso’ iareo an-tañako hao t’i Somerone?
Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim? Sun fanshi Samariya daga hannuna?
20 Ia amo ndrahare’ i tane rey iabio ty nañaha aze an-tañako, te havotso’ Iehovà an-tañako t’Ierosalaime?
Wanne cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa daga gare ni? Yaya kuwa Ubangiji zai iya ceci Urushalima daga hannuna?”
21 Fe nianjiñe avao iereo, leo volañe raike tsy natoi’ iareo aze, amy linili’ i mpanjakaiy, ty hoe: Ko itoiñañe.
Amma mutanen suka yi shiru ba su kuwa ce kome ba, gama sarki ya yi umarni cewa, “Kada ku amsa masa.”
22 Nomb’ am’ Iekizkia t’i Eliakime ana’ i Kilkeia mpifeleke i anjombay naho i Sebnà mpanokitse naho Ioàke ana’ i Asafe mpamolily, an-tsaroñe riatse, vaho nitaroñe i enta’ i Rabsakèy.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, Shebna magatakarda, da kuma Yowa ɗan Asaf marubuci suka tafi wurin Hezekiya, da rigunansu a kyakkece, suka kuwa faɗa masa abin da sarkin yaƙin ya yi ta farfaɗa.