< 2 Mpanjaka 22 >

1 Valo taoñe t’Iosià te namototse nifeleke, vaho nifehe telopolo taoñe raik’ amby e Ierosalaime ao. Iedidae, anak’ ampela’ i Adaià nte-Bots’kate, ty tahinan-drene’e.
Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
2 Nanao soa am-pivazohoa’ Iehovà re naho nañavelo an-tsata’ i Davide rae’e vaho tsy nitsile mb’an-kavana ndra mb’ankavia.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
3 Ie amy taom-paha-folo-valo-ambi’ Iosià mpanjakay, le nampihitrife’ i mpanjakay t’i Safane, ana’ i Atsaliaho ana’ i Meso­lame mpanokitse mb’ añ’ anjomba’ Iehovà mb’eo, ami’ty hoe:
A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
4 Akia mb’amy Kilkià mpisoroñe hamolily o volafoty fa nasese añ’anjomba’ Iehovào, o natonto’ o mpañambin-dalambeio am’ ondatioo;
“Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
5 le ampanesefo am-pità’ o mpanao i fitoloñañeio, amo mpisary i anjomba’ Iehovàio; le hatolo’ iereo amo mpifanehak’ añ’ anjomba’ Iehovào hamboareñe o vakivaky amy anjombaio;
Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
6 amo mpandranjio, naho amo mpamboatseo naho amo mpan­dranjy vatoo naho hiviliañe hatae naho vato pinèke hampisomontieñe i anjombay,
wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
7 vaho tsy ampivolilieñe o tolorañe i drala am-pitañeio, amy te matoe ty fitoloña’ iareo.
Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
8 Le hoe t’i Kilkià, mpisoroñe, amy Safane, mpanokitse; Nitreako añ’ anjomba’ Iehovà ao ty boke Hake. Le natolo’ i Kilkià amy Safane, vaho vinaki’e.
Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
9 Nimb’ amy mpanjakay mb’eo t’i Safane mpa­nokitse vaho nahere’e amy mpanjakay ty saontsy manao ty hoe: Fa natonto’ o mpitoroñeo o drala niisak’ añ’ anjombao vaho natolo’ iereo am-pità’ o mpitoloñe misary ty anjomba’ Iehovào;
Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
10 le tinaro’ i Safane amy mpanjakay ty hoe: Nanese boke amako t’i Kilkia mpisoroñe. Aa le nivakie’ i Safane añatrefa’ i mpanjakay.
Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
11 Ie jinanji’ i mpanjakay ty enta’ i boke Hakey, le rinia’e o saro’eo;
Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
12 le linili’ i mpanjakay t’i Kilkia mpisoroñe, naho i Akikame, ana’ i Safane naho i Akbore ana’ i Mikaià naho i Safane mpanokitse vaho i Asaià mpitoro’ i mpanjakay ami’ty hoe:
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
13 Akia, añontaneo am’Iehovà ho ahy naho ondatio naho Iehoda iaby o tsara’ i boke nioniñeio, fa akore ty haviñera’ Iehovà misolebotse amantika, ie tsy hinaon-droaen-tika o tsara ami’ty boke toio; hera fonga hanoe’e aman-tikañe o sinokitseo.
“Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
14 Aa le nimoak’ amy Koldàe mpitoky ampela, vali’ i Salome, ana’ i Tikvà, ana’ i Karkase mpañambin-tsikiñe, mpimoneñe e Ierosa­laime an-kibohom-panokiram-boke ao, t’i Kilkià mpisoroñe naho i Akikame, naho i Akbore naho i Safane vaho i Asaià, le nifañaoñe ama’e.
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
15 Le hoe re am’ iereo, Hoe t’Iehovà Andrianañahare’ Israele, Saontsio indaty nañirak’ anahareo amakoy,
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
16 Hoe ty tsara’ Iehovà: Mahaoniña te hametsahako hankàñe ty toetse toy naho o mpimoneñe ama’eo; toe ze hene enta’ i boke’ vinaki’ i mpanjaka’ Iehoday;
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
17 amy te naforintse’ iereo iraho naho nañenga aman-drahare ila’e, hanigike ty haviñerako amo satam-pità’ iareoo; aa le hisolebotse ami’ty toetse toy ty haviñerako vaho tsy hakipeke.
Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
18 Fe hoe ty ho saontsi­eñe amy mpanjaka’ Iehodà nañirak’ anahareo hañontane amy Iehovày: Hoe t’Iehovà, Andrianañahare’ Isra­ele: ty amo tsara inanji’oo,
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
19 kanao mitrotrotrotro ty arofo’o naho nireke añatrefa’ Iehovà, ie jinanji’o i vinolako ami’ ty toetse toiy naho amo mpimone’eo, t’ie ho fatra naho fatse, vaho te rinia’o o saro’oo vaho nirovetse añatrefako; le toe tsinanoko irehe, hoe t’Iehovà.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
20 Aa le oniño te hatontoko aman-droae’o irehe, le hambineñe an-kibori’o ao an-kanintsiñe, vaho tsy ho isam-pihaino’o ty hankàñe hafe­tsako ami’ty toetse toy. Aa le nahere’ iareo amy mpanjakay i entañe zay.
Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.

< 2 Mpanjaka 22 >