< Salamana Pamācības 3 >
1 Mans bērns, neaizmirsti manu mācību, bet lai tava sirds patur manus baušļus.
Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
2 Jo tie tev pieliks daudz dienu un dzīvības gadus un mieru.
gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
3 Žēlastība un ticība tevi neatstās; sien tos ap savu kaklu un ieraksti tos savas sirds galdiņā;
Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Tad tu atradīsi žēlastību un labprātību Dieva un cilvēku acīs.
Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
5 Paļaujies uz To Kungu no visas savas sirds un nepaļaujies uz savu gudrību.
Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
6 Visos savos ceļos ņem Viņu vērā, tad Viņš darīs līdzenas tavas tekas
cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
7 Neesi gudrs savās acīs; bīsties To Kungu un atkāpies no ļauna.
Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
8 Tās būs tavai miesai zāles, kas dziedina, un atspirgšana taviem kauliem.
Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
9 Godā To Kungu no savas mantas, un no visa sava ienākuma pirmajiem,
Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
10 Tad tavi šķūņi pildīsies ar pilnību, un tavi vīna spaidi plūdīs no jauna vīna.
ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
11 Mans bērns, neatmet Tā Kunga pamācīšanu, un lai viņa pārmācīšana tev neriebj;
Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
12 Jo ko Tas Kungs mīļo, to Viņš pārmāca, kā tēvs dēlu, pie kā tam labs prāts.
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
13 Svētīgs tas cilvēks, kas atradis gudrību, un cilvēks, kam tiek saprašana.
Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
14 Viņu mantot ir labāki nekā sudrabu mantot, un viņu krāt labāki nekā spožu zeltu.
gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
15 Viņa ir dārgāka pār pērlēm un viss, ko tu kārotos, tai netiek līdzi.
Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
16 Garš mūžs ir viņas labā rokā, un viņas kreisā bagātība un gods.
Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
17 Viņas ceļi ir jauki ceļi, un visas viņas tekas ir miers.
Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
18 Viņa ir dzīvības koks tiem, kas viņu tver, un kas viņu cieti tur, tas ir laimīgs.
Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
19 Tas Kungs ar gudrību licis pamatus zemei, ar saprašanu viņš sataisījis debesis.
Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
20 Caur viņa ziņu plūda ūdens plūdi, un padebeši pilēja ar rasu.
ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
21 Mans bērns, lai tās neizzūd no tavām acīm, pasargi apdomīgu prātu un samaņu.
Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
22 Jo tā būs tavas dvēseles dzīvība un glītums tavam kaklam.
za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
23 Tad tu savu ceļu staigāsi droši, un tava kāja nepiedauzīsies;
Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
24 Apguldamies tu nebīsies, bet gulēsi, un tavs miegs būs gards.
sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
25 Tu nebīsies no piepešas izbailes, nedz no bezdievīgo posta, kad tas nāk;
Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
26 Jo Tas Kungs būs tavs patvērums un pasargās tavu kāju no valgiem.
gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
27 Neliedzies labu darīt, kam tas nākas, ja Dievs devis, ka tev pie rokas, to darīt;
Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
28 Nesaki uz savu tuvāko: „Ej un nāc, es tev rīt došu!“un tev tomēr ir.
Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
29 Neperē ļauna pret savu tuvāko, kad tas tev uzticēdamies pie tevis dzīvo.
Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
30 Nebaries par nepatiesu ar cilvēku ja viņš tev ļauna nav darījis.
Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
31 Neapskaudi varas darītāju un neizraugies sev neviena no viņa ceļiem;
Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
32 Jo netiklais Tam Kungam ir negantība, bet viņam ir draudzība ar sirdsskaidriem.
Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
33 Tā Kunga lāsti ir bezdievīga namā, bet taisno mājas vietu viņš svētī.
La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
34 Smējējus tiešām viņš apsmies, bet pazemīgiem dos žēlastību.
Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
35 Gudrie iemantos godu, bet ģeķi atradīs kaunu.
Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.