< Asan'ny Apostoly 23 >
1 Nitalatse amy Sinedrionay t’i Paoly, nanao ty hoe: Ry roahalahiko, fa mpiaiñe an-kazavan-troke añatrefan’ Añahare iraho ampara’ ty andro toy.
Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
2 Aa le linili’ i Ananiasy mpisorom-bey o narine azeo ty hitampify aze am-palie’e.
Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
3 Le hoe t’i Paoly ama’e: Ho tampifien’ Añahare irehe, ty rìndri-foty tia. Ihe miambesatse ey handily ahy amy Hake te mone mañota Hake amy nandilia’o ho tampifieñey.
Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
4 Hoe ty asa’ o narineo: Mañondritse i talèm-pisoron’ Añaharey v’iheo?
Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
5 Aa hoe t’i Paoly, Ry rahalahio, tsy nirendreko t’ie talèm-pisoroñe, fa pinatetse ty hoe: Ko injè’o ty mpifehe ondati’oo.
Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
6 Ie nifohi’ i Paoly te Tsadoke ty ila’ iareo vaho Fariseo ty ila’e, le hoe ty koi’e amy fivoriy: Ry roahalahio, Fariseo iraho, ana’ ty Fariseo. Mijohañ’ etoan-draho hizakañe amy fitamañe te hitroatse o mihomakeo.
Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
7 Amy fipaza’ey, le nifanointoiñe o Fariseoo naho o Tsadokeo vaho nifanarake i fivoriy.
Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
8 (Liere’ o Tsadokeo ty fivañonam-beloñe, naho anjely, vaho arofo, f’ie fonga ifahara’ o Fariseoo.)
(Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
9 Nipoñak’ amy zao ty hozakozake, le niongake vaho nimanea’ ty Fariseo mpañoke Hake lietse ami’ty hoe: Tsy oni’ay ty hila’ ondatio. Ke tsinara’ ty fañahy he ty anjely?
Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
10 Niindra i hotakotakey, le nihakahaka i talè, hera ho rifodrifoteñe t’i Paoly, le linili’e o lahin-defo’eo ty hizotso mb’eo hanintak’ aze an-kaozarañe, hampoly aze mb’añ’akiba añe.
Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
11 Ie haleñe, le nijohañe añ’ila’eo t’i Talè nanao ty hoe: Mireareà! Fa hambañe ami’ty nitaroña’o ahy e Ierosaleme ao, ty ho taroñe’o e Roma añe.
Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
12 Amy loak’ àndroy le nifañosoñe hikitrok’ aze o Tehodao, nifamehe am-panta te tsy hikama ndra hinoñe ampara’ te havetra’ iareo t’i Paoly.
Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
13 Mandikoatse ty efa-polo i nikilily rey.
Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
14 Niheo mb’ amo beim-pisoroñeo naho o roaeo iereo nanao ty hoe: Nifamehe am-panta mijadoñe zahay te tsy hitsope-draha ampara’ te vonoe’ay t’i Paoly.
Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
15 Ie amy zao, ry amo Sinedrionaio, Ehe mihalalia amy talèy ty hanjotsoañe aze ama’ areo mintse hamotopotorañe aze, fa veka’e hanjevoñ’ aze zahay aolo’ t’ie mitotoke.
Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
16 Fe tsinano’ ty ana-drahavave’ i Paoly i famandroñañey le nimb’eo nizilik’ añ’anjomba’ o lahin-defoñeo nitalily amy Paoly.
Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
17 Kinanji’ i Paoly ty mpifehe zato, le hoe re: Endeso mb’amy talè ao ty ajalahy toy, fa aman-ko volañe’e.
Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
18 Aa le nente’e naho nasese amy talèy, nanao ty hoe: Nitok’ ahy t’i Paoly mpirohy, nihalaly te hendeseñe ama’o ty ajalahy toy fa aman’ entañe.
Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
19 Rinambe’ i talèy an-taña’e i ajalahiy le natola’e vaho nañontanea’e ty hoe: Ino ty enta’o ho ahiko?
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
20 Hoe re: Fa nilahatse hihalaly ama’o o Tehodao ty haneseañe i Paoly mb’amy fivoriy ao hamaray, hanao sare hañotsohotso aze.
Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
21 Ko no’o, amy te amandroña’ ty mandako ty efa-polo nifanta te tsy hikama ndra hinoñe ampara’ t’ie vinono; fa veka’e henaneo iereo, mandiñe ty fampitamà’o.
Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
22 Aa le napo’ i talèy hiavotse i ajalahiy, ie fa nitoroa’e ty hoe: Ko mivolañe ama’ iaia i nitalilie’oy.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
23 Kinanji’e ty mpifehe zato roe le natà’e ty hoe: Añajario lahin-defo roan-jato hikatsakatsake mb’e Kaisaria añe, naho mpiningi-tsoavala fitom-polo vaho mpitàm-pìletse roan-jato amy ora faha-telo’ i haleñeiy.
Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
24 Toloro soavala hiningira’ i Paoly, le aseseo mb’am-pitsolohañe amy Ragova Feliksa añe.
Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
25 Nanokira’e taratasy hoe zao:
Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
26 Klaodio Lisia: Ho an-dRagova Feliksa, foloaingitroke, Fañanintsiñe!
Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
27 Ingo t’indaty tsinepa’ o Tehodao, le didý tsy ho vinono’ iereo, f’ie nivotrake eo reketse lahin-defoñe nandrombak’ aze, ie nirendreko te nte-Roma.
Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
28 Aa izaho te hahafohiñe ty talin-kitomboha’ iareo aze, le naseseko mb’amy Sinedriona’ iareoy,
Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
29 fe nizoeko te ontane amo lili’ iareoo ty nanisíañe aze, le tsy amo sisì’eo ty mañeva hamonoañe ndra handrohizañe aze.
Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
30 Ie nampaharendreheñe te nikililieñe indatiy, le nahitriko mb’ama’o mb’eo amy zao, vaho liniliko o mpanisý azeo te haseseke añatrefa’o ty talin-tsisì’ iareo.
Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
31 Aa ie namantohañe, le nendese’ o lahin-defoñeo t’i Paoly naho nasese mb’e Antipatria mb’eo amy haleñey.
Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
32 Amy loak’ àndroy le nampindrezeñe ama’e o mpiningi-tsoavalao vaho nimpoly mb’an-tobe mb’eo ty ila’e.
Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
33 Ie nipotìtse e Kaisaria añe, le natolotse amy Ragovay i taratasiy le nasese ama’e ka t’i Paoly.
Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
34 Vinaki’ i ragovay i taratasiy vaho nañontanea’e ty faritse nihirifa’e. Ie rendre’e te nte Kilkia,
Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
35 le hoe re: Hitsanoñako naho avy o mpanisý azoo, le linili’e te hambenañe añ’ anjombam-pizakà’ i Heroda ao.
sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.