< Asan'ny Apostoly 7 >
1 Hoe i talèm-pisoroñey: To v’zao?
Sai babban firist ya tambaye shi ya ce, “Waɗannan zargen gaskiya ne?”
2 Hoe t’i Stefana: Ry longo, naho ry aba, Inao! Ie mbe te Mesopotamia añe taolo’ te nimoneñe e Haraña t’i Abraàme raen-tikañe le niheo ama’e t’i Andrianañahare Rengèñey,
Game da wannan ya amsa ya ce, “’Yan’uwa da ubanni, ku saurare ni! Allah mai ɗaukaka ya bayyana ga kakanmu Ibrahim yayinda yake a ƙasar Mesofotamiya tukuna, kafin ya yi zama a Haran.
3 le nanoa’e ty hoe: Misitaha an-tane’o naho an-drolongo’o, mimoaha an-tane hatoroko azo.
Allah ya ce, ‘Ka bar ƙasarka da kuma mutanenka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.’
4 Aa le niakats’ i tane Kaldea añe re nivotrake e Harane. Ie añe, naho fa vilasy ty rae’e, le nampiavote’e homb’an-tane fimoneña’ areo atoy henaneo.
“Saboda haka ya bar ƙasar Kaldiyawa ya kuma yi zama a Haran. Bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya aika da shi wannan ƙasar da yanzu kuke zama.
5 Fe tsy nimea’e lova ama’e, ndra ty tane handiam-pandia’e, ie mbetsiterake, le nampitama’e te hatolots’aze naho amo tarira’e hanonjohy azeo ho fanañañe izay.
Bai ba shi gādo a nan ba, ko taki ɗaya na ƙasa. Amma Allah ya yi masa alkawari cewa shi da zuriyarsa masu zuwa bayansa za su mallaki ƙasar, ko da yake a lokacin Ibrahim ba shi da yaro.
6 Hoe ty nitsaran’ Añahare, t’ie: Ho renetane an-tanen’ ambahiny o tarira’eo, naho hondevozeñe, vaho ho volevolèñe efa-jato taoñe.
Allah ya yi magana da shi ta haka, ‘Shekara ɗari huɗu, zuriyarka za tă yi baƙunci a wata ƙasar da ba tasu ba, za su yi bauta su kuma sha wulaƙanci.
7 Fe ho zakaeko ze tane mañondevo iareo, hoe t’i Andrianañahare, ie añe, le hiavotse iereo, hitoroñe ahy ami’ty toetse toy.
Amma zan hore ƙasar da suka bauta wa.’ Allah ya ce, ‘Kuma daga baya za su fita daga wannan ƙasa su kuma yi mini sujada a wannan wuri.’
8 Le natolo’e aze ty fañinam-pisavarañe naho nisamake Isaka re le nisavare’e ami’ty andro fahavalo, naho nisamake Iakobe t’Isaka vaho i androanavy folo ro’amby rey t’Iakobe.
Sa’an nan ya yi wa Ibrahim alkawari game da kaciya. Ibrahim kuwa ya zama mahaifin Ishaku ya kuma yi masa kaciya kwana takwas bayan haihuwarsa. Daga baya Ishaku ya zama mahaifin Yaƙub, Yaƙub kuma ya zama mahaifin kakanninmu sha biyun nan.
9 Ie nikirañe Iosefe i androanavy rey, le naleta’ iereo ho ondevo Egipte añe. Fe tama’e t’i Andrianañahare
“Domin kakanninmu sun ji kishin Yusuf, sai suka sayar da shi bawa zuwa Masar. Amma Allah ya kasance tare da shi
10 nandrombak’ aze amy ze fonga haoreañe naho tinolo’e hihitse naho fañisohañe añatrefa’ i Farao mpanjaka’ i Egipte le nanoe’e mpamandroñe hifehe i Egipte vaho o añ’ anjomba’e iabio.
ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
11 Nandramban-tane Egipte naho Kanana amy zao ty san-kasalikoañe vaho ty hasotriam-bey le tsy nahaoniñe mahakama o roaentikañeo.
“Sai yunwa ta auko wa dukan Masar da Kan’ana, ta kawo wahala mai tsanani, kakanninmu ba su iya samun abinci ba.
12 Ie jinanji’ Iakobe te aman-tsako ty Egipte, le nampihitrife’e mb’eo o roaentikañeo amy valoha’ey.
Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa akwai hatsi a Masar, sai ya aiki kakanninmu ziyararsu ta farko.
13 Ie amy faha roey le nampahafohim-batañ’ amo rahalahi’eo t’Iosefe vaho nampandrendreheñe i Farao o longo’ Iosefeo.
A ziyararsu ta biyu, Yusuf ya faɗa wa’yan’uwansa wane ne shi, Fir’auna kuwa ya sami sani game da iyalin Yusuf.
14 Aa le nampisangitrife’ Iosefe t’Iakobe rae’e naho o longo’eo, i fitom-polo-lime amby rey.
Bayan wannan, Yusuf ya aika a zo da mahaifinsa Yaƙub da dukan iyalinsa, gaba ɗaya dai mutum saba’in da biyar ne.
15 Le nañavelo mb’e Egipte mb’eo t’Iakobe vaho nihomake, ie naho o roaentikañeo,
Sai Yaƙub ya gangara zuwa Masar, inda shi da kuma kakanninmu suka mutu.
16 le nasese mb’e Sekema añe, ie nirohoteñe amy lonake vinili’ i Abraàme drala amo ana’ i Hamora nte Sekemaio.
Aka dawo da gawawwakinsu Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya daga wurin’ya’yan Hamor da waɗansu kuɗi a Shekem.
17 Aa naho fa an-titotse ty andro nampitaman’ Añahare i nifantà’e amy Abraàmey, le nitombo naho nangetseketseke Egipte añe ondatio.
“Da lokaci ya yi kusa da Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim, sai yawan mutanenmu da suke a Masar ya ƙaru ƙwarai.
18 Loneak’amy zao ty mpanjaka hifehe i Egipte tsy nahafohiñe Iosefe.
Sa’an nan wani sarki, wanda bai san kome game da Yusuf ba, ya zama mai mulkin Masar.
19 Ie ty nañaramamo ondatin-tikañeo am-pamañahiañe naho famorekekeañe, naho nampiboake o ajajamena’ iareoo tsy hahatam-beloñe.
Ya kuwa wulaƙanta mutanenmu sosai, ya kuma gwada wa kakanni-kakanninmu azaba ta wurin tilasta su su zubar da sababbin jariransu, don su mutu.
20 Toly henane zay t’i Mosè, le nisoa vintañe am-pivazohoan’ Añahare, vaho nitaiàñe telo volañe an-trañon-drae’e ao.
“A lokacin nan aka haifi Musa, shi kuwa ba kamar sauran jarirai ba ne. Wata uku aka yi renonsa a gidan mahaifinsa.
21 Aa ie niotañe, rinambe’ ty anak’ ampela’ i Farao naho nibeize’e ho ana’e,
Sa’ad da aka ajiye shi a waje, diyar Fir’auna ta ɗauke shi ta kuma rene shi kamar ɗanta.
22 le naòke amy ze hene hilala’ o nte Egipteo t’i Mosè vaho ni-fanalolahy an-tsara naho fitoloñañe.
Musa ya sami ilimi cikin dukan hikimar Masarawa ya kuma zama mai iko cikin magana da ayyuka.
23 Ie fa ho efa-polo taoñe t’i Mosè, le niheo añ’arofo’e ty hitilike o longo’e ana’ Israeleo.
“Da Musa ya cika shekara arba’in da haihuwa, sai ya yanke shawara yă ziyarci’yan’uwansa Isra’ilawa.
24 Ie nioni’e te nisamporeraheñe tsy aman-tali’e ty raike, le nañolots’ aze, namale fate i niforekekeñey vaho nañoho-doza amy nte-Egiptey.
Ya ga ɗayansu yana shan wulaƙanci a hannun wani mutumin Masar, sai ya je ya kāre shi, ya rama masa ta wurin kashe mutumin Masar ɗin.
25 Natao’e ho rendre’o longo’eo ty fandrombahan’ Añahare am-pità’e, f’ie tsy nahafohiñe.
Musa ya yi tsammani mutanensa za su gane cewa, Allah yana amfani da shi don yă cece su, amma ba su gane ba.
26 Ie niloakandro, niheo am’iereo mb’eo re nanjo ty nifandrapak’ aly, le nimanea’e fifampilongoañe ami’ty hoe: O lahireo, mpiroahalahy nahareoo; Akore te mifampijoy?
Kashegari, Musa ya sadu da Isra’ilawa biyu suna faɗa. Ya yi ƙoƙari ya sasanta su, yana cewa, ‘Ku mutane, ku’yan’uwa ne, don me kuke so ku cutar da juna?’
27 Fe nanafasiotse aze i namofoke i rañe’eiy, nanao ty hoe: Ia ty nañory azo ho mpifehe naho mpizaka anay?
“Amma mutumin da yake wulaƙanta ɗayan, ya tura Musa a gefe ya ce, ‘Wa ya mai da kai mai mulki, da alƙali a kanmu?
28 Hamono ahy v’iheo, hambañe amy nanoa’o i nte Egipte omaley?
Kana so ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan na jiya?’
29 Ty amy entañe zay, nitriban-day t’i Mosè naho nirenetane e Midiana añe vaho nisamak’ anadahy roe.
Sa’ad da Musa ya ji haka, sai ya gudu zuwa ƙasar Midiyan, inda ya yi baƙunci, ya kuma haifi’ya’ya biyu maza.
30 Ie nimodo ty efa-polo taoñe, le nisodehañe ama’e an-dratraratram-bohi-Sinaiy añe ty anjeli’ Iehovà ami’ty lel’afo an-drongoñe.
“Bayan shekaru arba’in suka wuce, sai mala’ika ya bayyana ga Musa cikin harshen wuta a ɗan itace a hamada kusa da Dutsen Sinai.
31 Ie nioni’ i Mosè zay le hinarahara’e i nizoeñey; le nañarivoa’e hahaisake vaho nivovo ama’e ty fiarañanaña’ Iehovà nanao ty hoe:
Sa’ad da ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya yi kusa domin ya duba sosai, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,
32 Izaho o Andrianañaharen-droae’ areoo, t’i Andrianañahare’ i Abraàme, naho Isaka vaho Iakobe. Aa le ninevenevetse t’i Mosè tsy nahavany niisake.
‘Ni ne Allahn kakanninka, Allah na Ibrahim, Ishaku, da kuma Yaƙub.’ Sai Musa ya yi rawan jiki don tsoro, bai kuwa yi karambanin dubawa ba.
33 Le hoe t’ Iehovà tama’e: Afaho o hana am-pandia’oo fa masiñe o toetse ijohaña’oo.
“Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, ‘Ka cire takalmanka; wurin da kake tsayen nan mai tsarki ne.
34 Toe niisako ty falovilovia’ ondatiko e Egipt’aoo, naho tsinanoko ty toreo’ iareo vaho nizotso hañaha iareo. Antao arè, fa hahitriko mb’e Egipte mb’eo irehe.
Tabbatacce na ga wulaƙancin da ake yi wa mutanena a Masar. Na ji nishinsu na kuma sauka domin in’yantar da su. Yanzu ka zo, zan aike ka ka koma Masar.’
35 Fe kiniho’iareo ami’ty hoe t’i Mosè: Ia ty nañory azo ho mpifehe naho mpizaka anay? Ie ty nafanton’ Añahare ampità’ i anjely niboak’ ama’e amy rongoñeiy ho mpifehe naho mpandrombake iareo.
“Wannan Musa ɗin da suka ƙi suna cewa, ‘Wa ya mai da kai mai mulki da kuma alƙali?’ Allah da kansa ya aike shi, ta wurin mala’ikan da ya bayyana a gare shi a ɗan itace, yă zama mai mulkinsu, da kuma mai cetonsu.
36 Indatiy ty nampiavotse iareo naho nanao halatsàñe naho viloñe tsi-tantane Egipte ao naho amy Riake Menay vaho am-patrambey ao efa-polo taoñe.
Ya fitar da su daga Masar ya kuma yi ayyukan da abubuwan banmamaki a Masar, a Jan Teku, da kuma cikin hamada har shekara arba’in.
37 Ie i Mosè nitaroñe amo nte-Israeleo ty hoe: Hampitroaren’ Añahare ho anahareo ty mpitoky hambañe amako boak’amo longo’ areoo.
“Wannan Musa ne ya ce Isra’ilawa, ‘Allah zai aika muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku.’
38 Ie ty nitraok’ amy anjeliy amy fivori-bey am-patram-bey añey, niharo amy anjely nisaontsy ama’e am-bohi-Sinaiy vaho taman-droaentikañe; ie ty nandrambe o fetse veloñe nitaroña’e aman-tikañeo.
Ya kasance a cikin taron nan a hamada, tare da mala’ikan da ya yi magana da shi a Dutsen Sinai, da kuma tare da kakanninmu; ya kuma karɓi kalmomi masu rai don yă miƙa mana.
39 Fe, nizeharen-droaentika naho nasiotsio’ iareo, vaho nitolike mb’Egipte ty arofo’ iareo
“Amma kakanninmu suka ƙi yin masa biyayya. A maimakon haka, sai suka ƙi shi a cikin zuciyarsu kuwa suka koma Masar.
40 le nanao ty hoe amy Arone: Andranjio ndrañahare hiaolo anay, f’i Mosè nañavotse anay añ’Egipte izay, amoea’ay ty nizò aze!
Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana allolin da za su yi mana jagora. Game da wannan Musa ɗin wanda ya fitar da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba!’
41 Nitsene bania iereo henane zay naho nibanabana soroñe amy sarey, vaho nirebek’ amy sata-pità’ iareoy.
A lokacin ne suka ƙera gunki mai siffar ɗan maraƙi. Suka kawo masa hadayu suka kuma yi bikin girmama abin da suka ƙera da hannuwansu.
42 Aa le niambohoan’ Añahare naho nitolora’e ty hitoroñe i fifamorohotan-dindìñey, ie pinatetse amy bokem-pitokiy: O ry anjomba’ Israeleo, nañenga biby linenta vaho soroñe amako efa-polo taoñe am-patram-bey añe v’inahareo?
Sai Amma Allah ya juya musu baya ya kuma ba da su ga bautar abubuwan da suke a sararin sama. Wannan ya yi daidai da abin da yake a rubuce a cikin littafin annabawa cewa, “‘Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in cikin, hamada, ya gidan Isra’ila?
43 Te mone nitarazoe’ areo ty kivoho’ i Moloka, naho ty vasia’ i Refane ndrañahare’areoy, o samposampon-draha namboare’ areo ho fitalahoañeo. Aa le haseseko mb’an-kalo’ i Bavele añe nahareo.
Kun ɗaukaka gidan tsafin Molek, da tauraron allahnku Refan, gumakan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Saboda haka zan aike ku zuwa bauta’ gaba da Babilon.
44 Taman-droaen-tikañe an-dratraratra añe i kivohom-pitaroñañey, namboareñe do’e amy nisaontsie’e amy Mosèy te hamboare’e hamban-tsata amy niisa’ey.
“Kakanni-kakanninmu suna da tabanakul na Shaida tare da su a hamada. An yi shi bisa ga yadda Allah ya umarci Musa, bisa ga zānen da ya gani.
45 Le nampizilihe’ o roae’ay nandrambe azeo izay mindre amy Josoa, ie tinava’ iareo amo kilakila’ ndaty nasiotsion’ Añahare aolon-dahara’ iareoo i Taney; ie izay ampara’ i Davide;
Bayan sun gāji tabanakul nan, kakanninmu a ƙarƙashin jagorancin Yoshuwa suka kawo shi tare da su, lokacin da suka ƙwace ƙasar daga al’umman da Allah ya kora a idanunsu. Tabanakul ɗin ya kasance a ƙasar har zamanin Dawuda,
46 ie nanjò fañisohañe añatrefan’ Añahare, le nihalaly ty hahaoniña’e toetse himoneñan’ Añahare’ Iakobe.
wanda ya sami tagomashi daga Allah, ya kuma nemi yă yi wa Allah na Yaƙub wurin zama.
47 Fe i Selomò ty nandranjy anjomba ho aze.
Amma Solomon ne ya gina masa gida.
48 Toe tsy miambesatse ami’ty nanoem-pitàñe t’i Andindimoneñe, amy tsara’ i mpitokiy:
“Duk da haka, Mafi Ɗaukaka ba ya zama a gidajen da mutane suka gina. Kamar yadda annabi ya faɗi cewa,
49 Fitobohako i likerañey, fitongoàn-tomboko ty tane toy. anjomba manakore arè ty ho ranjie’ areo ho ahiko? Hoe t’Iehovà. Ke, aia ty toetse hitofàko?
“‘Sama ne kursiyina, duniya kuma wurin ajiye tafin ƙafata. Wane irin gida za ka gina mini? Ko kuwa ina wurin hutuna zai kasance? In ji Ubangiji.
50 Tsy ty tañako hao ty nanao ze he’e zao?
Ba hannuna ne ya yi dukan waɗannan abubuwa ba?’
51 Ry gan-katoke tsy sinavatse añ’arofo ndra an-dravembia. Zehare’ areo nainai’e i Arofo Masiñey manahak’ an-droae’ areo avao.
“Ku mutane masu taurinkai, da zukata da kuma kunnuwa marasa kaciya! Kuna kama da kakanninku. Kullum kuna tsayayya da Ruhu Mai Tsarki!
52 Ia amo mpitokio ty tsy nisamporerahen-droae’ areo? Nañohofa’ iareo loza o nitoky ty fitotsaha’ i Vañoñeio, i nafote’ areo naho vinono’ areo anianiy;
An yi wani annabin da kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun ma kashe waɗanda suka yi maganar zuwan Mai Adalcin nan. Yanzu kuwa kun bashe shi kuka kuma kashe shi
53 iereo fa nandrambe i Hake nafè’ o anjelioy, f’ie tsy nambenañe.
ku da kuka karɓi dokar da aka sa a aiki ta wurin mala’iku amma ba ku yi biyayya da ita ba.”
54 Ie jinanji’iereo i hoe zay, le niromotse añ’arofo vaho nampikodrì-nife.
Da membobin Sanhedrin suka ji haka, sai suka yi fushi suka ciji haƙoransu.
55 Ie ka, lifotse i Arofo Masiñey, niandrandra nitalake i likerañey vaho nahaisake ty engen’ Añahare naho Iesoà nijohañe am-pitàn-kavanan’ Añahare ey.
Amma Istifanus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dubi sama ya kuma ga ɗaukakar Allah, da Yesu kuma tsaye a hannun dama na Allah.
56 Heheke, hoe re, Treako te misokake o likerañeo vaho mijohañe ampitàn-kavanan’ Añahare eo i Ana’ondatiy.
Ya ce, “Ga shi, na ga sama a buɗe da kuma Ɗan Mutum tsaye a hannun dama na Allah.”
57 F’ie nipoña-koràke, nanentsen-dravembia vaho fonga nitrao-pañoridañe aze,
Da jin haka sai suka tattoshe kunnuwansu, suka kuma yi ihu da ƙarfi sosai, suka aukar masa gaba ɗaya.
58 le naronjeronje’ iareo alafe’ i rovay, naho nametsa-bato ama’e vaho napo’ o valolombeloñeo an-tombo’ ty dogalahy atao Saole eo o sarimbo’ iareoo.
Suka ja shi zuwa bayan birnin suka kuma yi ta jifansa da duwatsu. Ana cikin haka, shaidun suka ajiye tufafinsu a wurin wani saurayi mai suna Shawulu.
59 Ie nitolom-pametsam-bato amy Stefana, le nikaihe’e ty hoe: Ry Iesoà Talè, rambeso ty troko.
Yayinda suke cikin jifansa, sai Istifanus ya yi addu’a ya ce, “Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”
60 Ie tafatongaleke, le pinaza’e am-piarañanañañe ty hoe: O Talè, ko tiñea’o am’iareo ty hakeo toy. Ie nanao izay le nirotse.
Sa’an nan ya durƙusa ya ɗaga murya ya ce, “Ubangiji, kada ka riƙe wannan zunubi a kansu.” Da ya faɗi haka, sai ya yi barci.