< 2 Samoela 18 >

1 Niahe’ i Davide amy zao ondaty nindre ama’eo, vaho najado’e am’ iereo ty mpifelek’ arivo naho mpifehe zato.
Dawuda ya tattara mutanen da suke tare da shi, ya naɗa musu komandodi na dubu-dubu, da na ɗari-ɗari.
2 Nirahe’ i Davide mb’eo, am-banem-pità’ Ioabe, ty fahatelo’ ondatio naho ambanem-pità’ i Abisaý ana’ i Tseroia rahalahi’ Ioabe ty faha­telo’e vaho ambanem-pità’ Itaie nte-Gate ty faha­telo’e. Le hoe i mpanjakay am’on­datio, toe hindre hionjo ama’ areo ka iraho.
Dawuda ya sa rundunoni kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Yowab, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Abishai, ɗan’uwan Yowab ɗan Zeruhiya, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Ittai mutumin Gat. Sai sarki ya ce wa rundunonin, “Tabbatacce zan tafi tare da ku.”
3 Fe hoe ondatio: Tsy hionjo mb’eo irehe, amy te tsy hahoa’ iereo te zahay ro hitriban-day añe, aa ndra te mivetrake ty vaki’ay, tsy ho haoñe’ iereo; fa mañeva ty rai-ale ama’ay irehe: ie amy zao hàmake te zahay ro hampionjone’o hiakatse ty rova toy.
Amma mutanen suka ce, “Ba za ka fita ba; gama in ya kasance tilas mu gudu, ba za su kula da mu ba. Ko da rabinmu sun mutu, ba za su damu ba; amma kai kanka ka fi mutum dubu goma namu. Zai fi maka ka zauna a cikin gari, ka dinga aika mana da taimako.”
4 Le hoe i mpanjakay am’ iereo: Hanoeko arè ze atao’ areo hahasoa. Aa le nijohañe añ’ ila’ ty lalambey re vaho niavotse mb’eo ki-zato’e naho ki-arivo’e ondatio.
Sarki ya ce, “Zan yi duk abin da ya fi muku kyau.” Saboda haka sarki ya tsaya kusa da bakin ƙofa yayinda dukan mutane suke fitowa a ƙungiyar ɗari-ɗari da ta dubu-dubu.
5 Le linili’ i mpanja­kay t’Ioabe naho i Abisaý vaho Itaie ami’ty hoe: Ehe ano’ areo mora ty amako i ajalahiy, i Absalome. Songa jinanji’ ondatio ty namantoha’ i mpanjakay i mpifehe rey ty amy Absalome.
Sarki ya umarci Yowab, Abishai, da Ittai, ya ce musu, “Ku yi mini hankali da saurayin nan Absalom.” Dukan mutane kuwa suka ji yadda sarki yake ba wa kowane komanda umarni.
6 Aa le nipara­tsake añe ondatio hiatreatre am’ Israele; vaho tañ’ ala’ i Efraime ao i hotakotakey.
Rundunonin suka tafi zuwa fili don su yi yaƙi da Isra’ila. Aka kuwa yi yaƙi a kurmin Efraim.
7 Zinevoñ’ añatrefa’ o mpitoro’ i Davideo o ana’ Israeleo, le akore ty fanjamanañe amy andro zay kanao lahilahy ro’ale ty nivetrake.
A nan ne mutanen Isra’ila suka sha kashi a hannun mutanen Dawuda. Waɗanda suka yi rauni da kuma waɗanda suka mutu a ranar sun yi yawa, mutum dubu ashirin.
8 Fa niparaitak’ amy tane iabiy i hotakotakey vaho maro ty nabotse’ i alay te amy fibaray.
Yaƙin ya bazu a duk fāɗin ƙauyukan, abin da kurmin ya ci kawai a ranar ya fi yawan abin da aka kashe da takobi.
9 Ie nifanojo amo mpitoro’ i Davideo t’i Absalome, le niningitse amy borìke’ey t’i Absalome, naho nimb’ ambane’ ty tsampan-kobaiñe jabajaba mb’eo i borìkey, naho nazi’ i kobaiñey ty añambone’e, naho naonjo’e añi­von-dike­rañey naho ty tane toy vaho nitolom-pilay mb’eo i borìke tambane’ey.
To, Absalom ya haɗu da mutanen Dawuda. Yana hawan dokinsa, kuma yayinda dokin ya kusa kai cikin rassan babban itacen oak, sai kan Absalom ya sarƙafe a kan itacen oak ɗin. Dokin ya wuce da gudu, shi kuwa ya rataye a can yana lilo.
10 Niisa’ t’indaty Izay le nitalily am’ Ioabe, ty hoe: Inao! nitreako niradorado ami’ ty kobaiñe t’i Absalome.
Sa’ad da wani daga cikin mutanen ya gan haka, sai ya gaya wa Yowab, “Na ga Absalom yana rataye a itacen oak.”
11 Le hoe t’Ioabe amy lahilahy nitalily azey: Aa ihe nahaisak’ azey: akore t’ie tsy linafa’o mb’an-tane? fa ho nitolorako volafoty folo reke-piètse.
Yowab ya ce wa mutumin da ya ba shi labarin, “Mene! Ka ga shi? Don me ba ka buge shi har ƙasa nan da nan ba? Ai, da na ba ka shekel goma na azurfa da abin ɗamarar jarumi.”
12 Fe hoe indatiy am’ Ioabe: Ndra te ho nandrambe volafoty arivo an-tañako, tsy ho nahitiko mb’amy ana-dahi’ i mpanjakaiy ty tañako, fa am-pijanjiña’ay ty namantoha’ i mpanjakay ama’o naho amy Abisaý vaho am’ Itaie ty hoe: Mitaoa hera eo ty hitsapa i ajalahy Absalomey.
Amma mutumin ya ce wa Yowab, “Ko da za a auna mini azurfa dubu a hannuna, ba zan miƙa hannuna in taɓa ɗan sarki ba. A kunnuwanmu fa sarki ya umarce ka, da Abishai, da Ittai cewa, ‘Ku tsare saurayin nan Absalom a madadina.’
13 Aa le ho nanoeko afero mamitak’ ate ty vatako, ie tsy ietahañe amy mpanjakay, le ihe ka ho niatreatre ahy.
Da na yi haka da na sa kaina a halin ƙaƙa-ni-ka-yi, kuma babu abin da zai ɓoyu ga sarki, kai kuwa za ka janye abinka daga gare ni.”
14 Aa le hoe t’Ioabe: Tsy hihene­kenek’ ama’o atoy iraho. Le ninday ana-pale telo am-pità’e vaho natrofa’e añ’ arofo’ i Absalome, ie mbe niveloñe amy kobaiñey.
Yowab ya ce, “Ba zan ɓata lokaci da kai ba.” Saboda haka sai ya ɗauki māsu uku a hannunsa ya zura su a ƙahon zuciyar Absalom, tun Absalom yana da sauran rai a maƙale a itacen oak.
15 Niarikoboñe aze amy zao ty ajalahy folo mpi­tàm-pikala’ Ioabe, naho linafa’ iareo t’i Absalome, toe navetra’ iareo.
Masu ɗaukan kayan yaƙin Yowab goma kuwa sun kewaye Absalom, suka bubbuge shi suka kashe.
16 Aa le pinopò’ Ioabe i antsivay, vaho nibalik’ ami’ty fañoridañañe Israele ondatio; nitana’ Ioabe ondatio.
Sa’an nan Yowab ya busa ƙaho, sai sojoji suka bar fafaran Isra’ila, gama Yowab ya tsai da su.
17 Rinambe’ iareo t’i Absalome naho navokovoko ami’ty koboñe jabajaba añ’ala ao le nampitoabora’ iareo ty votrem-bato folo-ay vaho songa nitriban-day mb’an-kibo­ho’e mb’eo t’Israele.
Suka ɗauki Absalom, suka jefa shi cikin wani babban rami a kurmin, suka kuwa tula tsibin duwatsu a kansa. Ana cikin haka, sai dukan Isra’ilawa suka tsere zuwa gidajensu.
18 Natroa’ i Absalome, ie mbe niveloñe, ty vatolahy añ’ ala-vondrom-panjaka ao ho am-bata’e, ami’ty hoe: Tsy manañe anadahy iraho hitiahiañe ty añarako; vaho nitokave’e ami’ty añara’e i vatoy; le atao ty hoe Vatolahi’ i Absalome pak’ androany.
A lokacin da Absalom yake da rai, Absalom ya gina wa kansa al’amudin tunawa, a Kwarin Sarki, gama ya yi tunani ya ce, “Ba ni da ɗa namiji wanda zai sa a riƙa tunawa da ni.” Sai ya kira ginshiƙin da sunansa, ana kuwa kira shi Al’amudin Absalom har wa yau.
19 Aa le hoe t’i Akimatse ana’ i Tsa­doke: Angao hilaisako hitalily amy mpanjakay, te vinale’ Iehovà fate o rafelahi’eo.
Ahimawaz ɗan Zadok ya ce, “Bari in ruga in kai wa sarki labari cewa Ubangiji ya cece shi daga hannun abokan gābansa.”
20 Le hoe t’Ioabe ama’e: Tsy hinday talily irehe te anito, fa andro hafa ty hindesa’o talily; kanao nihomake ty ana-dahi’ i mpanjakay tsy ho talilie’o te anito.
Yowab ya ce, “Ba kai ba ne za ka kai wannan labari a yau ba. Kana iya kai labarin wani lokaci, amma yau kam ba zai yiwu ba, saboda ɗan sarki ya mutu.”
21 Aa le hoe t’Ioabe amy nte-Kosiy: Akia, atalilio amy mpanjakay o niisa’oo. Niondrek’ amy Ioabe i nte-Kosiy vaho nihitrihitry mb’eo.
Sai Yowab ya ce wa wani mutumin Kush, “Je ka faɗa wa sarki abin da ka gani.” Mutumin Kush ɗin kuwa ya rusuna wa Yowab, sai ya ruga a guje.
22 Le hoe t’i natovo’ i Akimatse ana’ i Tsa­doke am’ Ioabe: Ndra te ino ty hifetsake, miambane ama’o, ehe adono hañeañe i Kosiy iraho. Le hoe t’Ioabe: Ino ty hilaisa’o, anako, ihe tsy handrambe tambe amy taliliy?
Ahimawaz ɗan Zadok ya sāke ce wa Yowab, “Ko mene ne zai faru, ina roƙonka bari in bi bayan mutumin Kush nan.” Amma Yowab ya ce, “Ɗana me ya sa kake so ka je? Ba ka da labarin da zai jawo maka lada.”
23 Ndra ino ty hizò, hoe re, Hilay iraho. Le hoe re ama’e: Milaisa. Aa le nihere­reake mb’ amontoñe t’i Akimatse vaho nilosore’e i nte-Kosiy.
Ya ce, “Ko mene ne zai faru, ina so in ruga da gudu.” Sai Yowab ya ce, “Ruga!” Sai Ahimawaz ya sheƙa a guje ya bi ta hanyar fili ya riga mutumin Kush nan.
24 Ie amy zao, niambesatse añivo’ ty lalambey roe eo t’i Davide; le ie nanganike mb’ an-tafon-dalambey ambone’ i kijoliy mb’eo ty mpijilo naho nampiandra fihaino naho nitalake, le naheo’e te ingo ty lahilahy milay mb’eo ie raike.
Yayinda Dawuda yake zaune tsakanin ƙofofin ciki da na waje, sai mai tsaro ya hau rufin ginin da yake kan hanyar shiga ta wajen katanga. Da ya duba sai ya ga wani mutum shi kaɗai yana gudu.
25 Nikaik’ amy zao i mpijiloy, nitalily amy mpanjakay: Le hoe i mpanjakay: Kanao mirery re, minday talily am-palie. Aa le niharine mb’eo re.
Mai tsaro ya tā da murya ya faɗa wa sarki. Sarki ya ce, “In shi kaɗai ne, ya kawo labari mai kyau ke nan.” Mutumin ya matso kusa-kusa.
26 Nahaisake mpihitrihitry raike ka i mpijiloy: le nikaihe’e ty hoe i mpigarin-dalañey: Heheke ondaty raike ka ty mihitrike mb’etoa. Le hoe i mpanjakay: Minday talily ka re.
Sai mai tsaron ya ga wani mutum yana zuwa a guje. Sai ya tā da murya ya kira mai tsaron ƙofa ya ce, “Duba, ga wani mutum kuma yana gudu shi kaɗai!” Sarki ya ce, “Shi ma yana kawo labari mai daɗi ne.”
27 Le hoe i mpijiloy: Ataoko ho filaisa’ i Akimatse ana’ i Tsadoke i miaoloy. Le hoe i mpanjakay: Ondaty mora minday talily soa izay.
Sai mai tsaron ya ce, “A ganina gudu na farin, ya yi kama da gudun Ahimawaz, ɗan Zadok.” Sarki ya ce, “Shi mutumin kirki ne, yana zuwa da saƙo mai kyau.”
28 Nikoike t’i Akimatse, le hoe re amy mpanjakay, Tsy mañahy. Le nidrakadrakak’ añatrefa’ i mpanjakay re nanao ty hoe: Andriañeñe abey t’Iehovà Andrianañahare’o, i nampilesa ondaty nañonjo-haok’ amy talèko mpanjakaio.
Sai Ahimawaz ya tā da murya ya ce wa sarki, “Kome lafiya yake!” Sai ya rusuna har ƙasa a gaban sarki ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka! Ya ba da mutanen da suka tayar wa ranka yă daɗe a hannunsa.”
29 Le hoe i mpanjakay: Mbe tsy mañahy hao i ajalahy Absalomey? Le hoe ty natoi’ i Akimatse: Ie nañitrike o mpitoro’oo t’Ioabe, le nahatrea fivoamboan-dra’elahy iraho fa tsy apotako ty tali’e.
Sai sarki ya ce, “Saurayin nan Absalom yana nan da rai?” Ahimawaz ya ce, “Na ga wani babban rikicewar a daidai lokacin da Yowab yake gab da aikan bawan sarki da kuma ni, sai dai ban san ko mene ne ba.”
30 Le hoe i mpanjakay, Misitsira mb’etoa, le mijohaña ey. Aa le niveve re, nijohañe.
Sai sarki ya ce, “Koma gefe ka jira a can.” Sai ya ja gefe ya tsaya.
31 Ingo te niheo mb’eo amy zao i nte-Kosiy; le hoe i nte-Kosiy: Talily ho a i talèko mpanjakay; fa vinale’ Iehovà fate ty azo anindroany amo nitroatse ama’o iabio.
Sai ga mutumin Kush ya iso ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, ka ji labari mai kyau! Ubangiji ya cece ka yau daga dukan waɗanda suka tayar maka.”
32 Le hoe i mpanjakay amy Kosiy: Mbe janga hao i ajalahi’ Absalomey?’ Aa hoe ty natoi’ i Kosy: Ee te hanahake i ajalahiy ze hene rafelahi’ i talèko mpanjakay naho ze miatreatre azo hijoy.
Sarki ya ce wa mutumin Kush, “Saurayin nan Absalom, yana nan lafiya?” Mutumin Kush ya ce, “Allah yă sa abokan gāban ranka yă daɗe, da duk waɗanda suka tayar maka da mugunta, su zama kamar saurayin nan.”
33 Nininininy amy zao i mpanjakay vaho nañambone mb’ an-traño ambone’ i lalañey mb’eo nirovetse, le nanao ty hoe t’ie nimb’eo: O Absalome anako, tiriko, o Absalome anako! ee te izaho ty nisolom-pihomake ho azo ry Absalome amoriko, anako!
Sai gaban sarki ya faɗi. Ya haura zuwa ɗakin da yake kan katangar hanyar shiga ya yi kuka. Yayinda yake tafiya ya ce, “Ya ɗana Absalom! Ɗana, ɗana Absalom! Da ma a ce ni ne na mutu maimakonka. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”

< 2 Samoela 18 >