< Asan'ny Apostoly 3 >
1 Nindre nionjomb’añ’anjomban’ Añahare mb’eo amy ora fitalahoañe amy siveiy t’i Petera naho i Jaona.
Wata rana, Bitrus da Yohanna suna haurawa zuwa haikali a lokacin addu’a da ƙarfe uku na rana.
2 Le teo ty lahilahy nitakoneñe, nikepeke boak’ ami’ty nahatoly aze, ie natobòke boak’ andro an-dalam-bei’ i anjomban’ Añaharey atao ty hoe Fanjàka eo, nihalaly falalàñe amo mizilik’ añ’ anjomban’ Añahareo.
To, sai ga wani da aka haifa gurgu ana ɗauke da shi zuwa ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, inda akan ajiye kowace rana, don yă yi bara daga masu shigowa cikin filayen haikali.
3 Ie nahaoniñe te hizilik’ amy anjombay t’i Petera naho i Jaona, le nihalalia’e falalàñe.
Da ya ga Bitrus da Yohanna suna gab da shiga, sai ya roƙe su kuɗi.
4 Fe nitalahare’ i Petera naho i Jaona, nanao ty hoe ama’e: Mivazohoa mb’etoa.
Bitrus kuwa ya kafa masa ido, haka ma Yohanna. Sai Bitrus ya ce, “Dube mu!”
5 Le nihaoñe’e fa nitama raha.
Saboda haka mutumin ya mai da hankalinsa a kansu, yana fata samun wani abu daga gare su.
6 Le hoe t’i Petera: Tsy amam-bolafoty ndra volamena iraho, fe homeiko azo ze amako: Ami’ty tahina’ Iesoà nte Nazareta Norizañey, Midraidraita!
Sai Bitrus ya ce, “Azurfa ko zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. A cikin sunan Yesu Kiristi Banazare, ka yi tafiya.”
7 le rinambe’e ty fitàn-kavana’e naho nongaha’e vaho nihafatratse amy zao o fandia’e naho fange’eo.
Ta wurin kama hannunsa na dama, ya taimake shi ya miƙe, nan take ƙafafu da idon sawun mutumin suka yi ƙarfi.
8 Le nitsamboan-dre naho nitrahañe vaho nitsontike le niharo fizilik’ am’ iereo mb’añ’ anjomban’ Añahare ao, mbore nijohañe mbore nitambòtrake vaho nibango an’Andrianañahare.
Sai ya yi wuf da ƙafafunsa ya fara tafiya. Ya tafi tare da su ya shiga cikin filin haikali yana tafiya yana tsalle, yana kuma yabon Allah.
9 Naho nioni’ i lahialeñey t’ie nitrantràñe, nisabo an’ Andrianañahare,
Sa’ad da dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana yabon Allah,
10 naho naharendreke i nikonenake nihalaly falalàñe an-dalam-bey Fanjàka’ i anjomban’ Añahareiy, le niveren-draha naho nilatsa amy nanoañey.
sai suka gane cewa shi ne mutumin nan wanda dā yake zama yana bara a bakin ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, suka kuwa cika da mamaki da tsoro a kan abin da ya faru gare shi.
11 Nireketse amy Petera naho i Jaona i nikepeke nampijangañeñey, le nilay mb’ am’ iereo amy kiririsa atao: A i Solomonay mb’eo ze hene ondaty, fa lifo-kavereñañe.
Tun mai bawan yana riƙe da Bitrus da Yohanna, dukan mutanen suka yi mamaki, suka zo wurinsu a guje a inda ake kira Shirayin Solomon.
12 Ie nirendre’ i Petera, le nilañona’e ty hoe am’ondatio: Ry nte Israeleo, ino ty ilatsà’ areo o raha zao? ino ty isambà’ areo anay hoe te zahay, ami’ty haozara’ay naho ami’ty havañona’ay, ro nampanjotike t’indaty toy?
Da Bitrus ya ga haka, sai ya ce musu, “Mutanen Isra’ila, don me wannan ya ba ku mamaki? Don me kuke kallonmu sai ka ce da ikon kanmu ne ko kuwa don ibadarmu ne muka sa wannan mutum ya yi tafiya?
13 I Andrianañahare’ i Abraàme naho Isaka vaho Iakobe, i Andrianañaharen-droaentikañey, ro mandrenge Iesoà mpitoro’e nasese naho nifarie’ areo añatrefa’ i Pilato, ie fa nisafiry ty hamotsotse aze.
Allah na Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub, Allah na kakanninmu, ya ɗaukaka bawansa Yesu. Ku kuka ba da shi domin a kashe, kuka yi mūsun saninsa a gaban Bilatus, ko da yake ya yi niyya ya sake shi.
14 Tineti’ areo i Masiñe naho Vañoñey naho nihalaly te hahàñe ama’ areo ty mpamono,
Kuka yi mūsun sanin Mai Tsarki da Mai Adalci kuka roƙa a sakar muku mai kisankai.
15 vaho vinono’ areo i Rañandrian-kaveloñey, f’ie natroan’ Añahare an-kavilasy; valolombeloñe zahay.
Kuka kashe tushen rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu. Mu shaidu ne ga wannan.
16 Ty fatokisa’e amy tahina’ey ty nampaozare’ i tahina’ey ondaty isa’ areo naho fohi’ areoo; eka, ty fatokisañe ama’e ty naha-arimoen-kajanganañ’ aze añatrefa’ areo iaby.
Ta wurin bangaskiya cikin sunan Yesu ne wannan mutum da kuke gani kuka kuma sani ya sami ƙarfi. Da sunan Yesu, da kuma bangaskiyar da take samuwa ta wurinsa ne ya ba shi cikakkiyar warkarwa, yadda dukanku kuke gani.
17 Ie amy zao, ry longo, fantako te namoea’ areo i nanoe’ areoy—hambañe amy nanoe’ o bei’ areoo.
“To,’yan’uwa, na san cewa, kun aikata wannan cikin jahilci ne, yadda shugabanninku suka yi.
18 F’ie ty nañenefan’ Añahare o nitaroñe’e am-palie’ ze fonga mpitoky haehaeo, te tsi-mahay tsy hijale i Noriza’ey.
Amma ta haka ne Allah ya cika abin da ya rigyafaɗi ta bakin dukan annabawa cewa, Kiristinsa zai sha wahala.
19 Misolohoa arè, mipolia, soa te ho faoheñe o tahi’ areoo, naho hitotsake boak’ am-piatrefa’ Iehovà ty san-kanintsiñe,
Saboda haka ku tuba, ku juyo ga Allah, don a shafe zunubanku, don lokutan wartsakewa su zo daga wurin Ubangiji,
20 vaho hirahe’e t’Iesoà, i Norizañe tinendre ho anahareoy,
don kuma ya iya aika da Kiristi, wanda aka naɗa tun dā saboda ku, Yesu ke nan.
21 ze tsi-mete tsy ho tanañe an-dikerañe ao hey ampara’ ty sam-pañavaoañe ze he’e tsinaran’ Añahare am-palie’ ze hene mpitoky masiñe boak’ am-pifotora’ ty voatse toy. (aiōn )
Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. (aiōn )
22 Fa hoe t’i Mosè: Mpitoky hambañ’amako ty hatroa’ Iehovà Andrianañahare boak’ amo longo’areoo; janjiño ze hene ho saontsie’e ama’areo.
Gama Musa ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai tasar muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku; dole ku saurari duk abin da ya faɗa muku.
23 Le hifetsake te haitoañe am’ ondati’eo ze tsy mañaoñe i Mpitokiy.
Duk wanda bai saurare shi ba za a ware shi gaba ɗaya daga mutanensa.’
24 Eka, songa nitoky o andro zao ze mpitoky nisaontsy mifototse amy Samoela vaho o nanonjohio.
“Tabbatacce, dukan annabawa daga Sama’ila zuwa gaba, dukansu da suka yi magana, sun rigya faɗin waɗannan kwanaki.
25 Inahareo ro tarira’ o mpitokio naho mpiamy fañina nanoen’ Añahare aman-droaentikañey, Ie nanao ty hoe amy Abraàme: I tiri’oy ro hitahiañe ze kila foko’ ty tane toy.
Ku kuwa magādan annabawan ne da kuma na alkawarin da Allah ya yi da kakanninku. Ya ce wa Ibrahim, ‘Ta wurin zuriyarka, dukan kabilan duniya za su sami albarka.’
26 Ie natroan’ Añahare ty mpitoro’e Iesoà le nahitri’e ama’areo hey hampanintsiña’e, amy nampiambohoe’e anahareo o sata tsivokatseo.
Da Allah ya tashe bawansa, ya aike shi da fari zuwa gare ku don yă albarkace ku ta wurin juye kowannenku daga mugayen hanyoyinku.”