< Ezra 8 >
1 Irezao ro mpiaolon-droae naho ty fiantoño’ o nindre amako boak’ am-pifehea’ i Artaksastà mpanjaka, nionjomb’eo boake Baveleo:
Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
2 Tamo ana’ i Pinekaseo: i Gersome; amo ana’ Itamareo, i Daniele; tamo ana’ i Davideo, i Hatose.
Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
3 Tamo ana’ i Sekaniào, amo ana’ i Paroseo, i Zekarià reketse ty zato-tsi-limampolo nivolilieñe ami’ty fiantoño’ o lahilahio.
ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
4 Tamo ana’ i Pakate-moabeo; i Elihoenay ana’ i Zerakià reketse ty lahilahy roanjato.
daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
5 Tamo ana’ i Sekaniào, i Zatò, ana’ Iakaziele, reketse ty lahilahy telonjato.
daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
6 Le tamo ana’ i Adineo, i Ebede ana’ Ionatane, reketse ty lahilahy limampolo.
daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
7 Le tamo ana’ i Elameo, Iesaia ana’ i Atalia, reketse ty lahilahy fitompolo.
daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
8 Le tamo ana’ i Sefatiào, i Zebadià, ana’ i Mikaele, reketse ty lahilahy valompolo.
daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
9 Tamo ana’ Ioabeo, i Obadià, ana’ Iekiele, reketse ty lahilahy roanjato-tsi-folo-valo’ amby.
daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
10 Le tamo ana’ i Banio, i Selomite, ana’ Iosifià, rekets ty lahilahy zato-tsi-enempolo.
daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
11 Le tamo ana’ i Bebaio; i Zekarià, ana’ i Bebay, reketse ty lahilahy roapolo-valo’ amby.
daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
12 Le tamo ana’ i Azgadeo; Iohanane, ana’ i Hakatane, reketse ty lahilahy zato-tsi-folo.
daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
13 Le tamo ana’ i Adonikameo, o tsitso’eo; zao o tahina’eo, i Elifelete, Ieiele naho i Semaià, reketse ty lahilahy enempolo.
zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
14 Le tamo ana’ i Bigvaio, i Otay naho i Zakore, reketse ty lahilahy fitompolo.
daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
15 Le hene natontoko amy saka mivariñe mb’e Ahava mb’eoy; naho nitobe eo telo andro, nisary ondatio naho o mpisoroñeo fe leo raik’ amo nte-Levio tsy nizoeñe ao.
Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
16 Aa le tinokako t’i Eliezere, i Ariele, i Semaià naho i Elnatane naho Iaribe naho i Elnatane naho i Natane naho i Zekarià naho i Mesolame, mpiaolo; naho Ioiaribe vaho i Elnatane, mpañoke.
Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
17 Le nafantoko am’iareo ty homb’ amy Ido mpiaolo mb’an-toetse atao Kasifia naho vinolako am’iereo ty ho asa’ iareo amy Ido naho amo rahalahi’e mitoroñe an-toe’ i Kasifiao, ty hinday mpitoroñe mb’amy anjomban’ Añaharey.
Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
18 Aa ty am-pitàn-tsoan’ Añahare’ay ama’ay le nandesa’ iareo ondaty mahihitse, ty ana’ i Maklý, ana’ i Levy, ana’ Israele, toe i Serebià rekets’ o ana’eo naho o rahalahi’eo, folo-valo’ amby;
Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
19 naho i Kasabià; le nindre ama’e t’Iesaià tamo ana’ i Merario, o rahalahy naho ana-dahi’ iareoo, roapolo;
Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
20 vaho tamo nte-Natoneo, o natolo’ i Davide naho o roandriañeo am-pitoroñañe o nte-Levio; nte-Natone roan-jato-tsi-roapolo songa tinoñoñe amy tahina’ey.
Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
21 Aa le nitsey fililiran-draho an-tsaka Ahavà eo, hiambanea’ay añatrefan’ Añahare’ay, hipay ama’e ty lalan-tsoa ho anay naho o keleia’aio vaho o vara’ay iabio.
A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
22 Fa ho nisalatse iraho te nihalaly firimboñan-dahindefoñe naho mpiningi-tsoavala amy mpanjakay, hañolora’e anay amo malaso an-dalañeo; ie fa nisaontsy amy mpanjakay, ty hoe: Ty fitàn’ Añahare’ay ro amo mipay aze iabio ho an-kasoa; fe atreatré’e an-kaozarañe naho an-kaviñerañe o mamorintseñe azeo.
Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
23 Aa le ie ty nililira’ay te nitsoek’ an’ Andrianañahare’ay; vaho vinale’e i halali’aiy.
Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
24 Aa le navìko ty mpiaolom-pisoroñe folo-ro’amby—i Serebià naho i Kasabià vaho ty folo amo longo’ iareoo.
Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
25 Le linanjako am’ iereo i volafotiy naho i volamenay naho o fanakeo, i nengae’ i mpanjakay naho o mpanolo-keve’eo naho o roandria’eo naho o nte-Israele teo iabio, amy anjomban’ Añahare’aiy.
Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
26 Eka, linanjako am-pità’ iareo ty volafoty talenta enen-jato-tsi-limampolo naho ty fanake volafoty talenta zato naho ty volamena talenta zato;
Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
27 naho koveta volamena roapolo, vilin-drala arivo; naho fanake roe an-torisike mikinokinoke, mañeva volamena.
kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
28 Le hoe ty asako am’ iereo, Miavake ho amy Iehovà nahareo, miavake ka o fanakeo; vaho nengaeñe an-tsatrin’ arofo am’ Iehovà Andrianañaharen-droae’ areo i volafotiy naho i volamenay.
Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
29 Ijilovo naho ambeno ampara’ t’ie lanjae’ areo amo mpiaolom-pisoroñeo naho amo nte-Levio naho amo roandrian’ anjomban-droae’ Israeleo e Ierosalaime añ’efen’ anjomba’ Iehovà ao.
Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
30 Aa le rinambe’ i mpisoroñe naho nte-Levy rey i volafoty naho volamena linanjay naho o fanakeo hendesa’ iareo mb’e Ierosalaime añe mb’añ’ anjomban’ Añahare’ay mb’eo.
Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
31 Aa le nienga i saka Ahavay zahay amy andro faha folo-ro’ambi’ i volam-baloha’eiy nionjone mb’e Ierosalaime mb’eo; naho tama’ay ty fitàn’Añahare’ay vaho rinomba’e am-pitàn-drafelahi’ay naho amy ze niampitse an-dalañe,
A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
32 le nivotrake e Ierosalaime ao vaho nitofa telo andro.
Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
33 Ie amy andro fahefatsey le nandanja i volafotiy naho i volamenay naho o fanakeo, añ’anjomban’ Añahare’ay am-pità’ i Meremote, ana’ i Orià mpisoroñe; nindre tama’e t’i Elazare, ana’ i Pinekase; le nimpiama’ iareo t’Iozabade ana’ Iesoà naho i Noadià, ana’ i Binoy, songa nte-Levy;
A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
34 ie iaby ami’ty ia’e naho an-danja’e; le sinokitse henane zay iaby i lanja’ey.
Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
35 Nañenga soroñe aman’ Añahare’ Israele o anam-pandrohizañe niboak’ am-paneseañeo, bania folo-ro’amby ho a Israele iaby, añondrilahy sivampolo-eneñ’ amby, vik’añondry fitompolo-fito’ amby vaho oselahy folo-ro’amby ho engan-kakeo; hene nisoroñañe am’ Iehovà.
Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
36 Le natolo’ iareo amo mpizaka’ i mpanjakaio naho amo mpifehe alafe’ i Sakaio i nampañitrifañey, vaho nimbae’ iereo ondatio naho i anjomban’ Añaharey.
Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.