< Ezekiela 26 >
1 Ie am-baloham-bola’ i taom-paha-folo-raik’ambiy, te niheo amako ty tsara’ Iehovà nanao ty hoe:
A shekara ta goma sha ɗaya, a rana ta fari ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 O ana’ondatio, Kanao nanao ty hoe ty Tsore ty am’ Ierosalaime: Hike! rotsake, i ni-lalambei’ o kilakila’ ndatioy; fa midañadaña mb’amako: ho vontsy ty ama’e iraho henaneo, ie fa nikoahañe,
“Ɗan mutum, domin Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Yauwa! Ƙofar zuwa al’ummai ta karye, an kuma buɗe mini ƙofofinta; yanzu da take kufai zan wadace,’
3 aa le hoe t’Iehovà Talè; Inay te atreatrèko, ry Tsore, vaho hampanameako azo ty fifeheañe maro manahake ty ampitroare’ i riakey o onja’eo.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da ke, ya Taya, zan kuwa kawo al’ummai masu yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa.
4 Ho demohe’ iareo ty kijoli’ i Tsore naho hampikoromahe’ iareo o fitalakesañ’ abo’eo; mbore ho haoreko ama’e ty debo’e vaho hampanahafeko ami’ty tarehen-damilamy.
Za su hallaka katangar Taya su kuma rurrushe hasumiyoyinta; zan kankare tarkacenta, in maishe ta fā.
5 Ho fandafihañe harato añivo’ i riakey, vaho ho fañaoha’ o kilakila‘ndatio amy te Izaho ty nitaroñe, hoe t’Iehovà Talè.
Za tă zama wurin shanya abin kamun kifi a tsakiyar teku, gama na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Za tă zama ganima ga sauran al’ummai,
6 Ho zamanem-pibara o anak’ ampela’e an-tetekeo le ho fohi’ iareo te Izaho Iehovà.
za a kashe mazaunan filin ƙasar da takobi. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.
7 Fa hoe ty nafè’ Iehovà Talè; Oniño te hampivotraheko amy Tsore t’i Nebokadnetsare, mpanjaka’ i Bavele, ty mpanjaka’ o mpanjaka avaratse añeo, reketse soavala naho sarete, naho mpiningi-tsoavala, naho o lian-dahin-defo’eo, vaho i valobohòkey.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa daga arewa zan kawo wa Taya Nebukadnezzar sarkin Babilon, sarkin sarakuna, tare da dawakai da kekunan yaƙi, da mahayan dawakai da babbar rundunar soja.
8 Ho zamanem-pibara o anak’ ampela’o an-kivokeo; naho handranjia’e rafi-panameañe, naho hampitoabora’e tamboho vaho hañonjona’e fikalañe.
Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
9 Hampitroara’e lamasinañ’ aly amo kijoli’eo, vaho hampikoromahe’e am-pekoñe o fitalakesañ’ abo’eo.
Zai rushe katangarki da dundurusai, ya rurrushe hasumiyoyinki da makamai.
10 Ty debo’ i fitozatozan-tsoavala’ey ty handembeke azo, hiezeñezeñe o kijoli’oo ami’ty fikoraha’ o mpiningi-tsoavalao, naho amo larò’eo, naho amo sareteo, amy fimoaha’e amo lalam-bei’oo manahake ty fiziliha’ ondaty amo heban-kijolin-drova’ rotsakeo.
Dawakansa za su yi yawa har su rufe ke da ƙura. Katanga za su girgiza saboda motsin dawakan yaƙi, kekunan doki da keken yaƙin sa’ad da suka shiga birnin da aka rushe katangar.
11 Hampitrobohe’e an-tombon-tsoavala ze hene lalan-damo’ iareo; ho fonga zamane’e am-pibara ondati’oo vaho songa hideboñe an-tane o samposampon-kaozara’oo.
Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki; zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki masu ƙarfi kuma za su fāɗi a ƙasa.
12 Ho kamere’ iereo o vara’oo le fonga hikopà’ iareo o kilanka’ areoo; hampiantoe’ iareo o kijoli’oo, vaho harotsake o anjomba’ areo sarotseo; vaho halafi’ iareo am-po’ i ranoy ao o vato naho boda naho debo’oo.
Za su washe dukiyarki, kayan cinikinki kuma su zama ganima; za su rurrushe katangarki su ragargaza gidajenki masu kyau su kuma zubar da duwatsunki, katakanki da kuma tarkacenki a cikin teku.
13 Hajiheko ty feon-tsabo’o; vaho le lia’e tsy ho janjiñeñe ka ty fivola’ o marovani’oo.
Zan kawo ƙarshen waƙoƙinki masu surutu, ba kuwa za a ƙara jin kaɗe-kaɗen garayunki ba.
14 Hanoeko hambañe ami’ty lamilamy miloeloe, ho fandafihañe harato; toe tsy haoreñe ka, amy te Izaho Iehovà ty nivolañe, hoe t’Iehovà Talè.
Zan maishe ki fā, za ki kuma zama wurin shanya abin kamun kifi. Ba za a sāke gina ki ba, gama Ni Ubangiji na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Hoe ty nafè’ Iehovà Talè amy Tsore: Toe hampitroetroe o tokonoseo ty figaragadebo’o, ie mikaikaike o nifereo, ie henek’ añivo’o ao i fizamanañey.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Taya. Ƙasashen da suke a bakin teku ba za su girgiza saboda ƙarar fāɗuwarki, sa’ad da nishin waɗanda aka yi wa rauni da kashe-kashen da aka yi a cikinki suka faru ba?
16 Ie amy zay songa hizotso amo fiambesa’eo o roandria’ i riakeio naho hambine’ iareo o sarimbo’ iareoo, naho hafaha’ iareo o saro’e soa vinahotseo, hisikiñe fititititihañe; hitozòke an-tane eo hitolom-pihondrahondràñe vaho ho daba ty ama’o!
Sa’an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci suna razana saboda abin da ya same ki.
17 Le hañonjom-bekom-pandalàñe ama’o iereo, ami’ty hoe: Akore ty firotsaha’o, Ry nimoneñam-piandriakeo? Ty rova team-bintañe, naozatse amy riakey, ie naho o mpimone’eo, ze nampirevendreveñe o mpitobok’ ama’ao iabio.
Sa’an nan za su yi makoki game da ke su ce, “‘Yaya kika hallaka haka nan, ya birnin da ta yi suna, cike da mutanen teku! Ke da kika zama mai ƙarfi cikin tekuna, ke da mazauna cikinki; kin sa tsoronki a kan dukan waɗanda suka zauna a can.
18 Aa le hanginikinik’ amy andro fideboña’oy o tokonoseo, hiriatsandry ami’ty hamongora’o, o tokonose an-driak’ añeo.
Yanzu tsibirai suna rawar jiki a ranar fāɗuwarki; tsibirai a cikin teku sun tsorata a ɓacewarki.’
19 Fa hoe ty nafè’ Iehovà Talè: Hanoeko rova bangiñe irehe, manahake o rova mangoakoakeo; hampionjoneko hisaroñe azo ty tsikeokeoke; vaho rano maro ty handipots’ azo.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na maishe ki kufai, kamar sauran biranen da ba a ƙara zama a ciki, sa’ad da kuma na kawo zurfafan teku a kanki da yawan ruwansa suka rufe ki,
20 Ie hampizotsoeko mindre amo mizotso mb’an-kiborio ao, hitraok’ am’ondaty taoloo, naho hadoko am-pigadoñan-tsikeokeok’ ao, manahake o tanan-taolo haehaeo, miharo amo migodañe mb’an-donakeo, soa tsy ho amam-pimoneñe ka irehe te hatoloko engeñe i tanen-kaveloñey.
a sa’an nan zan sauko da ke ƙasa tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna ƙarƙashin ƙasa, kamar a kufai na tun dā, tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, ba kuwa za ki ƙara dawowa ba ko ki ɗauki matsayinki a ƙasar masu rai.
21 Hanoeko fangebakebahan-drehe, le tsy ho eo in-tsasa, ndra te paiaeñe tsy ho oniñe ka, hoe t’Iehovà Talè.
Zan sa ki yi mummunan ƙarshe kuma ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a ƙara same ki ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”