< Psalmi 102 >

1 Bēdu cilvēka lūgšana, kad tas ir noskumis un savas žēlabas izgāž Tā Kunga priekšā. Ak Kungs, klausi manu lūgšanu, un mana saukšana lai nāk pie Tevis.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Neapslēp Savu vaigu priekš manis, atgriez Savu ausi pie manis bēdu laikā; tai dienā, kad es saucu, paklausi mani drīz.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Jo manas dienas ir iznīkušas kā dūmi, un mani kauli ir izdeguši kā pagale.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Mana sirds ir sasista un izkaltusi kā zāle, tā ka es aizmirstu pat savu maizi ēst.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Mani kauli līp pie manas miesas no kaukšanas un nopūšanās.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Es esmu tā kā dumpis tuksnesī, es esmu kā apogs (pūce) izpostītās vietās.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Es esmu nomodā un tāpat kā vientulis putns uz jumta.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Mani ienaidnieki mani nievā cauru dienu; kas pret mani trako, tie mani dara par lāsta vārdu.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Jo es ēdu pelnus kā maizi un sajaucu savu dzērienu ar asarām,
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 Tavas bardzības un dusmības pēc, jo Tu mani esi pacēlis un atkal nogāzis.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Manas dienas ir kā ēna pavakarē, un es kalstu kā zāle.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Bet Tu, Kungs, paliec mūžīgi un Tava piemiņa līdz radu radiem.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Kaut Tu celtos un apžēlotos par Ciānu, jo jau ir laiks par viņu apžēloties, jo tas nospriestais laiks ir atnācis.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Jo Tavi kalpi mīļo viņas akmeņus un žēlojās, ka tā guļ pīšļos.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Tad pagāni bīsies Tā Kunga Vārdu, un visi ķēniņi virs zemes Tavu godību,
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 Kad Tas Kungs Ciānu uztaisīs un parādīsies Savā godībā.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Viņš griežas pie bēdu ļaužu lūgšanas un nenicina pielūgšanu.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Lai tas top uzrakstīts pēcnākamiem, un tie ļaudis, kas vēl taps radīti, slavēs To Kungu.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 Jo Viņš skatās no Sava svēta augstuma, Tas Kungs lūko no debesīm uz zemi,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 Ka Viņš dzird cietumnieku nopūšanos un atsvabina nāves bērnus;
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 Ka Tā Kunga vārds top sludināts Ciānā un Viņa slava Jeruzālemē,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 Kad tautas sapulcējās kopā un valstis, Tam Kungam kalpot.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Bet Viņš ir pazemojis ceļā manu spēku un paīsinājis manas dienas.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Es saku: mans Dievs, neņem mani nost pusmūžā. Tavi gadi paliek līdz radu radiem.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Senlaikus Tu esi nodibinājis zemi, un debesis ir Tavu roku darbs.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Tās zudīs, bet Tu pastāvēsi; tās sadils visas, kā drēbes; Tu tās pārvērtīsi kā drānas, un tās pārvērtīsies;
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Bet Tu palieci tas pats, un Tavi gadi nebeigsies.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Tavu kalpu bērni paliks, un viņu dzimums būs pastāvīgs Tavā priekšā.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Psalmi 102 >