< Eksodosy 1 >
1 Iretoañe ty tahina’ o ana’ Israele nivotrake e Mitsraime ao nindre amy Iakòbeo songa an-kasavereña’e:
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
2 i Reòbene, i Simone, i Levy naho Iehodà,
Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
3 Isakare, i Zebolone naho i Beniamene,
Issakar, Zebulun da Benyamin;
4 i Dane naho i Naftalý, i Gade naho i Asere.
Dan da Naftali; Gad da Asher.
5 Fitom-polo ty ia’ ondaty nasama’ Iakòbeo. Fa te Mitsraime añe ka t’Iosefe.
Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
6 Ie nivilasy t’Iosefe naho i rahalahi’e rey iaby naho ze hene nimpirai-nono ama’e,
Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
7 le niraorao o ana’ Israeleo, nanarànake naho nitombo ho maro naho toe niha-ra’elahy vaho nahatsitsike i taney.
amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
8 Ie amy zao, nitroatse hifehe i Mitsraime ty mpanjaka tsy nahafohiñe Iosefe.
Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
9 Hoe re am’ondati’eo. Heheke, mandikoatse naho maozatse te aman-tika o ana’ Israeleo.
Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
10 Antao arè hinday iareo an-kihitse ke hitombo, hera mifetsak’ atoy ty aly le mete hirekets’ amo rafelahintikañeo iereo hialy aman-tika hienga an-tane atoy.
Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
11 Aa le nampijadoña’ iareo mpifelek’ ondevo, hamorekeke iareo an-kilankañe, le namboara’ iereo rova famandroñañe t’i Parò: i Pitòme naho i Raamèse.
Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
12 Aa ndra te nañindra i fampisilofañey, mbe nitombo naho nangetseketseke avao ondatio; toly ndra nampangebahebake iareo o ana’ Israeleo,
Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
13 le nampitoroñe’ o nte-Mitsraimeo an-kabodongero’e o ana’ Israeleo.
ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
14 Naho nanoeñe afero ty fiai’iareo, am-pifanehafañe mafe ami’ty birìke naho làlotse vaho amy ze hene fitoloñañe an-kivoke ey, le fonga an-tsenge-hery ty fampitromahañe nampanoeñe iareo.
Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
15 Le hoe ty mpanjaka’ i Mitsraime amo mpanaha-mampiterake o nte-Evreoo (i Siprahae ty añara’ ty raike naho i Poahae ty añara’ ty raike):
Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
16 Hoe re: Ie mampiterake ty rakemba nte-Evre naho mahaisak’ aze am-pitoboham-pisamahañe, ie lahilahy, vonò; fa naho ampela, apoho ho veloñe.
“Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
17 Fe nimpañeveñe aman’ Añahare o mpanàhao, le tsy nanoe’ iareo i nandilia’ i mpanjaka’ i Mitsraimeiy, fa nenga’ iareo veloñe o lahilahio.
Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
18 Aa le kinoi’ i mpanjaka’ i Mitsraimey i mpanaha rey naho nanoa’e ty hoe, Akore ty anoa’ areo zao, te apo’ areo veloñe o lahilahio?
Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
19 Hoe i mpanaha rey amy Parò, Toe tsy hambañe amo rakemba nte-Mitsraimeo o rakemba ana’ Israeleo fa mavitrike mahatoly aolo’ ty ivotraha’ ty mpanaha.
Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
20 Aa le nanoan’ Añahare soa o mpanahao; vaho niha-tsiefa naho nitombo an-kaozarañe ondatio.
Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
21 Aa kanao nañeveñe aman’ Añahare o mpanahao le nampisavereñe’e.
Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
22 Le hoe ty nafanto’ i Parò am’ondati’e iabio: Afetsaho amy Nailey ze hene anadahy samake, fa tano ho veloñe o anak’ampelao.
Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”