< Jaņa Atklāsmes Grāmata 21 >
1 Un es redzēju jaunu debesi un jaunu zemi; jo tā pirmā debess un tā pirmā zeme bija zudušas, un jūra vairs nav.
Sa’an nan na ga sabon sama da sabuwar duniya, gama sama na farko da duniya ta farko sun shuɗe, babu kuma wani teku.
2 Un es, Jānis, redzēju to svēto pilsētu, to jauno Jeruzālemi, no Dieva nokāpjam no debesīm, sataisītu kā savam vīram izgreznotu brūti.
Na ga Birni Mai Tsarki, sabuwar Urushalima tana saukowa daga sama, daga Allah, a shirye kamar amaryar da aka yi mata ado mai kyau saboda mijinta.
3 Un es dzirdēju lielu balsi no debesīm sakām: redzi, tas Dieva dzīvoklis pie cilvēkiem, un Viņš mājos pie tiem un tie būs Viņa ļaudis, un Dievs pats būs pie tiem, viņiem par Dievu.
Na kuma ji wata babbar murya daga kursiyin tana cewa, “Yanzu mazaunin Allah yana tare da mutane, zai kuma zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kansa kuwa zai kasance tare da su yă kuma zama Allahnsu.
4 Un Dievs nožāvēs visas asaras no viņu acīm un nāve vairs nebūs, nedz bēdas, nedz brēkšana, nedz raizes vairs nebūs; jo tās pirmās lietas ir pagājušas.
Zai share dukan hawaye daga idanunsu. Ba sauran mutuwa ko makoki ko kuka ko azaba, gama tsofaffin al’amura sun shuɗe.”
5 Un kas uz tā godības krēsla sēdēja, sacīja: redzi, visu es daru jaunu. Un Viņš uz mani saka: raksti! Jo šie vārdi ir uzticami un patiesīgi.
Wannan da yake zaune a kursiyin ya ce. “Ina yin kome sabo!” Sai ya ce, “Rubuta wannan, domin waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma.”
6 Un Viņš uz mani sacīja: tas ir noticis. Es esmu Tas A(Alfa) un Tas O(Omega), Tas Iesākums un Tas Gals. Es tam iztvīkušam došu no dzīvības ūdens avota bez maksas.
Ya ce mini, “An gama. Ni ne Alfa da kuma Omega, na Farko da kuma na Ƙarshe. Duk mai jin ƙishirwa zan ba shi abin sha kyauta daga maɓulɓular ruwan rai.
7 Kas uzvar, tam būs iemantot visas lietas, un Es būšu viņa Dievs, un viņš būs Mans dēls.
Duk wanda ya ci nasara zai gāji dukan wannan, zan kuma zama Allahnsa, shi kuma zai zama ɗana.
8 Bet tiem bailīgiem un neticīgiem un negantiem un slepkavām un mauciniekiem un burvjiem un elku kalpiem un visiem melkuļiem būs sava daļa tai zaņķī, kas deg ar uguni un sēru; tā ir tā otrā nāve. (Limnē Pyr )
Amma matsorata, da marasa bangaskiya, masu ƙazanta, masu kisankai, masu fasikanci, masu sihiri, masu bautar gumaka da dukan maƙaryata, wurinsu zai kasance a cikin tafkin wutar da yake farar wuta mai ci. Wannan fa ita ce mutuwa ta biyu.” (Limnē Pyr )
9 Un pie manis nāca viens no tiem septiņiem eņģeļiem, kam tie septiņi kausi bija, pildīti ar tām septiņām pēdīgām mocībām, un runāja ar mani sacīdams: nāc šurp! Es tev rādīšu to sievu, Tā Jēra brūti.
Ɗaya daga cikin mala’ikun nan bakwai masu kwanonin nan bakwai cike da annoban nan bakwai na ƙarshe, ya zo ya ce mini “Zo, zan nuna maka amaryar, matar Ɗan Ragon.”
10 Un viņš mani garā noveda uz lielu un augstu kalnu un man rādīja to lielo pilsētu, to svēto Jeruzālemi, kas no debesīm nokāpa no Dieva.
Ya kuwa ɗauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsayi, ya kuma nuna mini Birni Mai Tsarki, Urushalima, tana saukowa daga sama, daga Allah.
11 Un tai bija Dieva godība. Un viņas spožums bija tam visdārgākam akmenim līdzīgs, tā kā jaspisa akmens, kas spīd kā kristāls.
Ya haskaka da ɗaukakar Allah, haskensa kuwa ya yi kamar lu’ulu’u mai daraja sosai, kamar yasfa, yana ƙyalƙyali kamar madubi.
12 Un tai bija liels un augsts mūris ar divpadsmit vārtiem, un uz tiem vārtiem bija divpadsmit eņģeļi, un vārdi bija virsū rakstīti, kas ir tie divpadsmit Israēla bērnu cilšu vārdi.
Yana da babbar katanga mai tsayi, mai ƙofofi goma sha biyu, da kuma mala’iku goma sha biyu a ƙofofin. A bisa ƙofofin an rubuta sunayen kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
13 No austruma trīs vārti, no ziemeļa puses trīs vārti, no dienasvidus puses trīs vārti, no vakara puses trīs vārti.
Akwai ƙofofi uku a gabas, uku a arewa, uku a kudu, uku kuma a yamma.
14 Un pilsētas mūrim bija divpadsmit pamati un uz tiem Tā Jēra divpadsmit apustuļu vārdi.
An gina katangar birnin a kan tushen gini goma sha biyu, a kansu kuwa akwai sunayen manzannin sha biyu na Ɗan Ragon.
15 Un kas ar mani runāja, tam bija zelta kārts, ka tas to pilsētu mērotu un viņas vārtus un viņas mūrus.
Mala’ikan da ya yi magana da ni yana da sandan awo na zinariya don awon birnin, ƙofofinsa, da kuma katangarsa.
16 Un tā pilsēta bija četrstūrīga un bija tik gara, cik plata. Un viņš to pilsētu mēroja ar to kārti pie divpadsmit tūkstošiem birzumiem; viņas garums un platums un augstums bija it vienāds.
Birnin murabba’i ne, tsayinsa daidai ne da fāɗinsa. Ya auna birnin da sandarsa ya kuwa sami mil 1,400 (wajen kilomita 2,200) tsawonsa, fāɗinsa da kuma tsayinsa daidai suke.
17 Un viņš mēroja viņas mūri pie simts četrdesmit un četrām olektīm pēc cilvēka mēra, kas tam eņģelim bija.
Ya auna katangarsa ya kuma sami ƙaurinta kamun 144, bisa ga ma’aunin mutum, wanda mala’ikan ya yi amfani da shi.
18 Un viņas mūris bija uztaisīts no jaspisa; un tā pilsēta bija no skaidra zelta, kas skaidrai glāzei bija līdzīgs.
An yi katangar da yasfa, birnin kuma da zinariya zalla, yana kuma ƙyalli kamar madubi.
19 Un pilsētas mūra pamati bija izrotāti ar visādiem dārgiem akmeņiem; pirmais pamats bija jaspis, otrais safīrs, trešais kalķedons, ceturtais smaragds.
Tushen ginin katangar birnin kuwa an yi masa adon da kowane irin dutse mai daraja. Tushe na farko an yi shi yasfa, na biyu saffaya, na uku agat, na huɗu zumurrudu,
20 Piektais sardoniks, sestais sardis, septītais krizolits, astotais berils, devītais topāzis, desmitais krizoprazs, vienpadsmitais hiacints, divpadsmitais ametists.
na biyar onis, na shida yakutu, na bakwai kirisolit, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofuras, na goma sha ɗaya yasin, na goma sha biyu kuma ametis.
21 Un tie divpadsmit vārti bija divpadsmit pērles, un ikvieni vārti bija no vienas pērles, un pilsētas ielas bija skaidrs zelts tā kā skaidra glāze.
Ƙofofi goma sha biyun nan lu’ulu’ai goma sha biyu ne, kowace ƙofa an yi ta da lu’ulu’u guda. Babban titin birnin kuwa an yi shi da zinariya zalla, yana kuma ƙyalli kamar madubi.
22 Un es neredzēju nevienu Dieva namu iekš tās, jo Tas Kungs, tas visu valdītājs Dievs, ir viņas nams un Tas Jērs.
Ban ga haikali a cikin birnin ba, domin Ubangiji Allah Maɗaukaki da kuma Ɗan Ragon ne haikalin birnin.
23 Un tai pilsētai saules nevajag nedz mēneša, ka tie tur spīdētu, jo Dieva godība to apgaismo, un viņas gaišums ir Tas Jērs.
Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi, gama ɗaukakar Allah tana ba shi haske, Ɗan Ragon kuwa shi ne fitilar birnin.
24 Un tautas staigās viņas gaišumā, un ķēniņi virs zemes savu godu un slavu nesīs tur iekšā.
Al’ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin, sarakunan duniya kuma za su kawo darajarsu cikin birnin.
25 Un viņas vārti netaps aizslēgti dienā, jo nakts tur nav.
Ba za a taɓa rufe ƙofofin birnin da rana ba, gama ba za a yi dare a can ba.
26 Un tautu godu un slavu tur nesīs iekšā.
Za a kawo ɗaukaka da girmar al’ummai a cikin birnin.
27 Un tur neieies neviens, kas ir apgānīts un negantību dara un melus, bet tie vien, kas ir rakstīti Tā Jēra dzīvības grāmatā.
Babu wani abu marar tsarkin da zai taɓa shiga cikin birnin, babu kuma wani mai aikata abin kunya ko ruɗi da zai shiga, sai dai waɗanda aka rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Ɗan Ragon.