< 2 Samoela 3 >

1 Nitolom-pialy avao ty anjomba’ i Saole naho ty anjomba’ i Davide; le nihafatratse erike t’i Davide vaho ninìke erike ty anjomba’ i Saole.
Aka daɗe ana yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda. Dawuda kuwa ya yi ta ƙara ƙarfi, yayinda gidan Shawulu ya yi ta raguwa a ƙarfi.
2 Nisamak’ anadahy e Kebrone ao t’i Davide; i Amnone ty tañoloñoloña’e boak’ amy Akinoame nte-Iezreele;
An haifa wa Dawuda’ya’ya maza a Hebron. Ɗansa na fari shi ne Amnon, ɗan Ahinowam mutuniyar Yezireyel;
3 i Kilabe, ty faharoe, nasama’ i Abigale vali’ i Nabale nte-Karmele; ty fahatelo: i Abisalome, ana’ i Maakà ana’ i Talmay mpanjaka’ i Gesore;
na biyu shi ne Kileyab, ɗan Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel; na uku shi ne Absalom, ɗan Ma’aka’yar Talmai sarkin Geshur;
4 ty fah’efatse i Adonià, ana’ i Kagite; ty faha-lime, i Sefatià ana’ i Abitale;
na huɗu shi ne Adoniya, ɗan Haggit; na biyar shi ne Shefatiya, ɗan Abital;
5 vaho ty faha-eneñe, Itreame, amy Eglà vali’ i Davide. Songa nasama’ i Davide e Kebrone ao.
na shida kuma shi ne Itireyam, ɗan Egla matar Dawuda. An haifi waɗannan wa Dawuda a Hebron.
6 Ie nitolom-pialy avao ty anjomba’ i Saole naho ty an­jom­ba’ i Davide, le nampaozam-batañe añ’ anjomba’ i Saole t’i Abnere.
Sa’ad da ake yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda, sai Abner ya yi ta ƙarfafa matsayinsa a gidan Shawulu.
7 Nisakeza’ i Saole t’i Ritspà anak’ ampela’ i Aià. Le hoe t’Isbosete amy Abnere, Ino ty nimoaha’o amy sakezan-draekoy?
To, Shawulu yana da ƙwarƙwarar da ake kira Rizfa,’yar Aiya. Sai Ish-Boshet ya ce wa Abner, “Don me kake kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?”
8 Nampiforoforo i Abnere i enta’ Isbosete zay, le hoe re: Lohan’ amboa’ Iehoda hao iraho? Niferenaiñako anindroany hao ty anjomba’ i Saole, rae’o, naho o longo’eo naho o rañe’eo, te ihe tsy naseseko am-pità’ i Davide; t’ie nasisì’o ho aman-kakeo amy rakembay androany?
Abner ya husata saboda abin da Ish-Boshet ya ce, sai ya ce, “Kana tsammani ni mai cin amana ne? Kana zato ni mai goyon bayan Yahuda ne? Tun farko na nuna aminci ga gidan babanka Shawulu, da’yan’uwansa, da abokansa! Ban kuwa ba da kai a hannun Dawuda ba. Ga shi yanzu a kan mace za ka ga laifina?
9 Ee te hanoen’ Añahare amy Abnere naho mandikoatse, naho tsy hanoeko ty nifanta’ Iehovà amy Davide;
Allah yă yi wa Abner hukunci mai tsanani, in ban goyi bayan Dawuda ya sami abin da Ubangiji ya yi masa alkawari da rantsuwa ba.
10 ty hampamindrañe boak’ añ’anjomba’ i Saole i fifeheañey naho hampitroareñe ambone’ Israele naho Iehoda boake Dane pake Beersevà ty fiambesa’ i Davide.
Zan kuma mayar wa Dawuda sarautar gidan Shawulu, in kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila, da kan Yahuda tun daga Dan har zuwa Beyersheba.”
11 Tsy nahavale i Abnere ndra volan-draike re amy fihembaña’ey.
Ish-Boshet bai ƙara yin karambanin ce wa Abner kome ba, gama yana tsoronsa.
12 Nañitrik’ amy Davide amy zao t’i Abnere nanao ty hoe: An’ ia o taneo? naho ty hoe: Mifañinà amako fa inao, ama’o ty tañako hanese Israele iaby.
Sai Abner ya aiki manzanni a madadinsa wurin Dawuda su ce masa, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi yarjejjeniya da ni, zan kuwa taimake ka, in juye dukan Isra’ila zuwa ɓangarenka.”
13 Le hoe re, Antao arè, hifañina; fe hafantoko ama’o, te tsy ho isa’o ty tareheko naho tsy endese’o heike t’i Mikale anak’ ampela’ i Saole, t’ie miheo mb’ amako mb’etoa hañisake ty tareheko.
Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi yarjejjeniya da kai, amma fa ina bukata abu guda daga gare ka, kada ka zo gabana in ba tare da matata Mikal,’yar Shawulu ba.”
14 Le nañitrik’ am’ Is’bosete ana’ i Saole t’i Davide nanao ty hoe: Aseseo amako i Mikale tañanjombako nifofoeñ’ añ’ ofon-te-Pilisty zatoy.
Sai Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-Boshet ɗan Shawulu cewa, “Ka ba ni matata Mikal wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari na Filistiyawa.”
15 Aa le nampihitrife’ Isbosete vaho rinambe’e amy Paltiele ana’ i Laise, vali’ey.
Sai Ish-Boshet ya ba da umarni, aka kuwa ɗauke ta daga gidan mijinta Faltiyel ɗan Layish.
16 Nangololoike ty rovetse i vali’ey, ie nañorik’ aze mb’e Bakorime mb’eo. Le hoe t’i Abnere ama’e: Akia, iamboho; le nimpoly re.
Amma mijin ya raka ta, yana tafe yana kuka, ya bi ta har Bahurim. Sai Abner ya ce masa, “Koma gida!” Sai ya koma.
17 Ie amy zao fa nifañaoñe amo talè’ Israeleo t’i Abnere, nanao ty hoe: Ie taolo ro nipay i Davide ho mpanjaka hifehe anahareo,
Abner ya tattauna da dattawan Isra’ila ya ce, “An daɗe kuna nema ku naɗa Dawuda sarkinku.
18 Aa le ano henaneo; amy te nafè’ Iehovà amy Davide ty hoe: Ty fitàm-pitoroko Davide ty handrombahako ondatiko Isra­eleo am-pità’ o nte-Pilistio, naho am-pità’ o rafelahi’ iareo iabio.
To, yanzu sai ku yi haka! Gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta wurin bawana Dawuda zan ceci mutanena Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da kuma hannun dukan abokan gābansu.’”
19 Tinaro’ i Abnere an-dravembia i Beniamine ka izay, le nañavelo t’i Abnere nisaontsy an-dravembia’ i Davide e Kebrone ao t’ie ninò’ Israele iaby naho ty anjomba’ i Beniamine iaby;
Abner kuma ya yi magana da mutane Benyamin da kansa. Sa’an nan ya tafi Hebron yă gaya wa Dawuda ko mene ne Isra’ila da kuma dukan gidan Benyamin suke so su yi.
20 le nimb’ amy Davide e Kebrone añe t’i Abnere rekets’ ondaty roapolo vaho nanoa’ i Davide sabadidake t’i Abnere naho ondaty nindre ama’eo.
Sa’ad da Abner wanda yake tare da mutane ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda ya shirya masa liyafa tare da mutanensa.
21 Le hoe t’i Abnere amy Davide: Hiongake iraho hiavotse le hatontoko amy talèko mpanjakay t’Israele iaby, hifañina ama’o, hifeleha’o ze satrin’arofo’o iaby. Aa le nirahe’ i Davide mb’eo t’i Abnere hañavelo am-panintsiñañe.
Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Bari in tafi nan da nan in tattara dukan Isra’ila wa ranka yă daɗe, sarki, saboda su yi alkawari da kai, ka kuma ka yi mulki bisa dukansu yadda ranka yake so.” Saboda haka Dawuda ya sallami Abner, ya kuwa tafi lafiya.
22 Ingo te boak’ an-kotakotak’ añe amy zao o mpitoro’ i Davideo naho Ioabe, ninday fikopaham-bey; fe tsy amy Davide e Kebrone ao t’i Abnere, ie niraheñe añe naho niavotse an-kanintsiñe.
Ba a jima ba sai mutanen Dawuda da Yowab suka dawo daga hari. Suka kawo ganima da yawa tare da su. Abner kuwa ya riga ya bar Dawuda a Hebron, domin Dawuda ya sallame shi, shi kuma ya tafi lafiya.
23 Aa ie pok’eo t’Ioabe naho i valobohòke nindre ama’e iabiy, le natalily am’ Ioabe ty hoe: Fa niheo amy mpanjakay t’i Abnere ana’ i Nere vaho nampiavote’e mb’eo le nienga am-panintsiñañe.
Sa’ad da Yowab da dukan sojoji suka dawo, aka gaya masa cewa Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya sallame shi, ya kuma tafi lafiya.
24 Aa le nomb’ amy mpanjakay t’Ioabe nanao ty hoe: Ino ze o nanoe’oo? Inao niheo mb’ama’o mb’etoa t’i Abnere; akore te ni­rahe’o mb’eo, ie vata’e añe?
Sai Yowab ya je wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka. Don me ka ƙyale shi yă tafi? Ga shi kuwa ya tafi!
25 Fohi’o t’i Abnere ana’i Nere, te nimb’ etoa hama­ñahy azo, hahafohiñe ty fiengà’o naho ty fiziliha’o, haharendreha’e ze anoe’o iaby.
Ka san Abner ɗan Ner ya zo ne yă ruɗe ka, yă ga fitarka da shigarka, yă kuma binciki kome da kake yi.”
26 Ie niavotse amy Davide t’Ioabe le nampihitrike ìrak’ amy Abnere nampibalike aze boake Bor’sirà; fe tsy nifohi’ i Davide.
Yowab ya tashi daga gaban Dawuda ya tafi ya aika manzanni su bi Abner. Suka same shi a rijiyar Sira suka komo da shi, Dawuda kuwa bai sani ba.
27 Aa ie nimpoly mb’e Kebrone mb’eo t’i Abnere, le natola’ Ioabe hisitak’ i lalam-beiy hibisibisiha’e vaho tinombo’e ambane-pa’e fahalime, le nihomake ty amy lion-drahalahi’e Asaeley.
To, da Abner ya komo Hebron, Yowab ya ratse da shi zuwa hanyar shigar gari kamar zai gana da shi a kaɗaice. Amma a can ya soki Abner a ciki, ya kashe shi don yă rama mutuwar ɗan’uwansa Asahel.
28 Ie jinanji’ i Davide le hoe re, Malio tahiñe am’ Iehovà, amy lio’ i Abnere ana’ i Nerey iraho naho ty fifeheako.
Daga baya, Dawuda ya ji labarin sai ya ce, “Ni da masarautata har abada ba mu da laifi a gaban Ubangiji game da jinin Abner ɗan Ner.
29 Ee te hipetak’ añambone’ Ioabe naho añ’ anjomban-drae’e le tsy hasitak’ ami’ty anjomba’ Ioabe ty aman-dio-lava, ke ty angamae, he ty miato am-pitoñoñe, ke ty ampitsingorom-pibara, he ty tsy aman-kàneñe.
Alhakin jininsa yă kasance a kan Yowab da kuma a kan dukan iyalin mahaifinsa! Kada gidan Yowab yă rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko mai jingina ga sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko kuma wanda ba shi da abinci.”
30 Vinono’ Ioabe naho i rahalahi’e Abisaiy t’i Abnere ty amy namonoa’e i rahalahi’ iareo Asaele an-kotakotake e Gibone añe.
(Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner don yă kashe ɗan’uwansu Asahel a yaƙin Gibeyon.)
31 Le hoe t’i Davide am’ Ioabe naho amo hene ondaty nindre ama’eo, Mandriata saroñe naho misikina gony vaho miroveta añatrefa’ i Abnere. Le nañorike i horantsañey t’i Davide.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku yayyage rigunarku, ku sa tsummoki, ku yi tafiya kuna kuka a gaban Abner.” Sarki Dawuda kansa ya bi masu ɗauke da gawar daga baya.
32 Nalente’ iereo e Kebrone ao t’i Abnere; le naonjo’ i mpanjakay ty fiarañanaña’e nangololoike ty rovetse an-kibori’ i Abnere eo vaho fonga nangoihoy ondatio.
Suka binne Abner a Hebron, sarki kuwa ya ɗaga murya ya yi kuka a kabarin Abner.
33 Aa le nandala i Abnere i mpanjakay, ami’ty hoe: Nihomake manahake ty fikenkañan-dagola t’i Abnere?
Sarki ya kuma yi wannan waƙar makoki domin Abner ya ce, “Daidai ne Abner yă mutu, kamar yadda marasa bin doka suke mutuwa?
34 Tsy nisingoreñe o fità’oo, tsy ni-an-dongoke o fandia’oo; nikorovoke hoe ondaty zinevo añatrefa’ o lo-tserekeo. Le niroveta’ ondatio indraike.
Hannuwanka ba a daure suke ba, ƙafafunka ba a tabaibaye suke ba. Ka mutu kamar waɗanda suke mutuwa a hannun mugaye.” Sai dukan mutane suka sāke fashe da kuka saboda shi.
35 Nimb’ amy Davide amy zao ondatio nanjotso mofo, ie mbe niantoandro, fe nifanta ami’ty hoe t’i Davide; Hanoen’ Añahare amako ndra losore’e naho mi­tsopeke mofo ndra inoñe am-para’ te tsofotse i àndroy.
Sa’an nan duk suka zo suka roƙi Dawuda yă ci wani abu tun rana ba tă fāɗi ba; amma Dawuda ya rantse ya ce, “Bari Allah yă hukunta ni, in na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta fāɗi!”
36 Nihaoñe’ ondatio izay le ninò’e; niantofa’ ondaty iabio ze nanoe’ i mpanjakay.
Dukan mutane suka lura suka kuma ji daɗi ƙwarai, tabbatacce kome da sarki ya yi, ya gamshe su.
37 Aa le nifohi’ ze hene ondaty naho Israele iaby amy andro zay te tsy nampivetraha’ i mpanjakay t’i Abnere ana’ i Nere.
Saboda haka a ranar dukan mutane da dukan Isra’ila suka gane sarki ba shi da hannu a kisan Abner ɗan Ner.
38 Le hoe i mpanjakay amo mpitoro’eo: Tsy fohi’ areo hao te nihotrake e Israele ao anindroany ty roandria fanalolahy?
Sa’an nan sarki ya ce wa mutanensa, “Ba ku gane cewa ɗan sarki kuma babban mutum ya mutu a ƙasar Isra’ila a yau ba?
39 Mamake iraho androany, ie vaho norizañe ho mpanjaka; toe loho gañe amako i ana’ i Tseroià rey; ehe ho vale’ Iehovà amy raty tserekey o hatsivokara’eo.
A yau, ko da yake ni naɗaɗɗen sarki ne, duk da haka na raunana, kuma waɗannan’ya’yan Zeruhiya sun fi ƙarfina. Ubangiji yă sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata!”

< 2 Samoela 3 >