< Isaia 14 >

1 Aa ie tretreze’ Iehovà t’Iakobe, naho joboñe’e t’Israele, vaho hampimoneñe’e an-tane’ iareo eo; le hirekets’ am’ iereo ty renetane, hipitek’ amy anjomba’ Iakobey.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 Ho rambese’ o kilakila’ ndatio naho hasese’iareo mb’an-toe’ iareo mb’eo; ie ho fanaña’ i anjomba’ Israeley ho mpitoroñe lahy naho ampela an-tane’ Iehovà ao; naho ho tsepahe’iareo o namahotse iareoo; vaho ho fehè’ iareo ­ o namorekeke iareoo.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 Ho tendreke amy andro hampanintsiña’ Iehovà anahareo amo fioremeña’ areoo, naho amo haorea’ areoo, naho amo fitromahañe namorekekeañe anahareoo,
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 t’ie ho ente’ areo amy mpanjaka’ i Baveley añe ty tafatoño toy, ami’ty hoe: akore te nijihetse i mpamorekekey! naho nipendreñe i fidabadoañey!
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 Fa pinoza’ Iehovà ty fitoño’ o lo-tserekeo, ty kobai’ o mpifeheo,
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 I nitolom-pamofoke ondatio ami’ty haboseha’ey, i nameleke ondatio ami’ty haviñera’e an-tsarerake tsy nimete kalañeñey.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 Manintsiñe iaby ty tane toy, vaho mitsiñe; ie ampipoñafan-tsabo.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Eka mirebeke ty ama’o o sohihio, naho o mendorave’ i Lebanoneo: Kanao nazevoñ’ ambane irehe, tsy mitroatse ama’ay ty mpamira.
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 Mangetseketseke ty ama’o ty tsikeokeoke hifanalaka ama’o amy figodaña’oy; ampibarakaofe’e ty ama’o o angatseo, o nifeleke tan-tane atoio; songa miongake amo fiambesa’eo o mpanjakam-pifeheañeo. (Sheol h7585)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
10 Songa mifañontane ama’e manao ty hoe: Toe maleme manahake anay irehe! Ihe hambañe ama’ay!
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Fa nampanjotso azo mb’an-kibory mb’atoy ty firegevoha’o, reketse ty fikoraha’ o karara’oo; Nalamake ambane’o ao o oletseo, vaho mañohoñe azo o kànkañeo. (Sheol h7585)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
12 Akore ty nideboña’o boak’ andikerañey, ry vasian-kandro, ana’ ty fanjirik’andro! Finira mb’an-tane, ihe nimpamotsake o fifeheañeo.
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 Nanoe’o an-tro’o ao ty hoe: Hionjoñe mb’andikerañe mb’eo iraho, ambone’ o vasian’ Añahareo ty hañonjonako ty fiambesako, vaho hiambesatse am-bohim-pivory eo, amo ila’e avaratseo;
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 Hionjoñe ambonen-dikera’ o rahoñeo iraho, hihambañako amy Abo-Tia.
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 Te mone hazotso mb’an-tsikeokeoke ao irehe, pak’am-para’ i halale’ i koboñeiy. (Sheol h7585)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
16 Hisamb’ azo o hahaisake azoo, hañarahara ty hoe: Itiañe hao indaty nampiezeñezeñe ty tane toiy, i ­nampihondrahondra o fifeheañeoy;
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 Ty nanao ty tane toy ho ratraratra, naho nandrotsake o rova’eo; vaho tsy nanokake ty vala-bei’e himpolia’ o narohi’eo?
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 Songa mirotse ami’ty enge’e o mpanjaka’ o fifeheañeoo, ie iabikey, sindre an-kibori’e ao.
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 F’ihe ka, ro navokovoko boak’ an-kibori’o ao hoe tsampañe tiva, an-tsaro’ ty vinono, tinomboke fibara, mihotrake mb’amo vato an-koboñeo hoe lolo linialiam-pandia.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 Tsy hitrao-pileveñe am’ iereo, amy te narotsa’o ty tane’o vaho zinama’o ondati’oo; toe tsy ho tiahieñe ka ty tarira’ o lo-tserekeo.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Mihentseña hanjamañe o ana’eo ty amo hakeon-droae’ iareoo; tsy mone hitroatse hitavañe ty voatse toy iereo, hanitsike o rova an-tane atoio.
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 Izaho, hoe t’Iehovà’ i Màroy, ty hitroatse am’ iereo, vaho haitoako amy Bavele ty añarañe naho ty sehanga’e, ty tariratse naho ty tamingañe, hoe t’Iehovà.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 Hatoloko ho fanaña’ ty trandrake, ho babangoa-mangenakenake; le ho piopioheko am-pamafa- karotsahañe, hoe t’Iehovà’ i Màroy.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 Nifanta’ Iehovà’ i Màroy ty hoe: Toe ho tondroke ze fitsakoreako; hijadon-ko do’e ze aereñereko.
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 Ho folaheko an-taneko ao ty Asore, ho lialiàko am-bohiko eo; habalake ty joka’e am’ iareo, vaho havotsotse an-tsoro’ iareo ty kilanka’e.
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 Izay ty safiry nalahatse ho a’ ty tane bey toy vaho itoy ty taña natora-kitsike amo fifeheañe iabio.
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 Naereñere’ Iehovà’ i Màroy, ia ty hahakalañe aze? Napololotse ty fità’e, ia ty hampipoly aze?
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 Tamy taoñe nahavilasy i Akhaze mpanjaka, ty niheova’ ty entañe toy.
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Ko mandia-taroba, ry Pilistý iabio, amy te pinozake ty kobaiñe nandafa azo, fa boak’ am-baha’ ty mereñe ty hitiria’ ty lapetake, ie ka ty hamoa fandrefeala mibela, mitiliñe.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 Hikama o loho rarakeo, naho hàndre am-pipalirañe ao o poi’eo; ho vonoeko ami’ty kerè o vaha’oo, izay ty hanjamanañe ty honka’o.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Mañaoloa ry lalambey, mikoiha ry rova; mitranaha ry Pilistý, nahareo iaby; hehe te boak’ avaratse añe ty hatoeñe, tsy ama’e ty mitakàtrotse am-pirimboña’e.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 Akore arè ty hamaleañe o ira’ i fifeheañeio? T’ie naore’ Iehovà t’i Tsione le hitsoloke ama’e ondati’e misotrio.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”

< Isaia 14 >