< 1 Mpanjaka 8 >

1 Natonto’ i Selomò amy zao o androanavi’ Israeleo, naho o mpiaolom-pifokoañeo, o roandrian’ anjomban-droaen’ ana’ Israeleo, mb’amy Selomò Mpanjaka e Ierosalaimey, hampionjoneñe i vatam-pañina’ Iehovày boak’ an-drova’ i Davide e Tsione ao.
Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
2 Aa le fonga nifanontoñe amy Selomò amy sabadidakey o nte Israeleo ami’ty saramañitse, ty volam-pahafito.
Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
3 Nimb’eo o roandria’ Israele iabio, vaho rinambe’ o mpisoroñeo i vatay.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
4 Nampionjone’ iereo i vatam-pañina’ Iehovày naho i kibohom-pamantañañey naho ze hene fanake amy kibohotsey; nampionjone’ o mpisoroñeo naho o nte-Levio.
suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
5 Niharo niaolo i vatay t’i Se­lomò mpanjaka naho i valobohò’ Israele nifamory ama’ey, le nisoroñe añondry naho añombe tsy nilefe talily ndra iake ami’ty fifamorohota’e.
sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
6 Le nendese’ o mpisoroñeo i vatam-pañina’ Iehovày mb’an-toe’e, mb’an-toe-miava’ i anjombay, mb’amy masiñe do’ey, ambane’ o ela’ i kerobe reio.
Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
7 Fa nivelare’ i kerobe rey ambone’ i toe’ i vataiy o ela’eo vaho tinako’ i kerobe rey i vatay naho o baom-pitarazoa’eo.
Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
8 Aa akore ty halava’ i baom-pitarazoañe rey kanao isake amy toe-miavakey aolo’ i toe-masiñey, f’ie tsy oniñe boak’ alafe’e ao; mbe eo irezay henanekeo.
Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
9 Vata koake re naho tsy i takelam-bato nagodo’ i Mosè ao e Korebe añe rey, ie nifañina amo ana’ Israeleo t’Iehovà, t’ie niavotse an-tane Mitsraime.
Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
10 Aa ie nivovotse boak’ amy miavakey o mpisoroñeo, le nañatseke i anjomba’ Iehovày i rahoñey;
Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
11 vaho tsy nahafijohañe eo hitoroñe o mpisoroñeo amy te na­tsafe’ ty enge’ Iehovà ty anjomba’ Iehovà.
Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
12 Aa le hoe t’i Selomò: Fa nitsarae’ Iehovà t’ie himoneñe an-drahoñe milodolodo ao.
Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
13 Toe namboarako anjomba fimoneñan-dRehe, toetse himoneña’o nainai’e donia.
ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
14 Nampitoli-daharañe am’ izao i mpanjakay, nitata i valobohò’ Israeley, vaho hene niongake i valobohò’ Israeley.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
15 Le hoe re: Andriañeñe t’Iehovà Andrianañahare’ Israele, ie ni­tsara am-palie amy Davide raeko vaho nifonire’e am-pità’e ami’ ty hoe:
Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
16 Sikal’ amy andro nampiavoteko amy Mitsraime ondatiko Israeleoy, le tsy eo ty rova nijoboñeko amo hene fifokoa’ Israeleo hañamboarako anjomba, hampipohako ty añarako, naho tsy i Davide ty jinoboko hifehe ondatiko Israeleo.
‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
17 Toe tañ’ arofo’ i Davide raeko ty hamboatse anjomba ho a i tahina’ Iehovà Andria­nañahare’ Israeley.
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
18 Fe nanao ty hoe amy Davide raekoy t’Iehovà: Amy te añ’ arofo’o ty handranjy akiba ho ami’ty añarako, le nanao soa kanao tañ’arofo’o;
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
19 fe tsy ihe ty hamboatse i anjombay, fa i ana-dahy hiboak’ an-tro’oy, ie ty handranjy ty anjomba ho ami’ty añarako.
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
20 Fa najado’ Iehovà i tsara nanoe’ey amy te nitroatse an-toe’ i Davide raeko iraho naho mitobok’ am-piambesa’ Israele eo ty amy tsara’ Iehovà, vaho namonitse ty anjomba ho a i tahina’ Iehovà Andria­nañahare’ Israeley.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
21 Le nampitoereko ao i vatay, ama’e ao i fañina’ Iehovà nanoe’e an-droaentika am-pampi­engae’e iereo an-tane Mitsraimeiy.
Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
22 Le nijohañe aolo’ i kitreli’ Iehovày t’i Selomò añatrefa’ i valobohò’ Israeley, vaho nonjone’e mb’an-dikerañe ey o fità’eo,
Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
23 nanao ty hoe: Ry Iehovà, Andrianañahare’ Israele, tsy eo t’i Andrianañahare manahak’ azo andin­dimoneñe añe ndra an-tane ambane atoy ze mahatambozòtse fañina naho ty fiferenaiñañe amo mpitoro’o mpañavelo añatrefa’o an-kaampon-trokeo;
ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
24 ie naha-tañe i tsinara’o am-pitoro’o Davide raekoy; toe tsinara’o am-palie vaho nihenefa’o am-pitàñe o isake henanekeo.
Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
25 Ie amy zao, ry Iehovà, Andrianañahare’ Israele, afaharo amy mpitoro’o Davide raekoy, i tsinara’o ama’ey ami’ty hoe: Tsy ho po-ondaty hiambesatse amy fiambesa’ Israeley am-pahatreavako irehe, naho toe ambena’ o ana’oo ty lala’ iareo hañavelo añatrefako manahake o fañaveloa’oo.
“Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
26 Ie amy zao ry Andria­nañahare’ Israele, ehe te ho venteseñe i tsara tsinara’o amy mpitoro’o Davide raekoiy.
Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
27 Aa vaho himoneñe an-tane atoy vata’e hao t’i Andrianañahare? kanao tsy mahatañ’ Azo i likerañey ndra i like­ran-dindimoneñey; sandrake ty anjomba rinanjiko toy!
“Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
28 Fa ehe haoño ty halali’ i mpitoro’oy, naho i fiambanea’ey ry Iehovà Andriana­ñahareko, janjiño ty toreo naho hàtake saboe’ ty mpitoro’o ama’o henaneo;
Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
29 te hisokake handro an-kàleñe mb’ ami’ty anjomba toy o fihaino’oo, mb’ amy toetse nitsarae’o ty hoe: Ho ao ty añarako; hahajanjiña’o o halaly ho halalie’ ty mpitoro’o mb’ ami’ ty toetse toio.
Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
30 Janjiño ty fidrakadrakafam-pitoro’o, naho ondati’o Israeleo, ie misabo mb’ami’ty toetse toy; janjiño am-pimoneña’o andindiñe ao; mijanjiña vaho mañahà.
Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
31 Naho anañan-drañetse hakeo t’indaty, naho ampititihen-dre, ie mb’eo mifanta añatrefa’ ty kitreli’o añ’anjomba atoy;
“Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
32 le mijanjiña andin­dimoneñe ao, naho mitoloña, vaho zakao o mpitoro’oo, taroño amy ratiy t’ie raty, hampibalike o hatsivokara’eo añ’ ambone’eo; naho meo tò ty vantañe, hañolo­rañe aze mañeva i fahiti’ey.
sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
33 Aa ie zevoeñe aolon-drafe­lahy ondati’o Israeleo, t’ie aman-tahiñe ama’o; naho mimpoly ama’o naho mamela-pitàn-droe amy tahina’oy, naho misoloho vaho mihalaly ama’o ami’ty anjomba toy,
“Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
34 le mijanjiña andindimoneñe ao, naho hahao o hakeo’ ondati’o Isra­eleoo vaho ampolio mb’an-tane’ natolo’o an-droae’ iareo mb’atoy.
ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
35 Ie migabeñe i likerañey, tsy avy i orañey kanao nandilatse ama’o iereo, le ie misoloho mb’ami’ty toetse toy mamela-pitan-droe amy tahina’oy naho miamboho amy hakeo nampisotria’o iareoy,
“Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
36 le mijanjiña andikerañe ao, naho apoho ty tahi’ o mpitoro’oo naho ondati’o Israeleo vaho anaro iareo i lalam-bantañe fañaveloañey, ham­pahavia’o orañe i tane’o na­tolo’o am’ondati’oo ho lovay.
ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
37 Naho kerè i taney, he angorosy ke pozy he tromambo ke valala he beañe, ke forokeken-drafelahi’e o rova an-tane’eo; ke kiria ino, hera areteñ’ ino;
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
38 le ze halaly ndra soloho anoe’ t’indaty ndra ze hene ondati’o Israeleo, ie songa fohi’e ty hìla an-tro’e ao vaho mamela-pitan-droe mb’ami’ty anjomba toy,
in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
39 le mijanjiña andin­diñe añe, amy akiba-pimoneña’oy, le apoho naho mitoloña, vaho sindre toloro ty amo sata’eo t’indaty, fa arofoana’o ty tro’e (amy te Ihe avao ro maharofoanañe ty arofo’ o ana’ ondatio),
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
40 hañeveña’ iereo ama’o amo hene andro hiveloma’ iareo an-tane natolo’o aman-droae’aio.
saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
41 Le i renetane tsy boak’ am’ ondati’o Israeleoy, ie hirike tsietoitane añe ty amy tahina’oy —
“Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
42 kanao ho janjiñe’e i ta­hina’o ra’e­lahiy naho i fità’o maozatsey vaho i fità’o natora­kitsi’oy— ie miheo mb’ etoa hitalaho mb’ami’ty anjomba toy;
gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
43 le mijanjiña andindimoneñe an-toe-pimoneña’o ao, naho henefo o kanjia’ i renetaney azoo; hahafohina’ ze kila’ ondati’ ty tane toy ty tahina’o, hañeveñe ama’o, manahake ondati’o Israeleo, hahafohina’ iareo te kanjieñe ami’ty anjomba niranjieko toy i tahina’oy.
ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
44 Aa ie mionjomb’ an-kotakotak’ amo rafelahi’eo ondati’oo, ndra mb’ aia aia ty hañiraha’o iareo, vaho mihalaly am’ Iehovà mb’amy rova nijoboñe’oy, mb’ amy anjomba namboareko ho amy tahina’oiy;
“Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
45 le janjiño an-dikerañe ao i sabo’ iareoy, naho i halali’ iareoy vaho meo to.
ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
46 Ie miota ama’o—amy te tsy eo ze ondaty tsy mandilatse zao—le iviñera’o vaho atolo’o an-dra­felahi’ iareo, hasese an-drohy mb’an-tanen-drafelahy añe, ke te lavitse he marine;
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
47 le ie mitsa­kore an-tane naneseañe iareo an-drohy añe, naho mitolike naho midrakadrakak’ ama’o an-tane’ o naneseañe iareo an-drohio, manao ty hoe: Nanao hakeo zahay, nanao hatsi­vokarañe, vaho nitolon-karatiañe;
in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
48 ie mimpoly ama’o an’ kaampon’ arofo naho an-kaliforam-pañova an-tanen-drafelahi’ o nanese iareo an-drohio, naho mitalaho ama’o mb’an-tane natolo’o aman-droae’ iareo, mb’androva jinobo’o toy; vaho mb’amy anjomba niranjieko ho amy tahina’oiy;
in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
49 le janjiño ty halali’ iareo naho ty fisa­boa’ iareo mb’ an-toe-pimoneña’o andindimoneñe añe, vaho meo to;
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
50 naho apoho o hakeo nandilara’ ondati’o ama’oo, naho o fiolàñe niolà’ iareo; le iferenaiño añatrefa’ o ninday iareo an-drohy mb’eo hitre­treza’ iareo;
Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
51 amy t’ie ondati’o, i lova’o na­kare’o amy Mitsraime, boak’ añivo i toñake viñey.
Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
52 Ehe manokafa fihai­no amo hala­lim-pitoro’oo naho ami’ty fisolohoa’ on­dati’o Israeleo, hi­ha­oña’o ndra mbia’ mbia ty itoreova’ iareo.
“Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
53 Amy t’ie navahe’o amo hene ondati’ ty tane toio, ho lova’o, amy nitsarae’o am-pità’ i Mosè mpitoro’oy, ie nampi­avote’o amy Mitsraime o roae’aio, ry Talè Iehovà.
Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
54 Ie nagado’ i Selomò ty nitaroñe’e i hene halaly naho soloho am’ Iehovà rezay le niongak’ aolo’ i kitreli’ Iehovày, amy niton­galefa’e naho namelatse fi­tañe mb’an-dindim-b’eoy,
Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
55 le nijohañe vaho nitata i hene valobohò’ Israele am-pazake ty hoe:
Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
56 Andriañeñe t’Iehovà nanolo-pitofàñe am’ondati’eo ty amo tsara’e iabio; leo raike tsy nipok’ amo tsara’e soa nampitama’e am-pità’ i Mose mpitoro’eo.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
57 Ho aman-tika t’Iehovà Andrianañaharen-tika, manahake t’ie nimpiaman-droaen-tikañe; lonike t’ie tsy hienga antika, tsy haforintse’e;
Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
58 fa hampitoliha’e mb’ama’e o arofon-tikañeo, hañaveloan-tika amo lala’eo, hañorike o lili’eo naho o fañè’eo vaho o fepètse linili’e an-droaen-tikañeo.
Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
59 Le ehe te harine’ Iehovà Andrianañaharen-tika handro an-kaleñe o entañe nihalalieko am’ Iehovào, hañomea’e to i mpitoro’ey naho ondati’e Israeleo, ami’ty fañeva’e boak’ andro;
Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
60 hahafohina’ ze hene ondati’ ty tane toy t’Iehovà, t’ie ro Andrianañahare tsy aman-tovo’e.
saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
61 Ee abey te ho am’ Iehovà Andrianañaharentika an-kaliforan’ arofo nahareo, hañavelo amo fañè’eo, naho hañori­ke o lili’eo, manahake henaneo.
Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
62 Le fonga nañenga soroñe añatrefa’ Iehovà eo i mpanjakay naho Israele ni­trao­k’ ama’e.
Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
63 Bi­nanabana’ i Selomò amy engam-panintsiñañe nisoroña’e am’ Iehovày ty añombe roe-ale-tsi-ro’ arivo, naho añondry rai-hetse-tsi-ro’ale. Izay ty nañoriza’ i mpanjakay naho o ana’ Israeleo ty anjomba’ Iehovà.
Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
64 Amy àndroy ka ty nañoriza’ i mpanjakay ty añivo’ i kiririsa aolo’ i anjomba’ Iehovày; fa teo ty nañenga’e o soroñeo, naho o enga-mahakamao, naho ty safo’ o engam-panintsiñañeo; amy te ni-loho kede ty kitrely torisike añatrefa’ Iehovà, tsy ho ni-tsahatse aze i nisoroñañe naho i enga-mahakama vaho safo’ o engam-panintsiñañeo rezay.
A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
65 Aa le nambena’ i Selo­mò miharo am’ Israele iaby henane zay i sabadidakey, nivalobohòke jabajaba boak’ am-pimoahañe e Kamate, pak’ an-toraha’ i Mitsraime añe añ’atrefa’ Iehovà Andrianañaharen-tikañe, fito andro nitovoñañe fito; andro folo-efats’ amby.
Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
66 Nampolie’e amy andro fahavaloy ondatio, naho nandriañe’ iareo i mpanjakay naho songa noly mb’an-kiboho’e mb’eo an-drebeke naho añ’ arofo mifale ty amo hene hasoa nanoe’ Iehovà amy Davide mpitoro’ey vaho am’ Israele ondati’eo.
A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.

< 1 Mpanjaka 8 >