< 2 Mpanjaka 20 >
1 Ie amy andro rezay, natindry fa heta’e t’i Kezkià, le nimb’ ama’e mb’eo t’Iesaià, ana’ i Amotse, le nanoe’e ty hoe: Hoe ty nafè’ Iehovà: Hajario ty anjomba’o fa hihomake, tsy ho veloñe.
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da rashin lafiya har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya ɗan Amoz ya zo wurinsa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka domin za ka mutu, ba za ka warke ba.”
2 Nampitolihe’e mb’an-drindriñe ty añ’ambone’e, vaho nihalaly amy Iehovà ami’ty hoe.
Hezekiya ya juya fuskarsa wajen bango ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
3 Midrakadrakak’ ama’o ry Iehovà, tiahio hey t’ie nañavelo añ’ atrefa’o an-kavañonañe naho an-troke vantañe vaho nanao ty hasoa am-pivazohoa’o. Le nangololoike ty rovetse t’i Kezkià.
“Ya Ubangiji, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da zuciya ɗaya, na kuma aikata abin da yake daidai a gabanka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 Aa ie mbe tsy anteñateña’ i kiririsay t’Iesaià, le niheo ama’e ty tsara’ Iehovà, ami’ty hoe:
Kafin Ishaya yă bar tsakiyar filin gida, sai maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
5 Mibaliha indraike le saontsio t’i Kezkià mpifehe ondatikoo, Hoe ty nafè’ Iehovà, Andrianañahare’ i Davide rae’o, Tsinanoko i halali’oy, fa nitreako o ranom-pihaino’oo, inao te ho jangañeko, Mionjona mb’ añanjomba’ Iehovà mb’eo ami’ty andro fahatelo.
“Ka koma ka ce wa Hezekiya, shugaban mutanena, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na mahaifinka Dawuda ya ce, na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan warkar da kai. A rana ta uku daga yau za ka haura zuwa haikalin Ubangiji.
6 Le ho tovoñako taoñe folo-lime amby o andro’oo naho havotsoko am-pità’ i mpanjaka’ i Asorey, ihe naho ty rova toy, vaho harovako ho Ahy naho ho a i Davide, mpitorokoy, ty rova toy.
Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuma cece ka daga hannun sarkin Assuriya. Zan kāre birnin nan saboda kaina da kuma bawana Dawuda.’”
7 Le hoe t’Iesaià, Angalao garaton-tsakoa. Aa le nangalake le nabatra’ iereo amy honay le nisotrake re.
Sai Ishaya ya ce, “A kwaɓa ɓaure.” Sai aka yi haka, aka shafa wa marurun, ya kuma warke.
8 Le hoe t’i Kezkià am’ Iesaià, Ino ty ho viloñe te hampijangañe ahy t’Iehovà, naho himoak’ añ’ anjomba’ Iehovà ao iraho te herone?
Hezekiya ya tambayi Ishaya, “Wace alama ce za tă nuna cewa Ubangiji zai warkar da ni, kuma cewa in tafi haikalin Ubangiji kwana uku daga yanzu?”
9 Le hoe t’Iesaià, Zao ty viloñe ho azo’o am’ Iehovà, te hanoe’ Iehovà i tsinara’ey: ke hionjo miaolo fange’e folo i talinjoy, he hibalike fange folo, akore?
Sai Ishaya ya ce, “Ga alamar Ubangiji zuwa gare ka da za tă nuna cewa Ubangiji zai cika alkawarinsa. Kana so inuwa tă yi gaba da taki goma, ko tă koma baya da taki goma?”
10 Le hoe ty natoi’ i Kezkià, Raha maivañe ty hizotsoa’ i talinjoy fange’e folo: Aiy! ampibaliho fange folo i talinjoy.
“Ai, abu mai sauƙi ne inuwa tă yi gaba da taki goma.” In ji Hezekiya, “Gwamma dai tă koma baya da taki goma.”
11 Aa le kinanji’ Iesaià t’Iehovà, le nahere’e ami’ ty fange folo nizotsoa’e amy tarehem-pamatarañ’ andro i Ahkazeo i talinjoy.
Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa inuwa ta koma baya da taki goma bisa ga magwajin rana wanda Sarki Ahaz ya gina.
12 Ie henane zay, nañitrike taratasy naho ravoravo amy Kezkià t’i Berodake-baladàne, ana’ i Baladane, mpanjaka’ i Bavele; fa jinanji’e te natindry t’i Kezkià.
A wannan lokaci, Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu tare da kyauta, domin ya sami labarin rashin lafiyar Hezekiya.
13 Nihaoñe’ i Kezkià iereo, le fonga nitoroa’e o am-pañajam-bara’eo, o volafotio, naho o volamenao, naho o raha mafirio, naho o solike sarotseo naho i anjombam-pikalaña’ey, vaho ze nitendrek’ am-panontonam-bara’e ao; ndra loli’e amy anjomba’ey tsy napo’e, ndra amy fifehea’e iabiy, ze tsy natoro’ i Kezkià iareo.
Hezekiya ya karɓi jakadun, ya nuna musu dukan abin da yake a ɗakunan ajiyarsa, azurfa, zinariya, kayan ƙanshi da mai, wurin ajiye makamansa da kuma dukan abin da aka samu a ɗakin ajiyarsa. Babu wani abu a fadansa ko a dukan mulkinsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
14 Pok’ amy mpanjakay amy zao t’Iesaià mpitoky, le nanoa’e ty hoe: Ino ty enta’ indaty rey, naho boak’ aia iereo te nivotrak’ ama’o? Le hoe t’i Kezkià, toe boake tsietoitane añe iereo, hirike Bavele ao.
Sai annabi Ishaya ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya tambaye shi ya ce, “Me mutanen nan suka ce, kuma daga ina suka fito?” Sai Hezekiya ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Daga Babilon.”
15 Le hoe re: Ino ty nioni’ iereo añ’anjomba’o ao? Le hoe ty natoi’ i Kezkià, Hene niisa’ iereo ze an-trañoko ao, tsy eo ty napoko tsy natoroko.
Annabin ya yi tambaya, “Me suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Ba abin da yake a ma’ajina da ban nuna musu ba.”
16 Le hoe t’Iesaià amy Kezkià, Janjiño ty tsara’ Iehovà.
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
17 Inao! ho avy ty andro te fonga hendeseñe mb’e Bavele mb’eo o añ’ anjomba’oo, naho ze vinandron-droae’o pak’ androany; tsy eo ty hapoke, hoe t’Iehovà.
Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
18 Le haneseañe añe o tariratse hiboak’ ama’oo, o hasama’oo, ho mpiatrak’ añ’ anjombam-panjaka’ i Bavele ao.
Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
19 Le hoe t’i Kezkià am’ Iesaià, Soa i tsara’ Iehovà tinaro’oy. Ie natao’e ty hoe: Aa tsy ho soa izay! te fierañerañañe naho hatò ty ho amo androkoo?
Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka faɗa ta yi kyau.” Gama ya yi tunani cewa, “Ai, ba ni da damuwa, tun da yake za a yi zaman lafiya da salama a kwanakina.”
20 Aa naho o fitoloña’ i Kezkià ila’eo, i haozara’ey, vaho ie namboatse ty antara naho zoho nampom-ba’e rano mb’ an-drova ao; tsy misokitse amy bokem-pamoliliañe o mpanjaka’ Iehodaoy hao?
Game da sauran ayyukan mulkin Hezekiya, dukan nasarorinsa da yadda ya yi tafki da kuma bututun ruwa inda ya kawo ruwa cikin birni, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
21 Nitrao-piròtse aman-droae’e t’i Kezkià; nandimbe aze nifehe t’i Menasè, ana’e.
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa. Manasse ɗansa kuma ya gāje shi.