< Psalmi 30 >
1 Dziesma pie Dāvida nama iesvētīšanas. Es Tevi augsti teikšu, Kungs, jo Tu mani augsti esi cēlis, un maniem ienaidniekiem neesi ļāvis priecāties par mani.
Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
2 Kungs, mans Dievs, kad es Tevi piesaucu, tad Tu mani dziedināji.
Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
3 Kungs, Tu manu dvēseli esi izvedis no elles, Tu mani dzīvu esi uzturējis, ka neesmu nogrimis kapā. (Sheol )
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol )
4 Dziedājiet Tam Kungam, jūs Viņa svētie, un teiciet Viņa svēto piemiņu.
Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
5 Jo Viņa dusmība pastāv acumirkli, Viņa žēlastība cauru mūžu: vakarā nāk raudāšana, bet rītā prieks.
Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
6 Es gan sacīju, kad man labi klājās: es nešaubīšos ne mūžam,
Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
7 Jo, Kungs, caur Tavu labprātību Tu manu kalnu esi darījis pastāvīgu; bet kad Tu Savu vaigu paslēpi, tad es iztrūcinājos.
Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
8 Tevi es piesaucu, Kungs, un pielūdzu Tevi, ak Kungs no sirds.
A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
9 Kāds labums atlec no manām asinīm, kad es būšu kapā grimis? Vai pīšļi Tevi slavēs? Vai tie sludinās Tavu patiesību?
“Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
10 Klausi, Kungs, un apžēlojies par mani: Kungs, esi man par palīgu!
Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
11 Manas žēlabas Tu esi pārvērtis par līksmību, Tu man to maisu esi novilcis un mani apjozis ar prieku.
Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
12 Tāpēc Tev dziedās mans gods un nestāvēs klusu; Kungs, mans Dievs, es Tev pateikšos mūžīgi.
don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.