< 2 Samoela 11 >

1 Ie an-tsam-pamalihan-taoñe, i sam-piavotam-panjaka hihotakotakey, le nirahe’ i Davide t’Ioabe, rekets’ o mpitoro’eo, naho Israele iaby; le rinotsa’ iereo o ana’ i Amoneo vaho niarikatohe’ iereo t’i Ramà. F’ie ni­tambatse e Ierosa­laime ao t’i Davide.
Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
2 Aa teo ty hariva te nitroatse am-pandrea’e t’i Davide, naho nidrai­draitse an-tafon’ anjomba’ i mpanjakay; ie an-tafo ey ro naha­talake ty rakemba niandro; nimontramontra i rakembay, hasoa-vintañe.
Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
3 Nampañitrike hañontane i rakembay t’i Davide. Le hoe re: Tsy ie hao i Batesevae, ana’ i Eliame, tañanjomba’ i Orià nte-Kite?
Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
4 Aa le nampihitrife’ i Davide; ie niheo mb’ama’e ao, niolora’e, aa ie fa nañefe-batañe amy haleora’ey ro nimpoly añ’anjomba’e ao.
Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
5 Nia­reñe i rakembay vaho nirahe’e amy Davide ty hoe: Mivesatse iraho.
Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
6 Aa le nafanto’ i Davide amy Ioabe ty hoe: Iraho mb’amako mb’etoa t’i Orià nte-Kite. Aa le nirahe’ Ioabe mb’ amy Davide t’i Orià.
Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
7 Aa ie pok’ ama’e t’i Orià, le nañontanea’ i Davide te nanao akore t’Ioabe, naho ondatio naho i fañotakotaha’ i aliy.
Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
8 Le hoe t’i Davide amy Orià: Akia, mizotsoa mb’añ’ akiba’o mb’eo, naho manasà fandia. Aa le niavotse añ’ anjomba’ i mpanjakay t’i Orià vaho nampañoriheñ’ aze ty mahakama, ravoravo boak’ amy mpanjakay.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
9 Fe nirotse an-dalan’ anjomba’ i mpanjakay t’i Orià mindre amo mpitoro’ i talè’ey iabio vaho tsy nizotso mb’ añ’anjomba’e mb’eo.
Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
10 Aa ie natalily amy Davide ty hoe: Tsy nizotso mb’añ’ an­jom­ba’e mb’eo t’i Orià. Le hoe t’i Davide amy Orià, Tsy vaho nihirik’ an-dia-lava v’iheo? Aa vaho akore t’ie tsy nizotso mb’ añ’an­jomba’o mb’eo?
Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
11 Le hoe t’i Orià amy Davide: Songa mimoneñe an-kibohotse i vatam-pañinay, naho Israele, vaho Iehodà; mbore mitobe an-kivok’ ey t’Ioabe talèko mindre amo mpitoron-talèkoo; aa le himoak’ añ’ anjombako ao hao iraho hihinañe naho hinoñe, vaho handre amy valikoy? Kanao velon-drehe naho veloñe ty arofo’o, tsy hanoeko.
Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
12 Le hoe t’i Davide amy Orià: Mahaliñisa atoy hey te anito, le hengako hiavotse te maray. Aa le niambesatse e Ierosalaime ao t’i Orià amy andro zay; le ie loakandro
Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
13 nikanjie’ i Davide naho nikama naho ninoñe ama’e; vaho nimamoe’e; le niakatse añe re te hariva nandre am-pandreañe mindre amo mpitoro’ i taleio, fe tsy nizotso mb’ añ’ anjomba’e mb’eo.
Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
14 Aa ie maraiñe, nanokitse taratasy am’ Ioabe t’i Davide, vaho nampisangitrifa’e am-pità’ i Orià.
Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
15 Le hoe ty sinoki’e amy taratasiy: Apoho aolo amy hotakotake miforoforoy t’i Orià, le isitaho, soa t’ie ho fofoheñe hivetrake.
A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
16 Ie amy zao, naho nisary i aliy t’Ioabe le nafanto’e hitoetse amo fanalolahio t’i Orià.
Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
17 Aa le niavotse ondati’ i rovaio, nifandraparapak’ am’ Ioabe; nitsin­goro eo ty ila’ ondatio, naho ty ila’ o mpitoro’ i Davideo; vaho nihomake ka t’i Orià nte-Kite.
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
18 Le nañirake t’Ioabe naho nita­lily i aliy amy Davide;
Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
19 le hoe ty nafanto’e amy nampihitrifa’ey: Ie fa nitalilie’o amy mpanjakay i aly iabiy,
Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
20 naho miforoforo ty haviñera’ i mpanjakay, manao ama’o ty hoe: Aa vaho akore t’ie niheo mb’eo hialy marine i rovay hoe zao? Tsy nifohi’ areo t’ie hitifitse boak’ ambone’ i kijoliy ey?
wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
21 ia ty nañoho-doza amy Akimelek’ ana’ Ierobesete? tsy roakemba hao ty nametsake vato-fandisanañe-ambone ama’e boak’ an-kijoly ey nampihomak’ aze e Tebetse añe? Aa vaho manao akore te niharinea’ areo i rindriñey? le hoe ty hatao’o: Nihomake ka i mpitoro’o Orià nte-Kitey.
Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
22 Aa le nimb’eo i nafantokey vaho natalili’e amy Davide iaby i nampañitrife’ Ioabe azey.
Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
23 Le hoe i ìrakey amy Davide: Toe naname anay ondatio naho niakatse mb’ ama’ay an-kivoke ey fe nampolie’ay pak’ am-pimoahañe an-dalam-bey eo.
Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
24 Le hiniriri’ o mpitàm-paleo o mpitoro’oo boak’ amy kijoliy, naho amo mpitoro’ i mpanjakaio ty nivetrake, vaho nihomake ka t’i Orià nte-Kite mpitoro’oy.
Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
25 Aa le hoe t’i Davide amy nihitrikey: Ty hoe ty ho enta’o am’ Ioabe: Ehe te tsy hampioremeñe azo o raha zao fa tsy mete tsy mampibo­tseke mb’eo mb’eo avao i fibaray; ampaozaro ty fihotakotaha’o amy rovay vaho rotsaho. Osiho re.
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
26 Ie jinanji’ i tañanjomba’ i Oriày te vilasy t’i Orià vali’e le nandala’e.
Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
27 Ie añe i fandalà’ey le nahitri’ i Davide ty holia’e añ’anjomba’e ao naho nengae’e ho vali’e vaho nisamak’ ana-dahy ho aze. Fe tsy ninò’ Iehovà i nanoe’ i Davidey.
Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.

< 2 Samoela 11 >