< 1 Timoty 1 >
1 I Paoly, Firàhe’ Iesoà Norizañey, ty amy lilin’ Añahare Mpandrombake antikañe naho Iesoà Norizañe fitamàn-tikañey,
Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin umarnin Allah Mai Cetonmu da kuma na Yesu Kiristi begenmu,
2 Ho a i Timoty, toe anako am-patokisañe: Hasoa naho fiferenaiñañe vaho fañanintsiñe boak’ aman’ Añahare Rae naho i Talèntika Iesoà Norizañey.
Zuwa ga Timoti ɗana na gaske cikin bangaskiya. Alheri, jinƙai da kuma salama daga Allah Uba da Kiristi Yesu Ubangijinmu, su kasance tare da kai.
3 Inay i nañosihako azoy, izaho nionjoñe mb’e Makedonia añe, le t’ihe hitoboke e Efesosy ao heike, handily o ila’eo tsy hañoke fañòhañe hafa,
Kamar yadda na gargaɗe ka sa’ad da zan je Makidoniya, ka zauna can Afisa domin ka umarci waɗansu mutane kada su koyar da ƙa’idodin ƙarya nan gaba
4 naho tsy ho haoñe’o o talilin-taoloo naho o toñon-droae tsy migadoñeo fa mampifandietse avao, he ho soloa’e i fañòhan’ Añahare mitoloñe am-patokisañey.
ko su ba da kansu ga tatsuniyoyi da ƙididdigar asali marar iyaka. Waɗannan suna kawo faɗa a maimakon aikin Allah wanda yake ta wurin bangaskiya.
5 Fa ty firefea’ o fanoroañeo le fikokoañe boak’ añ’arofo hiringiri’e naho hazavàn-troke miharo fatokisañe to;
Maƙasudin wannan umarnin dai ƙauna ce, wadda take zuwa daga zuciya mai tsabta da lamiri mai kyau da kuma sahihiyar bangaskiya.
6 teo ty nitsile ami’ty hiti’e naho nidrikiñe mb’ an-drehake borosode añe,
Waɗansu sun bauɗe daga waɗannan al’amura, suka koma ga maganganu marasa ma’ana.
7 ie te ho mpañoke Hake, fe tsy apota’e ndra ze rehafe’e ndra o raha vontitire’eo.
So suke su zama malaman doka, ba tare da fahimtar abin da suke faɗa ba, balle abubuwan da suke ta nacewa a kai.
8 Fohintika te soa t’i Hake naho oriheñe ami’ty lili’e,
Mun san cewa doka tana da kyau in an yi amfani da ita yadda ya kamata.
9 tsapa te tsy afetsake ami’ty vantañe t’i Hake fa ami’ty tsy mañaon-Kàke, o mpanjehatseo, o mpiolao naho o tsivokatseo; o aman-tahiñeo naho o miteraterao, ho amo mpamono rae naho reneo, o mpañoho-dozao,
Mun kuma san cewa an yi doka ba domin masu adalci ba sai dai masu tawaye, da marasa biyayya, da marasa bin Allah, da masu zunubi, da marasa tsarkaka, da masu saɓon Allah, da masu kashe iyaye maza da mata, da masu kisankai,
10 o mpañarapiloo, o sambe-lahy mpifandeotseo, o mpañovok’ ondatio, o mpandañitseo, o mpitalily vilañeo, vaho ze mpandietse fañòhañe to,
da masu zina da kuma da maza masu kwana da maza, ko mata masu kwana da mata, da masu cinikin bayi da masu ƙarya da kuma masu shaidar ƙarya, da kuma duk wani abin da ya saɓa wa sahihiyar koyarwa,
11 ty amy talili-soan’ Añahare rengeñe nafantoke amakoy.
da take bisa ga bishara mai ɗaukaka ta Allah mai albarka, wadda ya danƙa mini.
12 Andriañeko i Talèntika Iesoà Norizañey mampaozatse ahikoy, amy te natao’e ho migahiñe, vaho najado’e amy fitoroñañey,
Na gode wa Kiristi Yesu Ubangijinmu, wanda ya ba ni ƙarfi, saboda ya amince da ni, har ya sa ni aikinsa.
13 zaho nimpiteratera naho mpampisoañe vaho nimpijoy heike; fe niferenaiñañe amy te nanoeko tsy aman-kilala tsy am-patokisañe,
Ko da yake a dā ni mai saɓo da mai tsanantawa da kuma mai rikici ne, aka nuna mini jinƙai saboda na yi haka cikin jahilci ne da kuma rashin bangaskiya.
14 le nidobañe amako ty hasoa’ i Talèn-tikañey reketse ty fatokisañe naho fikokoañe am’ Iesoà Norizañey.
An zubo mini alherin Ubangijinmu a yalwace, tare da bangaskiya da ƙaunar da take cikin Kiristi Yesu.
15 Taroñe atokisañe naho mañeva fiantofañe pea, te, Nivotrake an-tane atoy t’Iesoà Norizañe handrombake o aman-kakeoo, izaho ty lombolombo’e;
Ga wata magana tabbatacciya wadda ta cancanci cikakkiyar karɓa. Kiristi Yesu ya zo duniya domin ceton masu zunubi, wanda nake mafi muni a cikinsu.
16 fe zao ty nitretrezañe ahy, ty amy hoe zay, soa te amako hey ty nampalangesa’ Iesoà Norizañey ty fahaliñisa’e do’e, hitsikombea’ o hiato ama’eo, hiveloma’e nainai’ey. (aiōnios )
Amma saboda wannan dalilin ne aka nuna mini jinƙai domin ta wurina, mafi zunubi duka, Kiristi Yesu yă iya bayyana matuƙar haƙurinsa a matsayin misali ga waɗanda za su gaskata shi su kuma sami rai madawwami. (aiōnios )
17 Ho amy Mpanjaka tsy ho modo, tsy ho momoke, tsy isakey, i Andrianañahare mahihitse tsy roe tsy teloy abey, ty asiñe naho ty engeñe nainai’e donia. Amena. (aiōn )
Bari girma da ɗaukaka su tabbata har abada abadin ga Sarki madawwami, wanda ba ya mutuwa, wanda ba a ganinsa, wanda kuma shi ne kaɗai Allah! Amin. (aiōn )
18 Inao ty fanoroañe hafantoko ama’o, ry Timoty anake, ty amo nitokiañe ama’oo, t’ie mañorike irezay ro hifañotak’ amy aly soay,
Timoti, ɗana, na ba ka wannan umarni bisa ga annabce-annabcen da aka yi a dā game da kai, domin ta wurin binsu ka iya yin yaƙi mai kyau,
19 hifahatse am-patokisañe naho an-kazavàn-troke; ie fa namoea’ o ila’eo, le nanao ty fatokisa’ iareo ho làka-nijoroboñe.
kana riƙe da bangaskiya da kuma lamiri mai kyau. Gama waɗansu mutane, saboda ƙin kasa kunne ga lamirinsu, suka lalatar da bangaskiyarsu.
20 Mpiam’ iereo t’i Himeneo naho i Aleksandro ze natoloko hioke amy mpañìnjey, tsy hiteratera.
Cikinsu kuwa akwai Himenayus da Alekzanda, waɗanda na miƙa ga Shaiɗan don su horo su bar yin saɓo.