< 2 Korintiana 3 >

1 Mamototse maniom-batañe in­draike hao zahay? ke t’ie, manahake o ila’eo, mipay taratas-pañiniañe ho ama’areo, he taratas-pañiniañe boak’ ama’areo?
Yabon kanmu ne kuma muka fara yi? Ko kuwa muna bukatar wasiƙun yabo ne zuwa gare ku, ko daga gare ku, kamar yadda waɗansu suke yi?
2 Inahareo ro taratasi’ay pinatetse añ’ arofo’ay atoañe, fohiñe naho vakie’ ze kila ondaty,
Ai, ku kanku ku ne wasiƙarmu, wadda aka rubuta a zukatanku, domin kowa yă santa, yă kuma karanta ta.
3 ie malange te taratasi’ i Norizañe toroñe’aiy, tsy sinokitse an-dranomainte fa amy Arofon’ Añahare veloñey, tsy an-takelam-bato fa an-takelan-tro’ ondaty.
Kun nuna cewa ku wasiƙa ce daga Kiristi, sakamakon hidimarmu, ba wadda aka rubuta da inki ba, sai dai da Ruhun Allah mai rai. Ba kuma a kan allunan dutse ba, sai dai a kan allunan zukatan mutane.
4 Izay ty fatokisa’ay aman’ Añahare añamy Norizañey.
Amincewa kamar wannan shi ne namu ta wurin Kiristi a gaban Allah.
5 Tsy te zahay ro mañeva hivolañe t’ie maha-pi-draha, fa boak’ aman’ Añahare ty faha­lefea’ay,
Ba mu da wani abin da za mu nuna cewa da iyawarmu ne muke aikin nan. Iyawarmu daga wurin Allah ne.
6 Ie ka ty nampahafaritse anay ho mpitoro’ i fañina vaoy; ie tsy an-tsokitse, fa amy Arofoy; mahafate i sokitsey, fe mahaveloñe i Arofoy.
Shi ya sa muka gwaninta a matsayinmu na masu hidimar sabon alkawari ba ta rubutacciyar Dokar ba, amma ta Ruhu; don Dokar, kisa take yi, Ruhu kuwa yana ba da rai.
7 Aa naho an’ engeñe ty nitotsaha’ i fitoroñam-pihomahañe an-tsokitse pinatetse am-batoy, ie tsy nahafitalatse ty lahara’ i Mosè o ana’ Is­ra­eleo ty amy engen-dahara’ey—ie nipoa-mavo,
To, in hidimar da ta kawo mutuwa, wadda an rubuta a kan allon dutse, ta zo da ɗaukaka har Isra’ilawa suka kāsa duban fuskar Musa saboda tsananin haskenta, ko da yake mai shuɗewa ce,
8 aa tsy handikoatse izay ty enge’ o fitoroñan’ arofoo?
ashe, hidimar Ruhu ba za tă fi wannan ɗaukaka ba?
9 Ie nanañ’ engeñe ty fitoroñam-pañozoñañe, sandrake te itoboaran’ engeñe ty fitoroñan-kavañonañe.
In hidimar da take jawo wa mutane hukunci tana da ɗaukaka haka, to, lalle, hidimar da take kawo adalci za tă fi ta ɗaukaka nesa!
10 Aa naho oharañe ami’ty engeñe mitoabotse toy, le tsy aman’ engeñe henaneo i nirengèñe taoloy.
Gama abin da dā take da ɗaukaka, ba ta da ɗaukaka a yanzu, in aka kwatantata da mafificiyar ɗaukaka ta yanzu.
11 Fa naho nanañ’ engeñe i mipoa-mavoy, antsake te hanam-bolonahetse i tsy mete modoy.
In kuma aba mai shuɗewa ta zo da ɗaukaka, ashe, abin da yake dawwammame, lalle ne yă kasance da ɗaukakar da ta fi haka nesa!
12 Aa kanao izay o fitamà’aio, le ra’e­lahy ty fahavania’ay,
Da yake muna da bege irin wannan, to, muna da ƙarfin zuciya sosai ke nan.
13 f’ie tsy manahake i Mosè nikolopofa’ ty lamba marerarera an-dahara’e tsy mone hitolom-pangareke aze o ana’ Israeleo ampara’ t’ie nimavo,
Mu ba kamar Musa ba ne, wanda ya rufe fuskarsa da lulluɓi, don kada Isra’ilawa su ga ƙarewar ɗaukakan nan mai shuɗewa.
14 fe nihagàñe ty fivetsevetse’ iareo, naho mbe tsy miafake henanekeo amy famakiañe i fañina taoloy i marerareray, fa amy Norizañey ty fañahañe aze.
Amma aka sa hankulansu suka dushe, gama har yă zuwa yau akwai lulluɓin nan a duk sa’ad da ake karatun tsohon alkawari. Ba a kawar da shi ba, sai a cikin Kiristi ne kaɗai ake kawar da shi.
15 Aa ndra henaneo, ndra mb’ia mb’ia vakieñe t’i Mosè le kolopofa’ i marerareray ty arofo’ iareo.
Har yă zuwa yau, duk sa’ad da ake karatun littattafan Musa, lulluɓin nan yakan rufe zukatansu.
16 Fe naho mitolike amy Talè t’indaty, le miafake i marerareray.
Amma duk sa’ad da wani ya juyo ga Ubangiji, akan kawar da lulluɓin.
17 I Talè ‘nio i Arofoy, le añ’Arofo’ i Talè ao ty fidadàñe.
Ubangiji fa, shi ne Ruhu, kuma duk inda Ruhun Ubangiji yake, a nan’yanci yake.
18 Fe itikañe iaby, an-daharañe tsy mikolopoke, mañisake hoe an-ketsoro ty enge’ i Talè, ro hovaeñe ho hambam-bintañe ama’e aman’ engeñe itoaboran’ engeñe añamy Talè, i Arofoy.
Mu da ba mu da lulluɓi a fuskokinmu duk muna nuna ɗaukakar Ubangiji, ana sauya mu mu ɗauki kamanninsa cikin ɗaukaka mai hauhawa. Ubangiji wanda yake ruhu kuwa shi ne mai zartar da haka.

< 2 Korintiana 3 >