< 1 Tesaloniana 2 >

1 Inahareo, ry longo, ro toe mahafohiñe te tsy nianto i fitiliha’aiy.
Domin ku da kanku kun sani, 'yan'uwa, cewa zuwan mu gareku, ba a banza yake ba.
2 Rendre’ areo ka t’ie nalovilovy naho nonjireñe e Filipy añe; fe nirearea aman’ Añaharen-tika nitaroñe i talili-soan’ Añaharey ama’areo ndra te niindra’ i fanjeharañey.
Kun kuma san yadda aka wulakantar damu, aka kuma kunyatar damu a Filibi, kamar yadda kuka sani. Muna nan kuwa da karfin zuciya cikin Allahnmu domin yi maku bisharar Allah cikin fama da yawa.
3 Toe tsy mifototse am-pandilarañe ndra haleorañe ndra famañahiañe ty fañosiha’ay;
Domin kuwa gargadinmu zuwa a gare ku ba gurbatacciya bace, ko cikin rashin tsarki, ba kuma ta yaudara bace.
4 fe ninòn’ Añahare ty fanolo­rañ’ anay i talili-soay; aa ie taroñe’ay le tsy t’ie hahaehake ondaty fa ho an’ Andrianañahare mpitsoke o tro’aio.
A maimako, kamar yadda Allah ya amince damu, ya kuma damka mana amanar bishararsa, haka kuma muke yin magana. Muna maganar ba domin mu gamshi mutane ba, amma domin mu gamshi Allah. Domin shi ne yake gwada zuciyarmu.
5 Fa fohi’ areo te le-lia tsy nanao kabeake an-drehake naho tsy nibatrake hanakona’ay fatitiañe (valolombeloñe t’i Andrianañahare),
Domin bamu taba yi maku dadin baki ba, ko sau daya, kamar yadda kuka sani, ko kwadayi a asirce, kamar yadda Allah shine shaidar mu.
6 mbore tsy nipay lomboke am’ondatio, ndra ama’ areo ndra amo ila’eo. Toe mete ho nañeva anay, kanao Firàhe’ i Norizañey ty nampivave anahareo,
Bamu kuma nemi daukaka daga mutane ko daga gare ku ko kuma wadansu ba. Da mun so da mun mori ikonmu a matsayin manzannin Almasihu.
7 te mone notroñe’ay hoe rakemba mampinono naho manombosombo i ana’ey.
A maimakon haka, mun kaskantar da kanmu a tsakanin ku kamar yadda uwa take ta'azantar da 'ya'yan ta.
8 Akore ty fikokoa’ay anahareo kanao nahaehake anay te tsy vaho handiva i talili-soan’ Añaharey fa hamoe-ay ami’ty fañisoha’ay.
Don haka muna da kauna domin ku, ba bisharar Allahnmu kadai muke jin dadin yi maku ba, amma harda bada rayukan mu domin ku. Domin kun zama kaunatattu ne a garemu,
9 Mete tiahi’ areo ry longo ty fitromaha’ay naho ty fifanehafa’ay; ie nitoloñe handro an-kaleñe tsy hiloetse ama’ ia’ia, nitaroñe i talili-soan’ Añaharey.
Kufa tuna, 'yan'uwa, game da aikinmu da famarmu. Dare da rana muna aiki sosai domin kada mu nawaita wa kowane dayan ku. A lokacin da muke yi maku bisharar Allah.
10 Valolombeloñe nahareo naho i Andrianañahare te niavake naho vañoñe vaho nalio-tahiñe ty fañaveloa’ay ama’areo mpiato.
Ku shaidu ne, haka ma Allah, yadda muka yi rayuwar tsarki da kuma adalci da rashin abin zargi a wajenku wadanda kuka bada gaskiya.
11 Fohi’ areo ka t’ie nañosike naho nañohò vaho nandrisike anahareo kiraikiraike hambañe ami’ty rae amo ana’eo,
Don haka kun kuma sani yadda muka rika yi da kowannenku, kamar uba da 'ya'yansa, yadda muka yi ma ku garadi da kuma karfafa ku, mun kuma shaida.
12 hañaveloa’ areo hañeva an’ Andrianañahare mpikanjy anahareo ho am-pifehea’e naho añ’enge’e ao.
Domin ku yi tafiya a hanyar da ta dace ga Allah, wanda ya kira ku zuwa ga mulkinsa da kuma daukakarsa.
13 Ie amy zao, tsy apo’ay ty mañandriañe an’ Andria­nañahare nainai’e, amy te rinambe’ areo i tsaran’ Añahare nitaroña’aiy le tsy nandrambe aze ho tsara’ ondaty, fa ami’ty vente’e t’ie tsaran’ Añahare mpifanehake ama’areo mpiato.
Domin wannan dalili ne yasa muke yi wa Allah godiya a koyaushe. Domin a lokacin da kuka karbi maganar Allah daga wurinmu wadda kuka ji, kun karbeta da gaske ba kamar maganar mutum ba. A maimako, kuka karbeta da gaskiyarta, kamar yadda take, maganar Allah. Wannan kalma kuma ita ce ke aiki a cikin ku wadanda kuka yi bangaskiya.
14 Vaho nitsikombe’ areo ry longo, o Fivorin’ Añahare am’ Iesoà Norizañey e Iehodào, ie nifeake fampisoàñañe am-pità’ o mpitrao-borizàñe ama’eo toe o Tehodao,
Domin ku 'yan'uwa, kun zama masu koyi da ikilisiyoyin Allah da ke Yahudiya cikin Almasihu Yesu. Domim kuma kun sha wahala irin tamu daga wurin mutanen kasarku kamar yadda suma suka sha a hannun Yahadawa.
15 ie songa vinono’ iareo t’Iesoà Talè naho o mpitokio, naho nandroake anay ka; ie tsy non’ Añahare vaho fonga mifandiets’ ama’ondaty,
Yahudawane suka kashe Ubangiji Yesu da sauran Annabawa, kuma Yahudawane suka koro mu, Basu gamshi Allah ba. A maimako, suna hamayya da dukkan mutane.
16 ami’ty fisebaña’ iareo anay tsy hitaroñe amo kilakila ondatio handrombake iareo, ie manovon-kakeo nainai’e, fa ho takaren-kaviñerañe am-para’e.
Sun kuma haramta mana yin magana da Al'ummai domin su sami ceto. Sakamakon haka kuwa kullum suna cika zunubansu. Fushi kuma ya afko kansu daga karshe.
17 Fe zahay, ry longo, naho fa nasitake ama’ areo hey, an-tsandriñe fa tsy añ’ arofo, le àntsake t’ie nirototse naho nisalala fatratse te hahaoniñe o lahara’ areoo,
Mu kuma, 'yan'uwa, mun rabu daku na karamin lokaci, a zahiri, ba a zuciya ba, mun kuma yi iyakar kokarinmu da marmarin ganin fuskarku.
18 fa sinda homb’ ama’ areo mb’eo; izaho Paoly mandikoatse te indraike, fe sineba’ i mpañìnjey.
Domin mun yi maramarin zuwa gareku. Ni, Bulus, ba sau daya ba, amma Shaidan ya hanamu.
19 Ia ty ho fitamà’ay, ty haèha’ay, ty kobay hiriñariñà’ay añatrefa’ Iesoà Talèntika amy fito­tsaha’ey? tsy inahareo hao?
To menene begenmu a gaba, ko murnarmu ko rawanin alfahari, a gaban Ubangijinmu Yesu a ranar zuwansa? Ko ba ku bane, da kuma sauran jama'a?
20 Eka, inahareo ro enge’ay naho haeha’ay.
Don kuwa kune daukakarmu da kuma farin cikinmu.

< 1 Tesaloniana 2 >