< Isaia 25 >
1 Ry Iehovà, Andrianañahareko irehe, hañonjoñ’Azo iraho, ho bangoeko ty tahina’o, ty amo fitoloña’o fanjàkao; ihe nisafiry haehae am-pigahiñañe naho an-katò.
Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
2 Fa nanoe’o votre ty rova, naho fianto i rova fatra-piaroy; tsy rova ka i anjomban’ ambahiniy, vaho tsy hamboareñe ka.
Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
3 Aa le hañonjoñe Azo ondaty manjofakeo, hañeveñe ama’o o rovam-pifeheañe mitromoroñeo.
Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
4 Fa nifipalira’ o rarakeo irehe, fitsoloha’ o misotrio, fiampirañe an-tio bey, fialofañe amy hatrovohañey; naho hoe tio-bey an-kijoly ty fikofoha’ o maharevendreveñeo.
Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
5 Manahake ty hatrevohañe an-tane maike eo, ty hampitsiña’o ty fikoraha’ o ambahinio; hambañe ami’ty talinjon-drahoñe amy fipisañañey, ty hampijomohoñe ty fibekoa’ o mangosasàkeo.
kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
6 Ami’ty vohitse toy ty hañalankaña’ Iehovà’ i Màroy sabadidake amo raha mafirio ze kila ondaty, takataka aman-divay natadrètse, ty vondrake pea’ ty betron-taolañe, vaho divay soa-filomboke.
A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
7 Le hagedra’e ami’ty vohitse toy ty fikolopofañe ami’ty vinta’ ze kila-ondaty naho ty marerarera mandrongoñe o fifeheañeo.
A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
8 Hatele’e ho mongotse ty havilasy, vaho ho faohe’ i Rañandria Iehovà amy ze hene laharañe ty ranompihaino; hafaha’e ami’ty tane toy ty sirika’ondati’eo; izay ty nitsarà’ Iehovà.
zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
9 Ho tseizeñe amy andro zay, ty hoe: Toe Ie t’i Andrianañaharentika nitamañe handrombake an-tikañey, Ie Iehovà niliñisan-tikañey, antao hifale naho hirebeke amy fandrombaha’ey.
A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
10 Fa ami’ty vohitse toy ty hitofà’ ty fità’ Iehovà, vaho ho lialiàñe an-toe’e eo t’i Moabe, hambañe ami’ty fandialiàñe ty ahetse an-ditsake ao.
Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
11 Le ho velare’e añivo’iareo o fità’eo, manahake ty famelara’ ty pilaño hilañoa’e, fe harèke ty firengevoha’e rekets’ o taña-politì’eo
Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
12 naho harotsa’e ambane o kijoli’o fatratse mitiotiotseo, eka, halama’e; hazevo’e an-tane, toe an-deboke ao.
Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.