< Pāvilavēstulē Romiešiem 3 >

1 Kas tad nu Jūdam ir pārāki, jeb kāds ir tas apgraizīšanas labums?
To ina fifikon da bayahude yake dashi? Kuma ina ribar kaciya?
2 Visādi liels! Jo pirmā kārtā Dieva vārdi tiem ir uzticēti.
Akwai muhimmancinsu ta kowacce hanya. Tun farko dai, yahudawa ne aka dankawa wahayi daga Allah.
3 Jo kas par to, ja kādi nav ticējuši? Vai viņu neticība Dieva uzticību iznīcinās?
Idan wasu yahudawa basu bada gaskiya ba fa? Rashin bangaskiyarsu zai hana amincin Allah aiki?
4 Nemaz ne! Bet lai tā paliek, ka Dievs ir taisns un ikkatrs cilvēks melkulis, itin kā ir rakstīts: “Ka Tu palieci taisns Savos vārdos un uzvari, kad Tu topi tiesāts.”
Bazai taba zama haka ba. Maimakon haka, bari Allah ya zama mai gaskiya, ko da kowanne mutum makaryaci ne. Kamar yadda aka rubuta, “Domin a nuna kai mai adalci cikin maganganunka, kuma kayi nasara a lokacin da aka kawo ka gaban shari'a.”
5 Kad nu mūsu netaisnība Dieva taisnību apstiprina, ko lai sakām? Vai tad Dievs nav netaisns, kad Viņš soda? To runāju, kā cilvēki mēdz runāt.
Amma idan rashin adalcinmu ya nuna adalcin Allah, to me zamu ce? Allah ba marar adalci ba ne, wanda ke aiwatar da fushinsa, ko kuwa? Ina magana bisa ga tunanin mutuntaka.
6 Nemaz ne! Jo kā tad Dievs pasauli tiesās?
Bazai taba zama haka ba. Domin idan haka ne ta yaya Allah zai shar'anta duniya?
7 Jo ja Dieva patiesība caur maniem meliem ir vairojusies Viņam par godu, ko tad es vēl kā grēcinieks topu tiesāts?
Amma idan gaskiyar Allah ta wurin karyata ta habaka yabonsa, To me yasa ake shar'anta ni a matsayin mai zunubi?
8 Un kam mēs nesakām, itin kā topam zaimoti, un itin kā daži teic, mūs sakām: darīsim ļaunu, lai nāk labums? Tādiem sods pēc taisnības notiks.
To me zai hana ace kamar yadda ake fadin zancen karya a kanmu, wasu kuma sun dauka cewa mun fadi hakan, “Bari muyi mugunta, domin nagarta tazo?” Hukuncin su halal ne.
9 Ko tad nu? Vai mēs esam labāki? Nemaz ne. Jo mēs jau pirmāk esam rādījuši, gan Jūdus, gan Grieķus, visus esam apakš grēka.
To me kenan? Zamu ba kanmu hujja ne? ko kadan. Domin mun riga munyi zargin yahudawa da hellinawa, da cewar dukkansu, suna karkashin zunubi.
10 Itin kā stāv rakstīts: nav neviena taisna, it neviena,
Kamar yadda aka rubuta, babu wani mai adalci, babu ko daya.
11 Nav neviena prātīga, nav neviena, kas Dievu meklē.
Babu wani mai fahimta. Babu wani mai neman Allah.
12 Visi ir atkāpušies un kopā tapuši nelieši, nav neviena, kas labu dara, it neviena.
Dukansu sun kauce hanya, dukansu gaba daya sun zama marasa amfani. Babu mai aikin nagarta, a'a, babu ko da guda daya.
13 Viņu rīkle ir atvērts kaps; ar savām mēlēm tie viltību dara: odžu dzelonis ir apakš viņu lūpām;
Makogwaronsu a bude yake kamar kabari. Harsunansu na dauke da cuta. Dafin macizai na karkashin lebunansu.
14 Viņu mute ir lāstu un rūgtuma pilna.
Bakunansu cike suke da la'ana da daci.
15 Viņu kājas ir čaklas izliet asinis.
Sawayensu na saurin zuwa zubar da jini.
16 Posts un sirdēsti ir pa viņu ceļiem,
Tafarkinsu wahala ce da lalacewa.
17 Un miera ceļu tie nezin.
Wadannan mutane basu san hanyar salama ba.
18 Dieva bijāšanas nav priekš viņu acīm.
Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19 Bet mēs zinām, ka bauslība visu, ko tā saka, to tā runā uz tiem, kas ir apakš bauslības, lai ikviena mute top aizbāzta, un visa pasaule ir noziedzīga Dieva priekšā.
To mun san dai duk abin da shari'a tace, shari'a na magana ne da wadanda ke karkashinta, domin a rufe kowanne baki, domin dukan duniya ta bada amsa a gaban Allah.
20 Tādēļ no bauslības darbiem neviena miesa netaps taisnota Viņa priekšā; jo caur bauslību nāk grēku atzīšana.
Domin a gabansa babu wanda zai barata ta wurin ayukan shari'a. Domin ta wurin shari'a ne sanin zunubi yazo.
21 Bet Dieva taisnība, kas no bauslības un no praviešiem ir apliecināta, tagad ir tapusi zināma bez bauslības,
Amma yanzu ba tare da shari'a ba an bayyana sanin adalcin Allah, wanda shari'a da annabawa suke shaidawa.
22 Tā Dieva taisnība caur ticību uz Jēzu Kristu priekš visiem un pie visiem, kas tic; jo tur nav nekādas starpības.
Wato, adalcin Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ga dukkan wadanda ke bada gaskiya. Domin babu bambanci:
23 Jo visi ir grēkojuši, un tiem trūkst teikšanas Dieva priekšā,
Domin duk sun yi zunubi sun kuma kasa kaiwa ga darajar Allah,
24 Un top taisnoti bez nopelna no Viņa žēlastības caur to atpirkšanu, kas notikusi caur Kristu Jēzu.
Da alherinsa an baratar da mu ta wurin fansar dake cikin Yesu Almasihu.
25 To Dievs ir nolicis par salīdzināšanu, caur ticību iekš Viņa asinīm, ka tas Savu taisnību parādītu, pamezdams tos priekšlaikā darītos grēkus
Amma Allah ya bayar da Yesu Almasihu wanda yake hadayar fansa ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya mika Almasihu a matsayin tabbacin hukuncinsa, sabo da kuma ketarewar zunubanmu na baya
26 Iekš dievišķas paciešanas, ka Tas Savu taisnību parādītu šinī laikā: Sevi esam taisnu, un taisnu darām to, kas ir no Jēzus ticības.
cikin hakurinsa. Duk wannan ya faru ne domin a bayyana adalcinsa cikin wannan zamani, domin ya tabbatar da kansa mai hukunci, kuma ya nuna shine mai baratar da kowa saboda bangaskiya cikin Yesu.
27 Kur nu ir tā lielīšanās? Tā ir zudusi. Caur kuru bauslību? Vai caur darbu bauslību? Nē! Bet caur ticības bauslību.
To ina fahariya? An fitar da ita. A kan wane dalilin? Don ayyuka? A'a, amma ta dalilin bangaskiya.
28 Tad nu mēs turam, ka cilvēks top taisnots caur ticību bez bauslības darbiem.
Domin wannan muka kammala cewar ana baratar da mutum ta wurin bangaskiya ba tare da ayyukan shari'a ba.
29 Jeb vai Dievs tikai Jūdu Dievs? Vai nav arī pagānu Dievs? Tiešām arī pagānu.
Ko kuwa Allah Allahn yahudawa ne kadai? Shi ba Allahn al'ummai bane? I, na al'ummai ne kuma.
30 Jo viens Dievs ir, kas taisno apgraizījumu no ticības un priekšādu caur ticību.
Idan dai lallai Allah daya ne, zai baratar da mai kaciya ta wurin bangaskiya, da marar kaciya kuma ta wurin bangaskiya.
31 Vai tad nu mēs bauslību iznīcinām caur ticību? Nemaz! Bet mēs bauslību apstiprinām.
Mun kawar da shari'a kenan ta wurin bangaskiya? ba zai taba kasancewa haka ba. Maimako ma, muna inganta shari'a kenan.

< Pāvilavēstulē Romiešiem 3 >