< 1 Jaona 1 >
1 Tam-pifotorañey i Tsaran-kaveloñey, ie i jinanji’aiy, niisam-pihaino’aiy, nisambà’ay naho tsinapa-pità’aiy.
Wannan da ya kasance tun farko, wanda muka ji, wanda muka gani da idanunmu, wanda muka duba, hannuwanmu kuma suka taɓa, wannan ne muke shela game da Kalman rai.
2 (Fa naboake i haveloñey le niisa’ay, naho mitalily, vaho itaroña’ay i haveloñe nainai’e aman-dRae ao vaho nabentatse ama’aiy.) (aiōnios )
Wannan Rai ya bayyana, muka kuwa gan shi, muka kuma shaida shi, muna kuwa yin muku shelar wannan rai madawwami, wanda dā yake tare da Uba, ya kuma bayyana a gare mu. (aiōnios )
3 Taroñe’ay ka o niisa’ay naho jinanji’aio, soa te hitrao-drehak’ ama’ay nahareo. Toe miharo rehak’ aman-dRae naho amy Ana’e Iesoà Norizañey zahay.
Muna yin muku shelar abin da muka gani, muka kuma ji ne, domin ku ma ku yi zumunci tare da mu. Zumuncinmu kuwa yana tare da Uba da kuma Ɗansa, Yesu Kiristi.
4 Isokira’ay o raha zao, hañenefañe ty haeha’areo.
Muna rubuta wannan domin farin cikinmu yă zama cikakke.
5 Zao ty entañe nijinanjiñe’ay naho itaroña’ay, Toe Hazavàñe t’i Andrianañahare; ie tsy aman’ ieñe, ndra loli’e.
Wannan shi ne saƙon da muka ji daga wurinsa, muna kuma sanar da ku cewa Allah haske ne; a cikinsa kuwa babu duhu ko kaɗan.
6 Naho mihàboke t’ie mitrao-drehak’ ama’e fe mañavelo amy ieñey ao, le mandañitse, tsy mañavelo an-katò.
In muka ce muna zumunci da shi amma muna tafiya cikin duhu, ƙarya muke yi, kuma ba ma rayuwa bisa ga gaskiya.
7 F’ie mañavelo an-kazavàñe, amy te Ie ro an-kazavàñ’ ao, le mitrao-drehake tika vaho liove’ ty lio’ Iesoà Ana’e amy ze fonga tahiñe.
Amma in muna tafiya cikin haske, yadda yake cikin haske, muna da zumunci da juna ke nan, kuma jinin Yesu, Ɗansa, yana tsarkake mu daga dukan zunubi.
8 Aa naho mieva t’ie tsy aman-kakeo le mamañahy vatañe, vaho tsy aman-tika ty hatò.
In muka ce ba mu da zunubi, muna ruɗin kanmu ne, gaskiya kuwa ba ta cikinmu.
9 Ie miantoke hakeo, le migahiñe naho vantan-dre hañaha o tahin-tikañeo, hañaliova’e amy ze fonga hatsivokarañe.
In muka furta zunubanmu, shi mai aminci ne, mai adalci kuma, zai gafarta mana zunubanmu, yă kuma tsarkake mu daga dukan rashin adalci.
10 Ie manao te mb’e lia tsy nanao hakeo le mampandañitse aze vaho tsy aman-tika o tsara’eo.
In muka ce ba mu yi zunubi ba, mun mai da shi maƙaryaci ke nan, maganarsa kuwa ba ta da wuri a cikinmu.