< Psalmi 39 >
1 Dāvida dziesma, dziedātāju vadonim, Jedutunam. Es esmu apņēmies, ka savu ceļu sargāšu, ka negrēkošu ar savu mēli; es sargāšu savu muti kā ar iemauktiem, kamēr bezdievīgais manā priekšā.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
2 Es esmu palicis kā mēms un klusu cietis, un nepieminu vairs labuma, bet manas sāpes vairojās.
Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
3 Mana sirds ir iekarsusi iekš manis; kad es uz to domāju, tad es iedegos kā uguns; es runāju ar savu mēli:
zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
4 Kungs, māci man manu galu un kāds ir manu dienu mērs, lai es zinu, cik nīcīgs es esmu.
“Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
5 Redzi, Tu manas dienas esi licis plaukstas platumā, un mans mūžs ir kā nekas Tavā priekšā; tiešām niecība vien ir ikviens cilvēks savā stiprumā. (Sela)
Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
6 Cilvēks staigā kā ēna un nieka dēļ raizējās; viņš krāj, bet nezin, kas to dabūs.
“Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
7 Nu tad, uz ko man būs gaidīt, Kungs? Es cerēju uz Tevi.
“Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
8 Izglāb mani no visām manām pārkāpšanām, un neliec man ģeķiem palikt par apsmieklu.
Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
9 Es esmu klusu un neatdaru savu muti; jo Tu to esi darījis.
Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
10 Atņem Savu mocību no manis, jo es nīkstu no Tavas rokas grūtuma.
Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
11 Kad Tu cilvēku pārmāci par noziegumiem, tad Tu iznīcini viņa skaistumu kā kodes; tiešām: visi cilvēki ir niecība.(Sela.)
Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
12 Klausi, Kungs, manu lūgšanu, ņem vērā manu saukšanu, un neciet klusu pie manām asarām, jo es esmu svešinieks un piedzīvotājs Tavā priekšā, tā kā visi mani tēvi.
“Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
13 Atstājies no manis, ka es atspirgstos, pirms noeju un vairs neesmu.
Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”