< Psalmi 31 >

1 Dāvida dziesma. Dziedātāju vadonim. Uz tevi, Kungs, es paļaujos, nepamet mani kaunā mūžīgi, izglāb mani caur Tavu taisnību.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
2 Atgriez Savu ausi pie manis, izglāb mani drīz, esi man par stipru patvērumu, par stipru pili man palīdzēt.
Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
3 Jo Tu esi mans akmens kalns un mana stiprā pils, un Tava Vārda dēļ ved un vadi mani.
Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
4 Izved mani no tīkla, ko tie priekš manis paslēpuši, jo Tu esi mans stiprums.
Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
5 Tavā rokā es pavēlu savu garu, Tu mani esi atpestījis, Kungs, Tu stiprais patiesības Dievs.
Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
6 Es ienīstu tos, kas dodas uz blēņu mācībām, bet es paļaujos uz To Kungu.
Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
7 Es priecāšos un līksmošos par Tavu žēlastību, ka Tu uzlūko manas bēdas, un vērā lieci manu dvēseli bailēs,
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
8 Un nenodod mani ienaidnieka rokā; Tu manām kājām lieci stāvēt plašā vietā.
Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
9 Esi man žēlīgs, ak Kungs! Jo man ir bail', no skumības ir sarucis mans vaigs, mana dvēsele un mana miesa.
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
10 Jo mana dzīvība ir nonīkusi caur noskumšanu un mani gadi caur nopūšanos, mans spēks caur manu noziegumu ir sakritis, un mani kauli ir sanīkuši.
Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
11 Caur visiem saviem pretiniekiem es esmu par kaunu tapis saviem kaimiņiem, un saviem pazīstamiem par biedēkli; kas mani uz ielām redz, tie bēg no manis.
Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
12 Es sirdīs esmu aizmirsts kā mironis, esmu tapis kā sadauzīts trauks.
An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
13 Jo es dzirdu no daudziem lamāšanās: bailība ir visapkārt; kad tie kopā sarunājās pret mani, tie domā paņemt manu dzīvību.
Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
14 Bet es cerēju uz Tevi, Kungs; es saku tā: Tu esi mans Dievs.
Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
15 Mani laiki stāv Tavā rokā; izglāb mani no manu ienaidnieku rokas un no tiem, kas mani vajā.
Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
16 Liec Savam vaigam spīdēt pār Savu kalpu, atpestī mani caur Tavu žēlastību.
Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
17 Kungs, neliec man kaunā palikt, jo es Tevi piesaucu; lai bezdievīgie paliek kaunā un top klusināti ellē. (Sheol h7585)
Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
18 Lai mēmas paliek melkuļu lūpas kas bezkaunīgi runā pret taisno ar lepnību un nicināšanu.
Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
19 Cik liels ir Tavs labums, ko Tu esi glabājis tiem, kas Tevi bīstas, un sataisījis tiem, kas cilvēku priekšā uz Tevi paļaujas.
Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
20 Tu tos slēpi Sava vaiga ēnā priekš cilvēku dumpjiem, Tu tos glabā kā namā priekš rējēju mēlēm.
Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
21 Slavēts lai ir Tas Kungs, jo Viņš brīnišķi man parādījis Savu žēlastību tā kā stiprā pilsētā.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
22 Gan es sacīju savās bailēs: es esmu atmests no Tava vaiga; taču Tu klausīji manas sirds lūgšanas balsi, kad es Tevi piesaucu.
Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
23 Mīlējiet To Kungu, visi Viņa svētie; Tas Kungs pasargā tos ticīgos, un atmaksā papilnam tam, kas dara pārgalvību.
Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
24 Esiet droši un stipri savā sirdī, visi, kas cerējiet uz To Kungu.
Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.

< Psalmi 31 >