< Hosea 5 >

1 Inao, ry mpisoroñeo, mitsendreña ry anjomba’ Israeleo, manokilaña ravembia ry anjomba’ i mpanjakay, fa ama’ areo i zakay; amy t’ie fandrik’ amy Mitspà naho harato nalafike ho amy Tabore;
“Ku ji wannan, ku firistoci! Ku kasa kunne, ku Isra’ilawa! Ku saurara, ya ku gidan sarauta! Wannan hukunci yana a kanku, kun zama tarko a Mizfa, ragar da aka shimfiɗa a kan Tabor.
2 vaho mpiola miheotse t’ie mandenta ndra te nendahako.
’Yan tawaye sun yi zurfi cikin kisan gilla. Zan hore su duka.
3 Fàntako t’i Efraime naho tsy mietak’ amako t’Israele; fa manao hakarapiloan-drehe Efraime, vaho maleotse t’Israele.
Na san Efraim ƙaf; Isra’ila ba a ɓoye take a gare ni ba. Efraim, yanzu ka juya ka shiga karuwanci; Isra’ila ta lalace.
4 Tsy ho safirie’ iareo ty himpoly aman’Añahare’ iareo; fa añivo’ iareo ao ty fañahin-kakarapiloañe, vaho tsy fohi’ iereo t’Iehovà.
“Ayyukansu ba su ba su dama su koma ga Allahnsu ba. Halin karuwanci yana cikin zuciyarsu; ba su yarda da Ubangiji ba.
5 Mitalily an-dahara’e ty fiebotsebora’ Israele; toly ndra hitsikapy an-kakèo t’Israele naho i Efraime; hiharo hihotrak’ am’ iereo ka t’Iehodà.
Girmankan Isra’ila yana ba da shaida a kansu; Isra’ilawa, har ma Efraim, sun yi tuntuɓe a cikin zunubinsu; Yahuda ma ya yi tuntuɓe tare da su.
6 Hendese’ iereo ty lia-rai’ iareo naho o mpirai-tro’ iareoo ho paia’ iereo t’Iehovà, fe tsy ho oniñe, fa nisitake.
Sa’ad da suka tafi tare da garkunan shanu, tumaki da awakinsu don su nemi Ubangiji, ba za su same shi ba; ya janye kansa daga gare su.
7 Fa niola am’ Iehovà iereo, naho nahatoly anak’amontoñe; aa le habotse’ ty pea-bolañe reke-panañañe.
Su marasa aminci ne ga Ubangiji; suna haihuwar shegu. Yanzu bukukkuwar Sabon Watansu za su cinye su da gonakinsu.
8 Tiofo e Gibà i antsivay naho e Ramà i soliy; koiho e Bet’avene ty hankàñe: mitoliha ry Beniamine.
“Amon kakaki a Gibeya, ƙaho a Rama. Ku yi kirarin yaƙi a Bet-Awen; ku ja gaba, ya Benyamin.
9 Ho koaheñe t’i Efraime amy andro fandilovañey; fa nampahafohineko o fifokoa’ Israeleo ze toe hifetsake.
Efraim za tă zama kango a ranar hukunci. A cikin kabilan Isra’ila na yi shelar abin da yake tabbatacce.
10 Manahake ty mpameve vorovoro o roandria’ Iehodào; hadoandoako am’ iereo hoe rano ty habosehako.
Shugabannin Yahuda suna kamar waɗanda suke matsar da duwatsun shaidar da aka sa a kan iyaka ne. Zan zubo musu da fushina a kansu kamar rigyawar ruwa.
11 Forekekèñe t’i Efraime demok’ an-jaka; ie nañorike haloloañe an-tsatri’e.
An danne Efraim, an murƙushe ta a shari’a ta ƙudura ga bin gumaka.
12 Aa le ho bararaok’ amy Efraime iraho, naho haloloañe amy anjomba’ Iehodày.
Na zama kamar asu ga Efraim, kamar ruɓa ga mutanen Yahuda.
13 Ie nahaoniñe i arete’ey t’i Efraime, naho i fere’ey t’Iehodà, le nihitrike mb’ Asorey mb’eo, naho nisangitrife’e i mpanjaka Iaribey; f’ie tsy hahajangañ’ azo, vaho tsy ho melañe’e i fere’oy.
“Sa’ad da Efraim ya ga ciwonsa, Yahuda kuwa miyakunta, sai Efraim ya juya ga Assuriya, ya aika wurin babban sarki don neman taimako. Amma bai iya warkar da kai ba, bai iya warkar da miyakunka ba.
14 Ho liona amy Efraime iraho, naho liona tora’e amy anjomba’ Iehodày; Izaho le Izaho avao ty handrimitse vaho hienga; hinday iraho le ia ty haharombake.
Gama zan zama kamar zaki ga Efraim, kamar babban zaki ga Yahuda. Zan yage su kucu-kucu in tafi; zan kwashe su, ba wanda zai kuɓutar da su.
15 Homb’eo iraho himpoly mb’añ’akibako añe, ampara’ t’ie miantoke o hakeo’eo, naho mipay ty tareheko; ie am-poheke ro hitsoek’ahy.
Sa’an nan zan koma wurina sai sun yarda da laifinsu. Za su kuma nemi fuskata; cikin azabansu za su nace da nemana.”

< Hosea 5 >