< 1 Petera 4 >
1 Aa kanao nilofek’ am-pañova’e i Norizañey, le adiaño ho fitalifirañe izay, amy te nijihetse tsy manao hakeo ka ty nijale an-tsandriñe,
Saboda haka, da yake Kiristi ya sha wahala a jikinsa, sai ku ma ku yi wa kanku ɗamara da irin wannan hali, gama wanda ya sha wahala a jikinsa ya gama da zunubi ke nan.
2 soa te amo andro sisa amy nofotseio, tsy hiveloma’e ka o hasijy rati’ ondatioo, fa ty satrin’ Añahare.
Ta haka, ba ya sauran rayuwarsa a kan mugayen sha’awace-sha’awacen jiki, sai dai nufin Allah.
3 Amy te nahatsàke anahareo o andro nitoloñañe amy ze fisatria’ o kilakila’ ndatio—nifanao haloloañe, hakarapiloañe, hamamoañe, fihisàn-draty, figologodrañan-divay, vaho fitalahoam-pahasive tiva.
Gama kun ɓata lokaci sosai a dā kuna yin abubuwan da masu bauta gumaka suka zaɓa su yi, kuna rayuwa cikin lalata, sha’awace-sha’awace, buguwa, shashanci, shaye-shaye da kuma bautar gumaka masu banƙyama.
4 Le hoe te ankafankafa amo mifosao t’ie tsy migodañe tsy nàhy mindre am’iereo mb’an-kaliforan-katsivokarañe ao.
Sun yi mamaki da ba kwa haɗa kai da su a yanzu, da ba kwa kutsa kai tare da su cikin irin rayuwar banzan nan, har suna zaginku.
5 F’ie tsy mahay tsy hamolily amy veka’e hizaka o veloñeo naho o vilasioy.
Amma dole su ba da lissafi gare shi wanda yake a shirye yă shari’anta masu rai da matattu.
6 Izay ty talim-pitseizañe i talili-soay amo nihomakeo, hizakañe hoe ondaty amy nofotsey vaho ho veloñe añ’arofo ao ty amy natoron’ Añaharey.
Dalilin ke nan da ya sa aka yi wa’azin bishara har ga waɗanda yanzu suke mutattu, don ko da yake an hukunta su a matsayin mutane a batun jiki, amma su rayu ga Allah a batun ruhu.
7 Fa an-titotse ty firefea’ ze he’e. Aa le miliera-vatañe vaho mijilova hahafilolofa’ areo.
Ƙarshen abubuwa duka ya yi kusa. Saboda haka ku kasance masu tunani mai kyau da masu kamunkai don ku iya yin addu’a.
8 Mandikoatse izay, imaneo fifampikokoañe, fa mahalembeke hakeo maro ty fikokoañe.
Fiye da kome, ku ƙaunaci juna sosai, domin ƙauna tana rufe zunubai masu ɗumbun yawa.
9 Mifampiantrañoa tsy aman-treotreoñe.
Ku riƙa karɓar juna ba da gunaguni ba.
10 Aa kanao songa nandrambe falalàñe le mitoloña am-pifampitoroñañe hoe mpamandroñe mahimba’ o hasoan’ Añahare ankafankafao.
Kowa yă yi amfani da kowace baiwar da ya samu don kyautata wa waɗansu, cikin aminci yana aikata alherin Allah a hanyoyi dabam-dabam.
11 Ndra iaia misaontsy le manahake t’ie misaontsy o fetsen’ Añahareo; ze mitoroñe, le ami’ty haozarañe atolon’ Añahare aze, soa te amy ze he’e, ho rengèñe t’i Andrianañahare añam’ Iesoà Norizañey. Aze ty engeñe naho ty fifeheañe nainai’e donia. Amena. (aiōn )
In wani ya yi magana, ya kamata yă yi ta a matsayin wanda yake magana ainihin kalmomin Allah. In wani yana yin hidima, ya kamata yă yi ta da ƙarfin da Allah ya tanadar, domin a cikin kome a yabi Allah ta wurin Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
12 O ry rañetse, ko ilatsa’ areo ty fitsohañe añ’afo mifetsake ama’areo, (ie famenteañe anahareo) manahake te nizò raha ankafankafa,
Abokaina ƙaunatattu, kada ku yi mamakin gwaji mai tsananin da kuke sha, sai ka ce wani baƙon abu ne yake faruwa da ku.
13 fe mirebeha t’ie mitraok’ ami’ty falovilovia’ i Norizañey, handià’ areo taroba ami’ty fiboaha’ o enge’eo.
Sai dai ku yi murna cewa kuna tarayya cikin shan wahalolin Kiristi, domin ku kai ga farin ciki mai yawa sa’ad da aka bayyana ɗaukakarsa.
14 Ie injèñe ty amy tahina’ i Norizañeiy, le mihahà, te ipetaha’ t’i Arofon-engen’ Añahare.
In an zage ku saboda sunan Kiristi, ku masu albarka ne, gama Ruhun ɗaukaka da kuma na Allah yana bisanku.
15 Ehe te tsy ama’ areo ty ho lovilovieñe t’ie mpamono ondaty, ndra mpikizo, ndra mpanao raty, ndra mitsoropoke am’ondaty mitoloñe.
In kuna shan wahala, kada yă zama don ku masu kisankai ne ko ɓarayi ko masu wani irin laifi ko kuma masu shisshigi.
16 F’ie mpiamy Norizañey, ee te tsy ho salatse, te mone mandrenge an’ Andrianañahare ty amy tsaraeñey.
Amma fa, in kuka sha wahala a matsayin ku Kirista ne, kada ku ji kunya, sai dai ku yabi Allah cewa kuna amsa wannan suna.
17 Fa tsatoke te hifotots’ amy hasavereñan’ Añaharey i zakay; aa kanao mamototse aman-tikañe, akore ty hizò o manjehatse amy talili-soan’ Añahareio?
Gama lokaci ya yi da za a fara yi wa iyalin Allah shari’a; in kuwa ya fara da mu, to, me zai faru da waɗanda ba sa biyayya da bisharar Allah?
18 Aa katao sarotse ho rombaheñe ty vantañe, akore ty hifetsak’ ami’ty tsy aman-Kake naho amy aman-kakeoy?
Kuma, “In da ƙyar masu adalci su kuɓuta, me zai faru da marasa tsoron Allah da kuma masu zunubi?”
19 Aa ze mijale amy satrin’ Añaharey, ee te hampiatoa’e aman’ Andrianamboatse migahiñey ty arofo’e, am-pitoloñan-tsoa.
Saboda haka, waɗanda suke shan wahala bisa ga nufin Allah ya kamata su danƙa kansu ga Mahaliccinsu mai aminci, su kuma ci gaba da aikata abin da yake daidai.