< Psalmi 105 >
1 Pateiciet Tam Kungam, piesauciet Viņa Vārdu, dariet zināmus starp tiem ļaudīm Viņa darbus.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Dziediet Viņam, slavējiet Viņu ar dziesmām, pārdomājiet visus Viņa brīnumus.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Slavējiet Viņa svēto vārdu; lai tās sirdis priecājās, kas To Kungu meklē.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Vaicājiet pēc Tā Kunga un pēc Viņa spēka, meklējiet vienmēr Viņa vaigu.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Pieminiet Viņa brīnumus, ko Viņš ir darījis, Viņa brīnuma darbus un Viņa mutes tiesas, -
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 Tu Ābrahāma, Viņa kalpa dzimums, jūs Jēkaba bērni, Dieva izredzētie!
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Viņš ir Tas Kungs, mūsu Dievs; Viņa tiesas iet pār visu zemi.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Viņš piemin Savu derību mūžam, to vārdu, ko Viņš ir iecēlis tūkstošiem dzimumiem,
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 Ko Viņš ar Ābrahāmu derējis un ko zvērējis Īzakam.
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 To Viņš arī Jēkabam ir iecēlis par likumu, Israēlim par mūžīgu derību,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 Sacīdams: tev Es došu Kanaāna zemi, jūsu mantības daļu;
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Kad tie vēl bija mazs pulciņš, ne daudz, un svešinieki iekš tās,
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 Un staigāja no vienas tautas pie otras, no vienas valsts pie otras valsts ļaudīm,
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Viņš nevienam neļāva tos apbēdināt, Viņš arī ķēniņus sodīja viņu dēļ:
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 Neaizskariet Manus svaidītos un nedariet ļauna Maniem praviešiem!
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Viņš aicināja badu pār zemi, Viņš atņēma visu maizes padomu.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Viņš sūtīja viņu priekšā vienu vīru; Jāzeps tapa pārdots par kalpu.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 Viņa kājas tapa spaidītas siekstā, viņa miesas nāca dzelzīs,
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Tiekams viņa vārds notika, un Tā Kunga sludinājums to pārbaudīja.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 Tas ķēniņš sūtīja un lika to atraisīt, tas ļaužu valdītājs to atlaida vaļā.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 Viņš to iecēla par kungu savam namam un par valdnieku visai savai mantai.
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 Ka tas saistītu viņa lielkungus pēc sava prāta un mācītu gudrību viņa vecākajiem.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Tā Israēls nāca Ēģiptes zemē un Jēkabs piemita Hama zemē.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 Un Viņš Saviem ļaudīm lika augumā augt un tos darīja jo varenus nekā viņu pretiniekus.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 Viņš pārvērsa viņu sirdi, ienīdēt Viņa ļaudis un ar viltu glūnēt uz Viņa kalpiem.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Viņš sūtīja Mozu, Savu kalpu, un Āronu, ko Viņš bija izredzējis.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 Tie darīja viņu starpā Dieva brīnumus un brīnuma zīmes Hama zemē.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Viņš sūtīja tumsu, tad kļuva tumšs; un tie Viņa Vārdam neturējās pretī.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Viņš pārvērsa viņu ūdeņus par asinīm un nokāva viņu zivis.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Viņu zeme mudžēja no vardēm viņu ķēniņu kambaros.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Viņš runāja, tad nāca kukaiņi, utis visās viņu robežās.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 Viņš tiem deva krusu lietus vietā, uguns liesmas viņu zemē,
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 Un sasita viņu vīna kokus un viņu vīģes kokus un salauzīja kokus viņu robežās.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Viņš runāja, tad nāca siseņi un vaboles neizskaitāmā pulkā,
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 Kas apēda visu zāli viņu zemē, un norija viņu zemes augļus.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Viņš kāva arī visus pirmdzimtos viņu zemē un visu viņu pirmo stiprumu.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 Un tos izveda ar sudrabu un zeltu, un neviena gurdena nebija viņu ciltīs.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 Ēģiptes zeme priecājās, kad tie izgāja, jo viņu bailes uz tiem bija kritušas.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Viņš deva padebesi par apsegu, un uguni naktī par gaismu.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 Tie lūdza un viņš lika nākt paipalām un tos ēdināja ar debes'maizi.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Viņš pāršķēla klinti, tad ūdens iztecēja, un upes skrēja tuksnesī.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Jo Viņš pieminēja Savu svēto vārdu un Ābrahāmu, Savu kalpu.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 Tā Viņš izveda Savus ļaudis ar prieku un Savus izredzētos ar gavilēšanu,
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 Un tiem deva pagānu zemes; tie iemantoja tautu sviedrus,
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 Lai turētu Viņa likumus un sargātu Viņa bauslību. Alleluja.
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.