< Ezra 7 >
1 Ie añe, le teo tam-pifehea’ i Artaksastà, mpanjaka’ i Parasey, t’i Ezrà, ana’ i Seraià, ana’ i Azarià, ana’ i Hilkià,
Bayan waɗannan abubuwa, a zamanin Artazerzes sarkin Farisa, sai Ezra ɗan Serahiya, ɗan Azariya, ɗan Hilkiya,
2 ana’ i Salome, ana’ i Tsadoke, ana’ i Akitobe,
ɗan Shallum, ɗan Zadok, ɗan Ahitub,
3 ana’ i Amarià, ana’ i Azarià, ana’ i Meraiote,
ɗan Amariya, ɗan Azariya, ɗan Merahiyot,
4 ana’ i Zerakià, ana’ i Ozý, ana’ i Boký,
ɗan Zerahiya, ɗan Uzzi, ɗan Bukki,
5 ana’ i Abisoà, ana’ i Pinekase, ana’ i Elazare, ana’ i Aharone, mpisorom-bey;
ɗan Abishuwa, ɗan Finehas, ɗan Eleyazar, ɗan Haruna babban firist.
6 nionjoñe boake Bavele añe i Ezrà zay, ie mpanokitse mahimbañe amy Tsara’ i Mosè natolo’ Iehovà Andrianañahare’ Israele azey; vaho hene nitolora’ i mpanjakay ze nihalalia’e amy te tama’e ty fità’ Iehovà Andrianañahare’e.
Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
7 Nionjomb’e Ierosalaime mb’eo ty ila’ o ana’ Israeleo naho o mpisoroñeo naho o nte-Levio naho o mpisaboo naho o mpañambeñeo naho o Natolotseo an-taom-paha-fito’ i Artaksastà,
Waɗansu Isra’ilawa, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali su ma suka zo Urushalima a shekara ta bakwai a zamanin mulkin sarki Artazerzes.
8 le nivotrake e Ierosalaime ao amy volam-paha-lime’ i taom-paha-fito’ i mpanjakaiy,
Ezra ya iso Urushalima a wata na biyar na shekara ta bakwai na kama mulkin sarkin.
9 ie namototse amy andro valoha’ i volam-baloha’ey ty fionjona’e boake Bavele añe le nitotsake e Ierosalaime ao amy andro valoham-bolam-paha-limey ty amy fitàn-tsoan’ Añahare ama’ey.
Ya fara tafiyarsa daga Babilon a rana ta farko ga watan farko, ya kuma iso Urushalima a rana ta farko ga watan biyar, gama alherin Allahnsa yana tare da shi.
10 Fa nihentseña’ i Ezra añ’ arofo’e ao ty hitsoeke i Tsara’ Iehovà naho ty hañorik’ aze naho ty hañòha’e e Israele ao o fañè naho fepè’eo.
Gama Ezra ya miƙa kansa ga bincike da kuma kiyaye Dokar Ubangiji, da kuma koya wa Isra’ilawa dokoki da kuma umarnan Ubangiji.
11 Le zao ty dika-hamban-taratasy natolo’ i Artaksastà mpanjaka amy Ezra mpisoroñe, mpanokitse, toe nanokitse ty tsara’ o lili’ Iehovào naho fañè’eo ho a Israeley:
Ga wasiƙar da sarki Artazerzes ya ba Ezra wanda yake firist da kuma malami, mutumin da yake cike da sani game da dokoki da kuma umarnan Ubangiji wa Isra’ila.
12 Artaksastà mpanjakam-panjaka, amy Ezra mpisoroñe, mpanoki-dilin’ Añaharen-dindiñey, fañanintsiñe. Ie henaneo
Artazerzes, sarkin sarakuna. Zuwa ga Ezra firist, malamin Dokar Allah na sama. Gaisuwa.
13 mikoi-dava iraho te ze nte-Israele naho o mpisoro’eo miharo amo nte-Levy am-pifeheako atoio, ze mañiriñe an-tsatrin’ arofo’e ty hindre lia ama’o mb’e Ierosalaime mb’eo, le mionjona.
Yanzu ina ba da umarni cewa duk wani mutumin Isra’ilan da yake cikin mulkina, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da suke so su tafi tare da kai zuwa Urushalima za su iya tafiya.
14 Amy te nirahe’ i mpanjakay naho i mpanolo-keve’e fito rey ama’o, hañontane Iehoda naho Ierosalaime ty amy lilin’ Añahare’o am-pità’oy;
Sarki ne da mashawartansa guda bakwai suka aike ka don ka je ka ga halin da Yahuda da Urushalima suke ciki game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka.
15 naho ty hinday ty volamena naho volafoty natolo’ i mpanjakay naho i mpanolo-keve’e rey an-tsatrin’ arofo mb’ aman’ Añahare’ Israele, mpimoneñe e Ierosalaime ao
Za ka kuma tafi da zinariya da azurfa waɗanda sarki da mashawartansa suka ba da kyautar yardar rai ga Allah na Isra’ila, wanda haikalinsa ke a Urushalima,
16 naho ze hene volafoty naho volamena ho zoe’o am-pifehea’ i Bavele ao, reketse ty engan-tsatrin’ arofo’ ondatio naho o mpisoroñeo, ie songa manolotse an-tsatri’e añ’ anjomban’ Añahare’e e Ierosalaime ao;
haɗe da duk zinariya da azurfan da za ka iya samu a Babilon, da kuma duk bayarwar yardar rai daga mutane da firistoci, domin haikalin Allahnsu da yake a Urushalima.
17 aa le ho vilie’o an-kahimbañañe amy volay o baniao, o añondrilahio, o vik’añondrio, mindre amo enga-mahakama’eo naho o enga-rano’eo ie hisoroña’o amy kitrelin’ Anjomban’ Añahare’ areo e Ierosalaimey.
Ka tabbata ka yi amfani da kuɗin nan don ka sayi bijimai, da raguna, da’yan raguna, da hadayu na gari, da na sha, ka kuma miƙa su a kan bagade na haikalin Allahnka a Urushalima.
18 Le ze atao’o naho o rahalahi’o ho soa anoeñe ami’ty sisa’ i volafoty naho volamenay; le ano ty amy satrin’ arofon’ Añahare’ areo.
Sa’an nan kai da’yan’uwanka Yahudawa ku yi abin da kuka ga ya fi kyau da sauran zinariya da azurfa ɗin bisa ga nufin Allah.
19 Natolotse azo ho amy fitoroñañe i anjomban’ Añahare’oy ka o fanakeo, aseseo añatrefan’ Añahare’ Ierosalaime ao.
Ka kai wa Allah na Urushalima duk kayan da aka ba ka amanarsu don yin sujada a haikalin Allahnka.
20 Aa ze tovo’e ho paiañe amy anjomban’ Añahare’oy, ze oni’o te azo tolorañe, le itoloro boak’ an-trañom-panontonam-baram-panjaka ao.
Duk kuma wani abin da ake bukata domin haikalin Allahnka, daga ɗakunan ajiya sarki za ka fitar da kuɗin.
21 Le izaho, eka izaho Artaksastà mpanjaka, ty mitsey amy ze hene mpamandrom-bara alafe’ i Sakay añe, te ze paia’ i Ezrà mpisoroñe, mpanoki-dilin’ Añaharen-dindiñey ama’ areo, le hanoeñe an-kahimbañañe,
Yanzu fa ni, Sarki Artazerzes, ina ba da umarni ga kowane ma’aji na Kewayen Kogin Yuferites su tanada duk abin da Ezra firist, wanda kuma yake malamin Dokar Allah na sama zai bukaci,
22 pak’ ami’ ty volafoty zato talenta naho ty vare-bolè zato kore naho ty divay zato bate naho ty menake zato bate vaho ty sira tsy amañ-iake.
har zuwa talenti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari na ruwan inabi, da garwa ɗari na man zaitun, da kuma gishiri ba iyaka.
23 Ze lilie’ i Andrianañaharen-dikerañey, le ano am-pilozohañe amy anjomban’ Añaharen-dindiñey, soa tsy ho an-kaviñerañe ty fifehea’ i mpanjakay naho o ana’eo.
A yi duk abin da Allah na sama ya ce don haikalin Allah na sama, sai a yi shi da himma. Me zai sa a jawo wa sarki da’ya’yansa fushin Allah?
24 Le afantok’ ama’ areo ty amo mpisoroñeo naho o nte-Levio, o mpisaboo, o mpañambeñeo, o mpitoroñeo naho o mpitoloñ’ añ’ anjomban’ Añahareo, te faly ty ipaiañe rorotse, ndra fondro ndra haba.
Ku kuma san cewa, ba ku da ikon sa firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofin haikali, da masu aiki a gidan Allah, ko waɗansu masu aiki a haikali su biya haraji, ko kuɗin shiga.
25 Aa Ihe Ezrà, ty amy hihin’ Añahare’o am-pità’oy, le ampijadoño mpandily naho mpizaka, hahafizaka ondaty alafe’ i sakay añe iabio, ze hene mahafohiñe o lilin’ Añahare’oo; le anaro ze mboe tsy mahafohiñe.
Kai kuma Ezra, bisa ga hikimar da Allah ya ba ka, sai ka zaɓi mahukunta da alƙalai waɗanda za su zama masu yanke hukunci ga dukan mutanen Kewayen Kogin Yuferites, duk waɗanda suka san dokokin Allahnka, ka kuma koya wa duk waɗanda ba su san dokokin ba.
26 Le ze tsy mete mañorike o lilin’ Añahare’oo naho ty lilim-panjaka, le afetsaho ama’e aniany ty zaka, ke t’ie havetrake, he hasese, hera hañafahañe vara, ke harohy.
Ba shakka duk wanda bai yi biyayya da dokokin Allahnka ba, da kuma dokokin sarki ba dole a yanke masa hukuncin kisa, ko hukuncin kora, ko hukuncin raba shi da mallakarsa, ko kuma hukuncin kulle shi a kurkuku.
27 Andriañeñe t’Iehovà Andrianañaharen-droaentikañe, te najo’e añ’arofo’ i mpanjakay, hampisomontie’e ty anjomba’ Iehovà e Ierosalaime ao;
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na kakanninmu, ya taɓa zuciyar sarki don yă kawo ɗaukaka ga haikalin Allah a Urushalima ta wannan hanya.
28 vaho nañitrike fiferenaiñañe amako añ’ atrefa’ i mpanjakay naho o mpanolo-keve’eo naho o roandriañe fatratse iabio. Le nampaozatse ahy te tamako ty fità’ Iehovà Andrianañahareko vaho namoriako mpiaolo ondaty boak’ Israele ao hitraok’ amako hionjoñe mb’eo.
Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a gaban sarki da mashawartansa, da kuma duk manyan masu muƙami nasa. Gama Ubangiji Allahna yana tare da ni, sai na sami ƙarfin hali na tattara shugabannin mutane daga Isra’ila, don mu tafi tare.