< Ceturtā Mozus 14 >
1 Tad visa draudze cēlās un pacēla savu balsi, un tie ļaudis raudāja to nakti.
A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
2 Un visi Israēla bērni kurnēja pret Mozu un pret Āronu, un visa draudze uz tiem sacīja: kaut Ēģiptes zemē būtu nomiruši, jeb kaut šinī tuksnesī būtu nomiruši!
Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
3 Un kāpēc Tas Kungs mūs ved uz šo zemi, ka mums būs krist caur zobenu, mūsu sievām un mūsu bērniņiem būs palikt par laupījumu? Vai mums nebūtu labāki, griezties atpakaļ uz Ēģiptes zemi?
Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
4 Un tie sacīja viens uz otru: celsim sev virsnieku un griezīsimies atpakaļ uz Ēģiptes zemi.
Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
5 Tad Mozus un Ārons nokrita uz savu vaigu priekš visa Israēla bērnu draudzes pulka.
Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
6 Un Jozuas, Nuna dēls, un Kālebs, Jefunna dēls, no tiem zemes izlūkiem, saplēsa savas drēbes.
Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
7 Un tie runāja uz visu Israēla bērnu draudzi un sacīja: tā zeme, ko esam pārstaigājuši izlūkot, ir ļoti varen laba zeme.
suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
8 Ja Tam Kungam ir labs prāts pie mums, tad Viņš mūs novedīs uz šo zemi un mums to dos, zemi, kur piens un medus tek.
In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
9 Tikai nesaceļaties pret To Kungu un nebīstaties no tās zemes ļaudīm; tie mums būs kā maizes kumoss. Viņu patvērums no tiem ir atstājies, un Tas Kungs ir ar mums; nebīstaties no tiem!
Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
10 Tad visa draudze sacīja, ka tie akmeņiem jānomētā. Bet Tā Kunga godība parādījās saiešanas teltī priekš visiem Israēla bērniem.
Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
11 Un Tas Kungs runāja uz Mozu: cik ilgi šie ļaudis Mani kaitina? Un cik ilgi tie negrib Man ticēt, pie visām tām zīmēm, ko Es viņu vidū esmu darījis?
Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
12 Es tos sitīšu ar mēri un tos izdeldēšu, un tevi darīšu par lielāku un stiprāku tautu, nekā viņi.
Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
13 Bet Mozus sacīja uz To Kungu: taču ēģiptieši dzirdējuši, ka Tu caur Savu spēku šos ļaudis no viņiem esi izvedis,
Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
14 Un sacījuši šās zemes iedzīvotājiem; tie dzirdējuši, ka Tu, ak Kungs, esi starp šiem ļaudīm, ka Tu, Kungs, acīm esi redzams, ka Tavs padebesis pār tiem stāv, un Tu viņu priekšā ej padebeša stabā dienu un uguns stabā nakti;
Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
15 Ja Tu nu šos ļaudis nokautu tā kā vienu vienīgu vīru, - tad tie pagāni, kas Tavu slavu dzirdējuši, tiešām runātu un sacītu:
In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
16 Tāpēc ka Tas Kungs šos ļaudis nevarēja ievest tai zemē, ko Viņš tiem bija zvērējis, Viņš tos ir nokāvis tuksnesī.
‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
17 Nu tad, lai Tā Kunga spēks paaugstinājās, kā Tu esi runājis un sacījis:
“Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
18 Tas Kungs ir pacietīgs un no lielas žēlastības, piedodams noziegumus un pārkāpumus, bet Viņš arī nepamet nesodītus, piemeklēdams tēvu grēkus pie bērniem līdz trešam un ceturtam augumam.
‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
19 Piedod jel šo ļaužu noziegumu pēc Savas lielās žēlastības un tā kā Tu šiem ļaudīm esi piedevis no Ēģiptes zemes līdz šim.
Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
20 Un Tas Kungs sacīja: esmu piedevis pēc tava vārda.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
21 Un nu, tik tiešām kā Es dzīvoju un visa pasaule taps pilna Tā Kunga godības,
Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
22 Visi tie vīri, kas ir redzējuši Manu godību un Manas zīmes, ko Es esmu darījis Ēģiptes zemē un tuksnesī, un Mani nu ir kārdinājuši desmitkārt un Manai balsij nav paklausījuši,
ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
23 Tiem nebūs redzēt to zemi, ko Es viņu tēviem esmu zvērējis: nevienam no tiem, kas Mani apkaitinājuši, to nebūs redzēt.
ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
24 Bet Savu kalpu Kālebu, tāpēc ka cits gars ar to ir bijis, un ka tas pareizi Mani klausījis, to Es gribu ievest tai zemē, kur viņš ir bijis, un viņa dzimumam to būs iemantot.
Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
25 Amalekieši un Kanaānieši dzīvo lejā. Griežaties rītā atpakaļ un ejat uz tuksnesi pa niedru jūras ceļu.
Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
26 Un Tas Kungs runāja uz Mozu un uz Āronu un sacīja:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
27 Cik ilgi tā būs ar šo ļauno draudzi, kas pret Mani kurn? Es esmu dzirdējis Israēla bērnu kurnēšanu, ar ko tie pret Mani kurn.
“Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
28 Saki tiem: tik tiešām kā Es dzīvoju, saka Tas Kungs, Es jums tā darīšu, kā jūs Manās ausīs esat runājuši.
Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
29 Šinī tuksnesī būs krist jūsu miesām, un visiem jūsu skaitītiem, pēc visiem jūsu pulkiem, tiem, kas divdesmit gadus veci un pārāki, kas pret Mani esat kurnējuši.
A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
30 Jums nebūs ieiet tai zemē, par ko Es Savu roku esmu pacēlis, lai tur mājojiet, bet tik vien Kālebam, Jefunna dēlam, un Jozuam, Nuna dēlam.
Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
31 Un jūsu bērnus, par ko jūs sacījāt, tie būšot par laupījumu, tos Es ievedīšu, un tie dabūs pazīt to zemi, ko jūs nicinādami esat atmetuši.
Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
32 Bet jums un jūsu miesām būs krist šinī tuksnesī.
Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
33 Un jūsu bērni būs gani tuksnesī četrdesmit gadus, un tiem būs jūsu maucību nest, tiekams jūsu miesas bojā iet tuksnesī.
’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
34 Pēc to četrdesmit dienu skaita, cik ilgi jūs to zemi esat izlūkojuši, ikvienu dienu skaitot par gadu, jums būs nest savus noziegumus četrdesmit gadus; ka jūs atzīstat, kas tas ir, kad Es no jums nogriežos.
Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
35 Es Tas Kungs esmu runājis, Es to tiešām darīšu visai šai ļaunai draudzei, kas pret Mani sametusies; šinī tuksnesī tiem būs iet bojā, un tur tiem būs nomirt.
Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
36 Tad nu tie vīri, ko Mozus bija sūtījis, to zemi izlūkot, kas bija atgriezušies atpakaļ un visu draudzi pret viņu rīdinājuši uz kurnēšanu un izpauduši nelabu slavu par to zemi,
Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
37 Tie vīri, kas tai zemei darījuši nelabu slavu, nomira caur vienu mocību Tā Kunga priekšā.
waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
38 Bet Jozuas, Nuna dēls, un Kālebs, Jefunna dēls, palika dzīvi no tiem vīriem, kas bija nogājuši, to zemi izlūkot.
Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
39 Un Mozus runāja šos vārdus uz visiem Israēla bērniem; tad tie ļaudis ļoti bēdājās.
Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
40 Un tie cēlās agri un devās augšā uz kalnu galu sacīdami: redzi, šeit esam un iesim uz to vietu, par ko Tas Kungs sacījis; jo mēs esam grēkojuši.
Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
41 Bet Mozus sacīja: kāpēc jūs pārkāpjat Tā Kunga vārdu? Jo tas jums neizdosies.
Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
42 Neejat uz augšu, Tas Kungs nav jūsu vidū, ka jūs netopat sakauti no saviem ienaidniekiem.
Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
43 Jo Amalekieši un Kanaānieši tur ir jūsu priekšā, un jūs kritīsiet caur zobenu; jo tāpēc ka jūs no Tā Kunga esat atkāpušies, Tas Kungs nebūs ar jums.
gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
44 Tomēr tie ar pārgalvību devās uz augšu, uz kalnu galu, bet Tā Kunga derības šķirsts un Mozus neatstājās no lēģera.
Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
45 Tad Amalekieši un Kanaānieši, kas uz tiem kalniem dzīvoja, nāca un tos sita un sakāva līdz Hormai.
Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.